Muryar Raunanan Duniya

Muryar Raunanan Duniya Mun bude wannan page din domin kawo maku abubuwan da shuka shafi Palestine

Hakki ne ga duk wani Ɗan Uwa da ya ga rubutun nan ya yaɗa shi, domin ya shiga ko'ina, yan uwa su falka.NAJERIYA INA MUKA...
24/10/2024

Hakki ne ga duk wani Ɗan Uwa da ya ga rubutun nan ya yaɗa shi, domin ya shiga ko'ina, yan uwa su falka.

NAJERIYA INA MUKA DOSA? 4

Babu tashin hankali kamar ace ga al'umma, iya al'umma, amma bata san makomarta ba. Bata san matserarta da mayankanta ba. Bata san macecinta da macucinta ba. Bata san Gabas ɗinta da yammanta ba.

Abunda ya fi wannan tashin hankali shi ne, wani daga cikinsu ya gano bakin zaren, alhali saura na cikin Ɗimuwa. To haka zai zauna a cikinsu tamkar fursuna. Ga halaka yana ganin tana kewayesu, za ta gama da su, amma babu mai saurarenshi, b***e ya ankare. Ganin alummarka tana halakewa a gaban idanunka, alhali Kanada da hanyar kuɓutar da su a hannunka, da ace sun saurareka, ba ƙaramar Azaba bace.

Shi ya sa a kullum dole mu Yan Harka Islamiyyah mu Tausayawa Shaikh Ibraheem Zakzaky (H). Da a ce wani zai daina bacci, ya dinga kukan jini, saboda tausayin wannan bawa na Allah, dangane da yadda al'ummar nan take bijirewa faɗakarwarsa da jan hankalinsa, dangane da yanayin da su ke ciki, da wanda Addininsu ya ke ciki, to da bai zamo abun zargi ba. Sai dai ma a yaba masa.

Billahi alaikum, ya ku wannan al'umma, minene Malam Ibraheem Al-zakzaky bai faɗa maku ba, game da sharrin Maƙiya a kanku, tun fiye da shekaru 40+?

Billahi alaikum, akwai wata kutungwuila, ko wani Sharri, ko makirci, tun daga rikicin mai tatsine, sauya tsarin mulki, cin hanci da rashawa, shari'ar bogi, rikicin Addini da ƙabikanci, rikicin mazhabobi da firkoki, rikicin boko haram, bandits, kidnapping, rikicin Hausawa da Fulani, satar ma'adanai, anshe gonaki, lalata tituna, tsadar man fetur, hauhawar farashi, rugujewar Tarbiyyah, shigowa da sabbin policies, hanƙoron Tinƙahon duniya, sharrin Yahudawa a kanmu, da dai sauran matsaloli, Shin akwai wadda bai gargademu a kan zuwanta tun kafin ta zo ba?

To kuma akwai wadda ya faɗa, aka ki saurarensa sai bata zo ba?
Shin wannan bai ishemu hankali ba?
Manta da Aƙidar malam, wadda wasu suke yiwa Mummunar fahimta, Shin ashe wanda ya ce da kai hattara ga rijiyan nan a gabanka, bai kamata ka saurari maganar sa a nan ba? Hatta kuwa koda ka ɗauka shi mara hankali ne, domin zai yiwu a nan yanada gaskiya.

Yanzu ga shi kusan duk sun gama lalata komai, saura su raba iyaye da Ɗiyansu, wanda shima yana daf da faruwa, musamman Ɗiya mata, daga nan sai a raba mutane da Addini, dama family ne ke rike da Addini, to idan an watse family addini zai ɓace.
Shin sai yaushe kunnuwanmu za su saurari wannan bawan Allah? Sai sun gama halaka mu?

Ko kuwa sai sun karkare kawarda da shi?
Kamar yadda suke yita hanƙoron haka, tun bayan fitowarsa daga gidan yari.

Musamman a kwanakinan, sun matsa sai sun kashe Sayyid Ibraheem Al-zakzaky, da Almajiransa a inda yake a Abuja.

