MADUBI News 24/7

MADUBI News 24/7 MADUBI News 24/7

Yadda ficewar Nijar da Mali da Burkina Faso daga Ecowas ka iya raunata ƙungiyarFicewar ƙasashen Mali da Nijar da Burkina...
29/01/2025

Yadda ficewar Nijar da Mali da Burkina Faso daga Ecowas ka iya raunata ƙungiyar

Ficewar ƙasashen Mali da Nijar da Burkina Faso daga ƙungiyar Ecowas a ranar Laraban nan bayan kwashen fiye da shekara guda ana zaman tankiya tsakanin ƙungiyar da ƙasashen guda uku, wani abu da ke nuni da rashin tabbas ga cigaba da kasancewar ƙungiyar ta Ecowas.

A ranar ta 29 ga watan Janairun 2024 ne ƙasashen guda uku da shugabannin mulkin soji ke jagoranta s**a sanar da ƙungiyar Ecowas a hukumance dangane da buƙatar ficewar tasu.

To sai dai bisa dokokin Ecowas, ƙasashen na buƙatar sanar da ƙungiyar shekara guda kafin amincewa da ficewar.

Kuma a ranar Larabar nan ne wa'adin ke cika, bayan dukkan ƙasashen uku sun yi watsi da kiran ƙungiyar ta Ecowas na su ƙara tsawaita zamansu mambobinta na watanni shida domin samo mafita.

Yanzu dai ƙasashen na Burkina Faso da Mali da Nijar sun zama ƙawaye inda s**a cure wuri guda ƙarƙashin ƙungiyar da suke kira Haɗakar Ƙasashen Sahel (Allaiance of Sahel States (AES).

Shugabannin mulkin sojin ƙasashen dai sun zargi Ecowas da ƙaƙaba musu takunkumi na "rashin imani kuma haramtattu" bayan juyin mulkin da ya kawo su kan karaga.

Sun kuma yi amannar cewa ƙungiyar ta Afirka ta Yamma ba ta ba su cikakkiyar gudunmawa ba wajen yaƙar ƴan'adda. Sun kuma yi amannar cewa Ecowas ɗin ƴar kanzagin tsohuwar uwar gijiyarsu ce wato Faransa.

Faransa ta kasance abokiyar hamayyar wannan ƙasashen da sojoji ke jagoranci da a yanzu haka s**a ƙwammace yin hulɗa da ƙasashe irin su Rasha da Turkiyya da Iran.

Ina ne maɓoyar Bello Turji, kuma me ya hana a k**a shi ?Da zarar an samu labarin sojoji sun kai farmaki kan ƴanbindiga a...
29/01/2025

Ina ne maɓoyar Bello Turji, kuma me ya hana a k**a shi ?

Da zarar an samu labarin sojoji sun kai farmaki kan ƴanbindiga a yankin arewa maso yammaci, musamman a jihar Zamfara, abin da mutane ke tambaya shi ne an k**a Bello Turji?

Ko a shekarar da ta gabata, bayan kashe fitacen ɗanbindiga, Halilu Sububu, babban hafsan tsaron Najeriya Janar CG Musa ya ce saura Bello Turji ya rage, inda a cewarsa sun kusa k**a shi.

A makon nan da ake ciki ma, dakarun Operation Fansan Yamma tare da haɗin gwiwar jami'an tsaron farin kaya (DSS), sun ce sun ƙwace tarin mak**ai a ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda ta jihar Zamfara, wanda a cewarsu, mak**an na Turji ne.

Dakarun sun kai samamen ne bayan samun bayanan sirri kan masu safarar mak**ai daga Jamhuriyar Nijar zuwa Najeriya, k**ar yadda kakakin rundunar, Laftanar-Kanal Abubakar Abdullahi ya sanar, inda ya ce sun ƙaddamar da farmakin ne a ranar 27 ga watan Janairun 2025, abin da ya kai ga ƙwato mak**an kan hanyar Namoda zuwa Zurmi.

