25/08/2022
HOTUNA: Obasanjo, Wike, Obi, da Wasu Sun Gana yau a can birnin Landan.
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, a ranar Alhamis, ya gana da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour, Peter Obi; da Gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike, a Landan.
Duk da cewa har yanzu ana kan zayyana cikakkun bayanai game da taron har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, jaridar The PUNCH ta samu labarin cewa wani bangare ne na tattaunawar da ake yi gabanin zaben shugaban kasa na 2023. Wike ya halarci taron tare da abokansa da s**a hada da Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo; Gwamna Samuel Ortom na jihar Benue; Gwamna Okezie Ikpeazu na jihar Abia da tsohon gwamnan jihar Cross River, Donald Duke da dai sauransu.
Credit: Olalekan Adetayo -- Ku biyo mu don samun labarai da bidiyo da dumi-duminsu