Musamman bayan Ɗufanul Aqsa, inda aka jiyo Na yan hoo yana rantsuwa sai ya Murkushe masu kishin Addinin musulunci a Yammacin Afrika. Wanda kai tsaye da Sayyid Ibraheem Al-zakzaky yake, domin shine Almajirin Sayyid Ali Khamene'i mai kira irin nasa.

Babban abun mamakin shi ne, idan mutanen gari basu damu da wannan Haɗarin da yake tunkarar mu ba, bai kamata a ce yan uwa musulmi, musamman yan Harka Islamiyyah sun gafala daga wannan sharrin ba. Shin so suke sai sun ji labarin wani abu mara daɗi ya faru sannan su yi fargar jaji?

Isra'ila ta rantse sai ta kashe malam, to mu kuma ashe bai kamata mu bashi kariya da dukkan abunda za mu iya ba.?

Wasu ma ɗauka ɗauka suke, komai ya wuce, malam na can zaune ne cikin aminci, ya Allah.

Wasu kuwa tunda suna da matsala da wasu to ba za su yi abunda ya dace ba, saboda wadannan. Wannan wane irin reverse ne?

Wasu kuwa sun rantse sai sun huce fushinsu ga wasu. Sai kace dama ba aikin addini suke ba.

Wasu kuma neman abinci da son hutu ya shagaltar dasu.

Maƙiya sun bi mabiya sun rabawa kowa aiki, ya ɗauka yanata yi.

An bar Malam kusan shi Kaɗai a filin daga kuraye suna daka masa harara, tamkar Imam Husaini a filin Karbala. 😭

Yaushe za mu falka yan uwa. Mu cika Abuja da kewayen Abuja, mu ba wannan bawan Allah kariya. Kowa ya ajiye son ran sa ya yi abunda ya dace. Tun kafin lokaci ya kure mana. Ba wanda suke tsoro a Ƙasar nan idan ba malam ba. Ba wanda s**a dage sai sun kawar kamarsa. To mu hana faruwar haka.

_Dr. Shamsudeen Hassan

Wasiyyar Shaheed Yahya al-Sinwar:"Nine Yahya ɗan mai hijira wanda ya canza ƙaura(Hijira) zuwa ƙasa ta wucin gadi, kuma y...
22/10/2024

Wasiyyar Shaheed Yahya al-Sinwar:

"Nine Yahya ɗan mai hijira wanda ya canza ƙaura(Hijira) zuwa ƙasa ta wucin gadi, kuma ya canza mafarki zuwa yaƙi na har abada. Ina rubuta waɗannan kalmomin, ina mai tunawa da kowanne lokaci da ya wuce a rayuwa ta tun daga yarintata a tsakanin tituna, zuwa shekaru masu tsawo a kurkuku, zuwa kowanne kwayar jini da aka zubar a kan wannan ƙasar(Palasɗinu.)

An haife ni a sansanin Khan Younis a shekara ta 1962, a lokacin da Falasdinu take tunani mai yawan ɓarna da taswirar da aka manta a kan teburan masu mulki. Ni mutum ne wanda rayuwata ta kasance tsakanin wuta da toka, kuma na fahimci tun daga ƙuruciyata cewa rayuwa a ƙarƙashin mamaya ba ta nufin komai sai kurkuku na dindindin.

Na sani tun yarinta cewa rayuwa a wannan ƙasa ba ta da al'ada, kuma wanda aka haifa anan yana da alhakin ɗaukar makami a zuciyarsa wanda ba zai karye ba, kuma ya fahimci cewa hanyar zuwa 'yanci tana da tsawo.

Wasiyyata gare ku tana farawa daga nan, daga wannan yaron da ya jefa dutse na farko akan mamaya, wanda ya koyi cewa dutsen shine kalmomin farko da muke furtawa a fuskantar duniya da tayi shiru a kan rauninmu.

Na koyi darasi a titunan Gaza cewa mutum ba a auna shi da shekaru, sai dai da abin da ya bayar ga ƙasarsa.

Haka rayuwata ta kasance: kurkuku da yaƙe-yaƙe, raɗadi da kuma fata.
Na shiga kurkuku a karon farko a shekara ta 1988, an hukunta ni da hukuncin zaman kurkuku har abada, amma ban san hanyar tsoro ba.