Fashewar tankar mai ta kashe mutum 18 a EnuguTankar mai.Hukumomin Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutum 18, yayin da wa...
26/01/2025

Fashewar tankar mai ta kashe mutum 18 a Enugu
Tankar mai.

Hukumomin Najeriya sun tabbatar da mutuwar mutum 18, yayin da wasu 10 s**a samu munanan raunukan ƙuna bayan fashewar tankar man fetur a jihar Enugu da ke kudu maso gabashin ƙasar.

Hukumar kiyaye aukuwar hatsura ta ƙasar, ta ce motar ta ƙwace wa direbanta bayan lalacewar birki, lamarin da ya sa ta bi ta kan wasu ƙananan ababen hawa a kan wani babban t**i, kafin ta fashe.

Fashewar tankar - wadda ta faru a ranar Asabar - ta ƙona mutane da dama ta yadda har ba aiya gena wasu.

Hatsarin ya kasance na baya-bayan nan cikin hatsuran fashewar motocin tankokin man futer da s**a yi sanadin rayuwa da dama a cikin ƙasar.

Ko a makon da ya gabata ma wani hatsarin tankar man fetur a jihar Neja ya kashe kusan mutum 98.

Tinubu ya tafi Tanzania taron Afirka kan mak**ashiBola Tinubu.Shugaba Bola Tinubu zai tafi Tanzania a yau Lahadi domin h...
26/01/2025

Tinubu ya tafi Tanzania taron Afirka kan mak**ashi
Bola Tinubu.

Shugaba Bola Tinubu zai tafi Tanzania a yau Lahadi domin halartar taron ƙoli na Afirka kan mak**ashi a babban birnin ƙasar, Dar es Salaam, wanda za a fara gobe Litinin zuwa jibi Talata.

Taron wanda gwamnatin ƙasar ta Tanzania za ta karɓi baƙuncinsa da haɗin gwiwar Bankin Raya Afirka da kuma Bankin Duniya, zai kasance ne da nufin tabbatar da shirin samar da wutar lantarki ga mutum miliyan 300 a Afirka nan da shekara ta 2030 - shirin da ake yi wa laƙabi da ‘‘Mission 300.’’

A yayin taron shugabannin Afirka, da shugabannin harkokin kasuwanci a nahiyar da kungiyoyin farar hula za su yi ƙoƙarin samo dabarun ciyar da shirin gaba cikin hanzari.

Haka kuma taron zai yi musayar dabaru kan yadda za a shawo kan matsalar mak**ashi a nahiyar.

Mahalatta taron za su tattauna kan yadda za a samar da mak**ashi kan yankunan da suke da matsala cikin sauri da samar da mak**ashi maras gurɓata muhalli da ƙoƙarin shigar da 'yankasuwa cikin harkar samar da mak**ashin.

A ranar farko ta taron ministocin mak**ashi na ƙasashen da ke halartar taron za su tattauna, yayin da a rana ta biyu shugabannin ƙasashen su kuma za su rattaɓa hannu kan daftarin shirin samar da mak**ashin na Afirka.

Harin Boko Haram ya kashe sojojin Najeriya da dama a BornoSoja da bindiga na wuce mota da aka kona.Rahotanni daga Najeri...
26/01/2025

Harin Boko Haram ya kashe sojojin Najeriya da dama a Borno
Soja da bindiga na wuce mota da aka kona.

Rahotanni daga Najeriya na nuna cewa sojojin Najeriya da dama ciki har da kwamandansu sun rasu a wani hari da mayaƙan Boko Haram s**a kai musu a sansaninsu da ke garin Malam-Fatori na karamar hukumar Abadam ta jihjar Borno.

Wasu bayanai na nuna cewa sojojin da s**a mutu sun kai 27 haɗi da kwamandan nasu.

Wasu kafofi sun ruwaito cewa majiya mai ƙarfi ta sheda musu cewa maharan sun yi wa sansanin dirar mikiya ne inda s**a yi ta bata-kashi da dakarun Najeriyar tsawon sa'o'i da dama a ranar Juma'a 24 ga watan nan na Janairun 2025, inda s**a yi nasarar cin ƙarfin sansanin.

