Amsar tambaya ta daya da Dr sharif Sadiq ya kalubalencemu akai kuma yace inde muka kawo zai bada dubu dari biyar
RUBUTU NA SHIDA KUMA GYARA NA BIYAR DAGA CLIP ƊIN SHARIF SADIQ NA HUDU AKAN HADISIN NANA AISHA DA YA KAFA HUJJA DASHI
Maganar Gaskiya nayi mamakin hujjar da sharif ya kawo akan cewa wai ga nana Aisha ta raɓawa annabi kalmar الهوى kuma har yake ganin cewa ya samu lasisin da zai iya gayawa annabi.
Na farko dai kafin na fara magana akan hadisin yana da kyau ace duk fannin da mutum yake da'awar ya karanta a jami'a ko ya mayar da hankalinsa akai to bai kamata ana samun wasu kananun kura-kurai ba daga gurinsa a fannin, abinda yasa nayi maganar nan shine an daɗe ana ce mana sharif sadiq Muhaddithi ne (ma'ana malamin hadisi) sai gashi a matsayinsa na muhaddithi ta bayyana gurin mu almajirai cewa bashi da zurfin bincike a sana'ar sa,kuma bashi da diqqah da tahqeequl masa'il
Sharif ya kawo hadisin nana aisha da yazo a littafin Al-imamul bukhari inda take cewa
ما أَرى ربك إلا يُسارِع في هواك.
"bana ganin ubangijin ka, face yana rige-rige a cikin yardarka" (ma'anar maganar ta dai "Ni gani nake kamar ma ubangijin naka rige-rige yake a cikin yardarka")
duk da shi sharif ya fassara kalmar nan ta الهوى da tazo a hadisin da "son rai" wadda ita ma ba haka malaman hadisi suka fassara ta ba.
Zanso malam ya duba babban littafin sharhi na Sahihul bukhari mai suna Fathul bariiy na Al-haafiz ibnu-hajar Al'asqalani, wannan littafin fa shine littafin da malamai suke masa kirari da faɗin Annabi cewa
لا هجرة بعد الفتح
Babu hijirah bayan Fathu makkah, ma'ana dai kamar yadda annabi yace babu hijra bayan fathu makkah hakanan malamai na cewa babu wani sharhi da za'ayi bayan fathul bariiy da zai kai shi in dai akan sharhin sahihul bukhari ne
A ciki ne Al-haafiz ibnu hajar yake cewa a karkashin sharhin wannan hadisin
قَوْلُهُ: (مَا أَرَى رَبَّكَ إِلَّا يُسَارِعُ فِي هَوَاكَ) فِي رِوَايَةِ مُحَمَّدِ بْنِ بِشْرٍ: إِنِّي لَأَرَى رَبَّكَ ي
RUBUTU NA SHIDA KUMA GYARA NA BIYAR DAGA CLIP ƊIN SHARIF SADIQ NA HUDU AKAN HADISIN NANA AISHA DA YA KAFA HUJJA DASHI
Maganar Gaskiya nayi mamakin hujjar da sharif ya kawo akan cewa wai ga nana Aisha ta raɓawa annabi kalmar الهوى kuma har yake ganin cewa ya samu lasisin da zai iya gayawa annabi.
Na farko dai kafin na fara magana akan hadisin yana da kyau ace duk fannin da mutum yake da'awar ya karanta a jami'a ko ya mayar da hankalinsa akai to bai kamata ana samun wasu kananun kura-kurai ba daga gurinsa a fannin, abinda yasa nayi maganar nan shine an daɗe ana ce mana sharif sadiq Muhaddithi ne (ma'ana malamin hadisi) sai gashi a matsayinsa na muhaddithi ta bayyana gurin mu almajirai cewa bashi da zurfin bincike a sana'ar sa,kuma bashi da diqqah da tahqeequl masa'il
Sharif ya kawo hadisin nana aisha da yazo a littafin Al-imamul bukhari inda take cewa
ما أَرى ربك إلا يُسارِع في هواك.
"bana ganin ubangijin ka, face yana rige-rige a cikin yardarka" (ma'anar maganar ta dai "Ni gani nake kamar ma ubangijin naka rige-rige yake a cikin yardarka")
duk da shi sharif ya fassara kalmar nan ta الهوى da tazo a hadisin da "son rai" wadda ita ma ba haka malaman hadisi suka fassara ta ba.