A cikin waɗannan kurkukun masu duhu, na ga tagogin haske a bangayen kurkukun, kuma kowane haske yana haskaka min hanyar 'yanci.

A cikin kurkuku, na koyi cewa hakuri ba kawai kyakkyawan hali ba ne, a'a makami ne... makami mai zafi da ƙarfin gaske.

Wasiyyata gare ku: kada ku ji tsoron kurkuku, domin ba su da wani abu sai ɓangare na hanyar mu mai tsawo zuwa 'yanci.
Kurkuku ya koya mini cewa 'yanci ba kawai hakkin da aka kwace ba ne, a'a ra'ayi ne da ke haifar daga zafi kuma ana gina shi da hakuri.

Lokacin da na fita a cikin yarjejeniyar "Wafa'a al-Ahrar" a shekara ta 2011, ban fita kamar yadda nake ba; na fita tare da ƙarfin gwiwa da ƙarin imani cewa abin da muke yi ba kawai yaƙi ne na ɗan lokaci ba, a'a ƙaddara ce da muka ɗauka har zuwa ƙarshen ɗigun jininmu.

Wasiyyata ita ce ku ci gaba da rike bindiga, da daraja sosai.

Abokan gaba suna so mu yi watsi da juriya, su canza batunmu zuwa tattaunawa marar ƙarewa... Amma ina gaya muku cewa: kada ku yi tattaunawa akan abin da yake hakkin ku. Suna tsoron juriyar ku fiye da yadda suke tsoron makaman ku.

Juriya ba kawai makami bane da muke ɗauka, a'a soyayyarmu ga Falasdinu a kowane numfashi da muke shaka, ita ce ƙarfinmu na zama, duk da shirin kullewa da hare-hare.

Wasiyyata ita ce ku kasance masu aminci ga jinin shuhada, ga waɗanda s**a tafi s**a bar mana wannan hanya. Su ne s**a yi mana hanyar 'yanci da jinin su, don haka kada ku ɓata waɗannan hadayar a cikin lissafin masu mulki da dabarun diplomasiyya.
Muna nan don ci gaba da abin da na farko s**a fara, kuma ba za mu yi watsi da wannan hanya ba ko da yaushe.

Gaza ta kasance kuma za ta cigaba da kasancewa babban birnin juriya, da zuciyar Falasdinu da ba ta daina bugawa ba, har ma idan ƙasa ta yi ƙanƙan da mu. Lokacin da na karɓi jagorancin Hamas a Gaza a shekara ta 2017, ba kawai canja wuri bane, a'a ci gaba ne na juriya da ta fara da dutse kuma ta ci gaba da bindiga. Ina jin zafi a kowanne rana da zafin al'umma ta a ƙarƙashin kullewa, kuma na san cewa kowanne mataki da muke ɗauka zuwa 'yanci yana zuwa da farashi. Amma ina ce muku: farashin juriya yana da girma fiye da haka.

Don haka, ku rike ƙasa kamar yadda ganye ke rike ƙasa, don haka babu iska da za ta iya janyowa al'umma da ta yanke shawarar rayuwa. A cikin yaƙin Tufanul Aqsa, ni ba shugaban wata ƙungiya ko motsi ba ne, a'a ina mai magana ga kowanne Falastini da ke mafarkin 'yanci. Imani na ya jagoranci ni cewa juriya ba kawai zaɓi ba ne, a'a wajibi ne. Ina so wannan yaƙin ya zama sabon shafi a cikin littafin yaƙin Falastin, inda ƙungiyoyi s**a haɗu, kuma kowa ya tsaya a cikin rami guda, a kan abokan gaba da ba su taɓa raba tsakanin yaro da tsoho, ko tsakanin dutse da itace.

Tufanul -Aqsa ya kasance yaƙi na ruhu kafin jiki, da ƙarfi kafin makami. Abin da na bar ba wani gado na mutum ba ne, a'a gado ne na haɗin kai, ga kowanne Falastin da ya yi mafarkin 'yanci, ga kowanne uwa da ta ɗauki ɗanta a kafadarta yayin da yake shahidi, ga kowanne uba da ya yi kuka da zafi akan yarinyarsa da aka kashe da harsashi mai ƙyama.