Sojojin da s**a tsira daga harin sun tsere daga sansanin, in ji rahotanni.

Bayanai sun tabbatar da cewa mayaƙan masu iƙirarin jihadi sun je sansanin ne da motoci masu bindigogi a kansu.

''An ji wa sojoji da dama mummunan rauni, yayin da wasu da yawa kuma ba a san inda suke ba,'' k**ar yadda tashar talabijin ta ce wata majiya ta sheda mata.

Kwamandan rundunar, Laftana Kanar Alari da wasu manyan sojoji biyu da s**a haɗa da babban darektan kula da lafiya na sansanin na daga cikin waɗanda aka kashe.

Sansanin na Malam-Fatori na wajen da ke da tazarar kilomita biyu ne kacal daga garin Bosso na Nijar da kan iyaka a yankin tafkin Chadi.

Sai dai kuma wata majiyar soji ta sheda wa tashar talabijin ɗin cewa an kai harin ne a sansanin lokacin da dakarun ke sintiri inda mayaƙan s**a yi musu kwanton-ɓauna, da ya kai ga kisan kwamandan.

Har yanzu hukumomin sojin Najeriya ba su ce komai ba game da harin.

Sanata Ahmed Wadada Aliyu ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar Nasarawa a shekarar 2027, saboda cancanta...
26/01/2025

Sanata Ahmed Wadada Aliyu ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan jihar Nasarawa a shekarar 2027, saboda cancantarsa ​​da kuma kiran Ubangiji.

Da yake zantawa da manema labarai a garin Keffi, Wadada ya bayyana kwarin gwuiwarsa kan iya shugabancin jihar, inda ya ce, “Ina da dukkan abin da ya k**ata na zama Gwamnan Jihar Nasarawa, bisa la’akari da bayanan da na yi na yi wa gwamnati hidima da kuma rahamar Ubangiji a gare ni.

Wadada, wanda a halin yanzu yake zama dan majalisar dattawa a karkashin wani dandali na daban, ya bayyana cewa an kira shi ne ya koma jam'iyyar All Progressives Congress (APC), jam'iyyar da ya bayyana a matsayin "a cikin kashina."

Ya bayyana irin rawar da ya taka wajen fitowar jam’iyyar APC, bayan da ya rike mukamin sakataren kudi na jam’iyyar New-PDP, wadda daga baya ya koma APC.

Ana dai kallon ayyana Wadada a matsayin wani gagarumin ci gaba a tunkarar zaben gwamna na 2027 a jihar Nasarawa.

25/01/2025

Ba domin tsawo a kan ga wata ba.

Ƙara kuɗin kira da na data rashin adalci ne- NLC.Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta yi kira ga ƴan Najeriya su fara shirye-...
23/01/2025

Ƙara kuɗin kira da na data rashin adalci ne- NLC.

Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta yi kira ga ƴan Najeriya su fara shirye-shiryen dakatar da amfani da kamfanoninin sadarwa domin nuna adawarsu ga amincewa da ƙarin kashi 50 na kuɗin kira da data da gwamnatin tarayya ta yi.

A wata sanarwa da NLC ta fitar a jiya Laraba, ta ce ƙarin kuɗin rashin adalci ne ga ƴan ƙasar, waɗanda a yanzu haka suke fuskantar ƙalubale saboda matsin tattalin arziki.

Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana damuwarsa kan ƙarin, inda ya ce, "wannan matakin, wanda ya zo a daidai lokacin da ma'aikata da sauran ƴan ƙasa suke fama da matsin tattalin arziki, tamkar ba kamfanonin sadarwar wuƙa da nama su yi yadda suke su da ƴan ƙasar, k**ar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

"Harkokin sadarwa na cikin abubuwa masu muhimmanci domin sadarwa da neman labarai. Kuma ko a yanzu ma ƙaramin ma'aikacin Najeriya yakan kashe kusan kashi 10 na albashinsa wajen sayan katin waya da data. Misali ma'aikacin da ke karɓar albashin naira 70,000, idan yana kashe naira 7,000 ne, yanzu zai fara kashe kusan naira 10,500 ne a waya."