Zanso malam ya duba babban littafin sharhi na Sahihul bukhari mai suna Fathul bariiy na Al-haafiz ibnu-hajar Al'asqalani, wannan littafin fa shine littafin da malamai suke masa kirari da faɗin Annabi cewa
لا هجرة بعد الفتح
Babu hijirah bayan Fathu makkah, ma'ana dai kamar yadda annabi yace babu hijra bayan fathu makkah hakanan malamai na cewa babu wani sharhi da za'ayi bayan fathul bariiy da zai kai shi in dai akan sharhin sahihul bukhari ne
A ciki ne Al-haafiz ibnu hajar yake cewa a karkashin sharhin wannan hadisin
قَوْلُهُ: (مَا أَرَى رَبَّكَ إِلَّا يُسَارِعُ فِي هَوَاكَ) فِي رِوَايَةِ مُحَمَّدِ بْنِ بِشْرٍ: إِنِّي لَأَرَى رَبَّكَ ي
RUBUTU NA BIYAR KUMA GYARA NA HUDU DAGA CLIP DIN SHEIKH SHARIF SADIQ NA BIYU AKAN MAGANARSA TA CEWA MUTUM KO FATIHA DA ƘULHUWALLAHU YA IYA ZA'A BASHI LIMANCIN JUMU'A
Duk da munyi magana akan wannan mas'alar a baya, tare da karanto masa sharuɗan da malamai suka rattabo, sai naga ya kyautu a kara yi masa ilzami da wasu hujjojin daban dan a kara nuna masa cewa wannan fatawar da ya bayar ta saɓawa malaman malikiyyah gaba ɗayan su (abisa binciken da nayi,wallahu a'alam)
Yazo a cikin كتاب الكافي في فقه أهل المدينة المالكي na Abu umar yusuf bin abdillahil qurɗabiy inda yake cewa a karkashin babul imamati (Ma'ana babin limanci)
و ينبغي أن يختار الإمام الراتب فيكون فقيها عالما بأحكام الصلاة محسنا بالقرآن سالما من البدع، و الكبائر،
yake cewa "kuma ya kamata a zaɓo limami ratibi,sa'annan ya kasance Masani (ma'ana Malami) kuma wanda ya san hukunce-hukuncen sallah, wanda ya iya karatun Alqur'ani, kuma wanda ya ƙubuta daga aikata bidi'a, ko kuma manya-manyan zunubai"
To Anan ne nake so na tambayi Sheikh Sharif sadiq shin idan har za'a rattabowa limami ratibi wannan sharuɗan, ashe ba limamin jumu'a bane yafi cancanta da ace ya cike wa'ennan ba ?
to me yasa malam zai ce ko fatiha da ƙulhuwallahu ?
sa'annan dai Sheikh abu umar Alqurɗubiy ya cigaba da cewa
و رب المنزل أولى بالإمامة فيه إن كان يحسن الصلاة من الفقيه و غيره، و لا يتقدمه في منزله أحد إلا بإذنه
"kuma mai gida shi yafi cancanta da yayi jagorancin sallah (a gidansa) idan har ya iya sallar akan malami ko kuma waninsa, kuma kada wani yace zai ja shi sallah a gidansa ba tare da izininsa ba"
Ashe dai maganar da sharif ya faɗa ta cewa idan sarki yazo gidanka shine zai bada sallah, bata da wani asali, idan kuma akwai to malam ya kawo mana wani magabaci da ya fadi hakan...
kuma ina so malam ya sani, hadisin
INA NE MAƘURA ? FADAR SARKI KO KUMA ZAWIYOYI DA MASALLATAN MALAMAI
abin mamaki ne sosai kaga malami yayi gina istidlalinsa (hujjarsa) da karshen aya kuma yace abinda yazo kafin wannan ayar shine hukunci na ƙarshe...