Ya kuma caccaki gwamnatin bisa yadda ta amince da ƙarin cikin gaggawa, amma ta ɗauki dogon lokaci kafin ta amince da mafi ƙarancin albashi.

An fara kwashe mutane a Los Angeles bayan wata gobara ta kunno kaiGobaraAsalin hoton,Getty ImagesWata gobara mai ƙarfi t...
23/01/2025

An fara kwashe mutane a Los Angeles bayan wata gobara ta kunno kai
GobaraAsalin hoton,Getty Images
Wata gobara mai ƙarfi ta sake tasowa a yankin Los Angeles, wanda ta sa aka fara kwashe dubban mutane daga yankin zuwa wani wurin daban.

Gobarar ta taso ne daga kimanin tafiyar mil 45 wato kilomita 72 ta arewa maso yammacin birnin na Los Angeles a ranar Laraba, a kusa da tafkin Castaic mai tsaunuka da dama, kuma akwai gidajen mutane da makarantu a kusa.

Tuni wutar ta faɗaɗa zuwa faɗin murabba'in ƙasa 10,000 a ranar Laraba saboda yanayin iska da buji da ake ciki, duk da cewa har yanzu ba ta kai ga cinye wani gida ko wurin kasuwanci ba, sannan mahukunta na cewa sun yi amannar kashe ta kafin ta munana.

Yankin ya sake faɗawa cikin shirin kar ta kwana ne saboda ganin yadda waccan wutar dajin ta ɗaiɗaita jihar.

Aƙalla mutum 31,000 ne aka ce tilas su bar yankin, sannan an yi wa wasu mutum 23,000 gargaɗin cewa akwai buƙatar su tashi daga yankin na Los Angeles, ciki har da fursunoni 500 da suma aka kwashe aka sauya musu wuri, k**ar yadda wani jami'in tsaron, Robert Luna ya bayyana.

Shugaban hukumar kashe gobara ta Los Angeles, Anthony Marrone ya ce ma'aikatansa suna aiki tuƙuru domin shawo kan gobarar, inda ya ce, "mun kashe kusan kashi 15 na wutar zuwa safiyar Alhamis."

Hukumomi a jihar na cewa wannan wutar ta bambanta da na'ukan wutar dajin da aka fuskanta kwanakin baya, inda aƙalla mutum 28 s**a rasu, sannan sama da gidaje 10,000 s**a lalace.

An K**a Tsohon Inspector Na ’Yan Sanda, Linus Monday, Bisa Gudanar Da Bincike Bayan RitayaAn k**a Linus Monday, tsohon ɗ...
23/01/2025

An K**a Tsohon Inspector Na ’Yan Sanda, Linus Monday, Bisa Gudanar Da Bincike Bayan Ritaya

An k**a Linus Monday, tsohon ɗan sanda mai mukamin Inspector kuma ɗan Najeriya, bisa laifin gudanar da bincike kan ababen hawa duk da cewa ya riga ya yi ritaya daga aikin ɗan sanda.

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon jami’in ya ci gaba da gudanar da aikin bincike na tsayawa da duba mutane ba tare da izini ba, lamarin da ya jawo hankalin hukumomi har ya kai ga nasarar samun cafke shi.

Hukumar ’yan sanda tana cigaba da gudanar da bincike kan lamarin don gano ainihin dalilan da s**a sa tsohon ɗan sandan ya ci gaba da wannan aiki bayan ritayarsa.

Rikici ya sake kunno kai a PDP kan muƙamin sakataren jam'iyyarPDPA Najeriya rikici na sake kunno kai a cikin babbar jam’...
21/01/2025

Rikici ya sake kunno kai a PDP kan muƙamin sakataren jam'iyyar
PDP

A Najeriya rikici na sake kunno kai a cikin babbar jam’iyyar hamayya ta PDP, bayan da sakataren watsa labaran jam’iyyar Debo Ologunagba ya bayar da sanarwar cewa jam’iyyar ta amincewa da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja da ke cewa an sauke Samuel Anyanwu daga kan muƙamin sakataren PDP na ƙasa.

Debo ya kuma ce jam'iyyar ta amince da maye gurbinsa da Sunday Kelly Enemchukwu Udeh-Okoye.

Daga bisani kuma shi ma mataimakin sakataren wata labaran jam’iyyar Ibrahim Abdullahi ya fitar da wata sanarwa da ke cin karo da ta farko, inda ya ce har yanzu Sanata Samuel Anyanwu ne sakataren jam’iyyar har sai kotun ɗaukaka ƙara ta kammala yanke hukuncinta a watan Febrairu mai zuwa.

21/01/2025

Trump ya ce Amurka za ta fice daga WHO

WHO ta buƙaci Amurka ta janye ƙudurin ficewa daga cikintaHukumar lafiya ta duniya, WHO ta yi kira ga Amurka da ta janye ...
21/01/2025

WHO ta buƙaci Amurka ta janye ƙudurin ficewa daga cikinta

Hukumar lafiya ta duniya, WHO ta yi kira ga Amurka da ta janye ƙudurinta da ficewa daga cikin harkokin hukumar.

Hukumar ta bayyana haka ne a wani rubutu da ta wallafa a shafinta na X, inda ta ce tana taka rawa wajen inganta lafiya da tsaron al'umma, ciki har da Amurka.

"Ta hanyar gano musabbabin cututtuka da inganta asibitoci da ganowa tare da kiyaye aukuwa ko yaɗuwar cututtuka ciki har da annoba."

Sanarwar ta ƙara da cewa Amurka na cikin ƙasashen da s**a assasa hukumar a shekarar 1948, kuma tun a lokacin take taimaka wa ayyukan ƙungiyar tare da sauran mambobin hukumar guda 193.

A sama da shekara 70 da hukumar ke aiki, WHO da Amurka sun ceci rayuka da dama da ba za a iya ƙididdigewa ba, sannan ta kare yaɗuwar cututtuka da dama a ƙasashen duniya ciki har da Amurka.

"Ta hanyar wannan haɗakar, muka yaƙi cutar smallpox, sannan muna gab da yaƙar polio. Wannan ya sa muke fata Amurka za ta sake tunani, tare da janye ƙudurinta na ficewa daga hukumar ta lafiya domin kula da lafiyar miliyoyin mutane a duniya."

Ɗanwasan Dortmund ya buɗe gidauniya a NajeriyaKarim Adeyemi.Ɗanwasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Dortmund da ke Jamus, Kari...
21/01/2025

Ɗanwasan Dortmund ya buɗe gidauniya a Najeriya
Karim Adeyemi.

Ɗanwasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Dortmund da ke Jamus, Karim Adeyemi ya buɗe gidauniyar a Najeriya.

Adeyemi, wanda yanzu yake wakiltar tawagar ƙasar Jamus, asalinsa ɗan Najeriya, kasancewar mahaifinsa ɗan Najeriya ne.

Ya buɗe gidauniyar ne a birnin Ibadan da ke jiyar Oyo a kudu maso yammacin Najeriya, inda ya ce gidauniyar za ta mayar da hankali kan koyar da wasanni da ilimi.

A kwanakin baya da ya ziyarci Najeriya, Adeyemi ya shaida wa BBC cewa nan gaba yana tunanin komawa taka leda a gasar Premier ta Ingila.

A gasar zakarun turai ta bana, ɗanwasan ya zura ƙwallo uku rigis a ragar ƙungiyar Celtic a wasan da s**a fafata.

A game da gidauniyar, ya ce, "na san yadda rayuwa take a nan Najeriya da kuma yadda rayuwa take a Jamus. Na daɗe ina da tunanin idan na samu ɗaukaka ta hanyar ƙwallon ƙafa, zan koma asalina a Najeriya in taimaka wa mutane. Ba zan taɓa mantawa da asalina ba. Wannan babban abin alfahari ne," in ji shi.