Abinda nake so nace shine,akwai wani clip da yake yawo na wani malami daga malaman Agege wanda a ciki yake kira zuwa ga faɗin Allah cewa
و إن تنازعتم في شيء فردوه إلى الله و الرسول
"idan kun samu jayayya a cikin wani abu, to ku mayar dashi zuwa ga Allah da manzon sa"
sai yake cewa, ai babu abinda yafi dacewa a mas'alar masallacin Agege kamar a koma zuwa gidan sarki, domin Allah subhanahu wa ta'ala yana cewa
يا أيها الذين آمنوا أطيعوا الله و أطيعوا الرسول و أولي الأمر منكم
"ya ku wayenda kukayi imani, kuyi ɗa'a ga Allah, kuma kuyi ɗa'a ga manzonsa da kuma majiɓanta lamuranku"
Har yake cewa jamhurin malamai sun tafi akan cewa ana nufin "sarakuna" kamar yadda yazo a tafsirin ibnu katheer, har ya kara da cewa idan mukayi duba zuwaga ANNAZMUL QUR'ANIY ma yana tabbatar da hakan, domin Allah ya fara jan kunnen bayinsa ne zuwa ga Adalci a ayar da ta gabaci wannan ayar, daga nan kuma sai yayi umarni da yi masa biyayya dashi da manzon sa da kuma masu mulki (wato sarakuna)
sai ni nake gani kamar an chakuɗa takardu a wannan bayanin, domin in har munyi duba dakyau da ANNAZMUL QUR'ANIY (Tsari irin na al'qur'ani) zamuce fasahar Allah ta wuce inda malam ya tsaya, domin Allah yace
إِنَّ اللَّهَ يَأْمُرُكُمْ أَن تُؤَدُّوا الْأَمَانَاتِ إِلَىٰ أَهْلِهَا وَإِذَا حَكَمْتُم بَيْنَ النَّاسِ أَن تَحْكُمُوا بِالْعَدْلِ ۚ إِنَّ اللَّهَ نِعِمَّا يَعِظُكُم بِهِ ۗ إِنَّ اللَّهَ كَانَ سَمِيعًا بَصِيرًا *** يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آمَنُوا أَطِيعُوا اللَّهَ
Sarki ba malami bane
DAGA CIKIN ABINDA KHALIFAN SHEIKH ADAM ABDULLAHI AL-ILORY (MUDIRUL MARKAZ) YA FAƊA GAME DA LIMANCIN MASALLACIN HAUSAWA NA AGEGE
"Shi SARKIN HAUSAWA an yarda (sarki ne) amma ba Malami bane, Shi yasa ya bar aikin malinta ga Malamai, kada ya dinga shiga"
Kaji aikin ilimi da hankali !!!
Agege
MUMINI SHINE WANDA YAKE IYA YIN SHAIDA AKAN GASKIYA
Allah yana cewa :
يا أيها الذين آمنوا كونوا قوامين بالقسط شهداء لله ولو على أنفسكم أو الوالدين والأقربين
"Yaku wanda kukayi imani ku kasance masu tsayuwa akan adalci kuna masu sheda ga Allah, koda akan kawunanku ne ko kuma iyayen ku, ko kuma makusantanku"
Allah kuma yana faďa mana cewa daga cikin siffofin muminai sune
وَالَّذِينَ هُمْ بِشَهَادَاتِهِمْ قَائِمُونَ
"sune wanda suke tsayuwa (da gaskiya) da shedarsu"
wannan videon an ɗauke shi ne a ranar da aka bawa Sheikh mustapha imam Na'ibancin garin Agege
A inda chairman din masallacin yake cewa
"Kuma da akwai ɗan uwanmu,yayan mu,malamin mu, Malam mustapha shine Na'ibi a yanzu, sannan kuma insha Allahu kafin Ace an gama gyaran, a buɗe masallaci, zamu nemi izinin ɗan limamin mu da kuma commitee,dan mu fitar da limami ratibi shine zai dinga bada khamsu salawati, insha Allahu, insha Allahu"
Wannan abu anyi shine bayan sallar jumu'a 26/sept/2020 wanda a gaban kowa ya faru, Domin a kafa sheda, a clip din akwai
Sheikh mustapha imam
Dan limamin mu Sharu sama'ila
Marigayi Alhaji abdul hadi bala (chairman din commitee) Allah ya kara masa rahama
Alhaji lawan yaro
Malam muniru (Sakataren sarki idan banyi kuskure ba)
Alhaji ibrahim Garba Tafida (Sarkin samarin Agege)
Ku tuna maganar Allah maɗaukakin sarki akan sheda...
و لا تكتموا الشهادة و من يكتمها فإنه آثم قلبه
Allah yace:
kada ku dinga ɓoye sheda, duk wanda ya ɓoye ta (Sheda) lallai mai zunubi ce zuciyar sa ( ma'ana dai mai zunubi ne shi)
Allah ya bamu ikon bin umarnin sa !!!