Trump zai ziyarci Los Angeles da gobara ta ɗaiɗaitaTrumpShugaban Ƙasar Amurka Donald Trump zai kai ziyara jihar Californ...
21/01/2025

Trump zai ziyarci Los Angeles da gobara ta ɗaiɗaita
Trump

Shugaban Ƙasar Amurka Donald Trump zai kai ziyara jihar California domin gane wa idonsa yadda gobara ta lalata birnin Los Angeles.

Trump ya bayyana cewa daga cikin ziyarce-ziyarcen da zai fara, akwai zuwa birnin, inda gobarar daji ta ɓulla a mako biyu da s**a gabata.

A hirarsa kafin rantsuwa, shugaban ƙasar ya ce zai je birnin ne a ranar Juma'a mai zuwa.

Gwamnan jihar California, Gavin Newsom, ya ce, "muna farin ciki da maraba da zuwan shugaban ƙasar."

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da ɓullar cutar Anthrax a Zamfara
21/01/2025

Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da ɓullar cutar Anthrax a Zamfara

Ƙungiyar masu amfani da wayar tarho a Najeriya ta yi barazanar shigar da ƙara kan ƙarin farashin kuɗin kiran wayaWata ƙu...
21/01/2025

Ƙungiyar masu amfani da wayar tarho a Najeriya ta yi barazanar shigar da ƙara kan ƙarin farashin kuɗin kiran waya

Wata ƙungiya da ke wakiltar masu amfani da wayar tarho a Najeriya ta yi barazanar maka gwamnatin ƙasar a kotu bayan da hukumar sadarwa ta Najeriya (NCC) ta amince da ƙarin kuɗin kiran waya da kashi 50 cikin 100 daga ewatan Fabrairun wannan shekarar.

Shafin yaɗa labarai na Daily Post ta rawaito cewa shugaban ƙungiyar Adeolu Ogunbanjo ya ce ƙarin kuɗin ya yi yawa, saboda ƴan Najeriya na kokawa da tsadar man fetur da kuma farashin kayan masarufi. “Yayin da na fahimci kalubalen da ake fuskanta a fannin sadarwa, mun amince da ƙarin kuɗin da bai wuce kashi 5% zuwa 10% ba, idan hakan bai wadatar ba, ya k**ata kamfanonin sadarwa su nufi kawsuwar musayar hannun jari damin tara kuɗaɗe'' In ji Ogunbanjo.

“Ƙarin Kashi 50% ya yi yawa, muna cewa ba mu yarda ba, ba abin yarda ba ne, duk abin da ya wuce kashi 10%, za mu kai ƙara kotu.

Amincewa da ƙarin kuɗin kiran wayar dai na zuwa ne shekaru 12 bayan da hukumar NCC ta amince da farashin a shekarar 2013.

Trump ya bayar da umarni dakatar da kwararowar baƙi AmurkaDonald TrumpShugaban Amurka Donald Trump ya bayar da umarni ga...
21/01/2025

Trump ya bayar da umarni dakatar da kwararowar baƙi Amurka
Donald Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayar da umarni ga sakataren tsaron ƙasar da sauran shugabannin hukumomin tsaro su aika dakaru zuwa iyakokin ƙasar don daƙile kwarar baƙin haure

Ya ayyana dokar ta-ɓaci a kan iyakar bayan shan rantsuwa jiya Litinin, tare da ba da izinin amfani da dukkan ƙarfin hukuma don tsare iyakar.

Dokar zartarwa ta kuma umurci sakaten tsaro da na cikin gida da su yi aiki tare da sakatariyar harkokin shari’a don aiwatar da tsarin da aka yi na yaƙi da matsalar da shugaban ya yi yaƙin neman zaɓe a kanta.

Address

Lafia Beriberi
5050

Telephone

+2348037773271

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MADUBI News 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MADUBI News 24/7:

Videos

Share