Wasiyyata ta ƙarshe, ku tuna koyaushe cewa juriya ba a banza take ba, ba kawai harsashi bane da aka harba, a'a rayuwa ce da muke rayuwa da daraja da girmamawa. Kurkuku da kullewa sun koya mini cewa yaƙi yana da tsawo, kuma hanyar tana da wahala, amma na kuma koyi cewa al'umma da ke ƙin yarda da juriya suna ƙirƙirar rauni da ƙasƙanci da hannayensu.

Kada ku jira duniya ta ba ku hakki, domin na rayu kuma na shaidi yadda duniya tayi shiru a game da zalintar mu.
Kada ku jira adalci, a'a ku zama ku ne adalci. Ku ɗauki mafarkin Falasdinu a cikin zukatanku, ku sanya kowanne rauni a matsayin makami, da kowanne hawaye a matsayin tushen fata.

Wannan shine wasiyyata: kada ku mika makaman ku, kada ku dena jefa dutse, kada ku manta da Shahidan ku, kuma kada ku yi musanya akan mafarkin da yake hakkin ku. Muna nan muna zaune, a ƙasar mu, a cikin zukatamu, da kuma a cikin makomar 'ya'yanmu.

Ina ba ku shawara da rike Falasdinu, ƙasar da nake ƙauna har zuwa mutuwa, da mafarkin da na ɗauka a kafaduna kamar dutse da ba ya yi lanƙwashewa.
Idan na faɗi, kada ku faɗi tare da ni, aa ku ɗauki tutar da ba ta faɗi ba, ku sanya jini na a matsayin gada da za ta wuce ta, wanda zai haifar da wani zamani da ya taso mai ƙarfi. Kada ku manta cewa ƙasa ba labari bane da za a ba da labari, a'a gaskiya ce da ake rayuwa, kuma a kowane shahidi da ya haifu daga wannan ƙasa, akwai dubban masu juriya.

Idan Tufan ya dawo kuma ban kasance a tsakanin ku ba, to ku sani cewa ni na kasance ɗaya daga cikin raƙuman 'yanci."(Da s**a bada rai)

Ku kasance masu tamkar ƙaya a cikin makogwaro, wannan guguwar ta Tufanul Aqsa babu juyawa kuma bazata taɓa lafawa ba har sai lokacin da duniya ta gane cewa mu ne masu gaskiya, kuma ba tamu ake ba a cikin rahotanni da Labaran duniya.

07/10/2024

ƘARIN HASKE SABON SHAFI (14): ƘARIN HASKEN ƘARIN HASKE

Yau shekara ɗaya kenan cif da fara rubuta ƙarin haske. 'Yan awowi da fara Ɗufanul Aqsa ke da wuya, aka farashi.

To Alhamdulillah a kan Ni'imarsa. Kuma madalla da Ƙarin Haske. Lallai kwalliya ta biya kuɗin Sabulu dana Omo.

A wannan fitar, ƙarin haske ne ake so a yiwa ƙarin haske.

Da farko dai Manufar farashi itace, taimakon taimakon gaskiya, taimakon raunana, mazlumai, wanda yake wajibi ne na addini. Kuma ana yinsa ne domin neman yardar Allah, kamar yadda ake yin Sallah da azumi. Ba domin ita kanta gaskiyar kawai ba.

Da kuma wayar da kan al'ummar Musulmi Hausawa game da rikicin gabas ta tsakiya, Gwagwarmayar Addinin Musulunci, da kuma buɗa masu idanunsu game da matsalolin Diplomasiyyah, geostrategy, geopolitics, Islamic political thought da Islamic eschatology (علم المعاد).

Musamman da yake mu a nan farfaganda ta yi yawa a kafofin yaɗa labarai, saboda duk na Yammatawa ne.

To ko ba a faɗa ba, duk wani mai bibiyar ƙarin haske ya san ƙarin haske ya yi Nasara ba ƙarama ba. Saboda wasu dalilai. Babba daga ciki shine, Salo da tsarin da aka bi wajen yin rubutun, da kuma Manhajin da aka zaɓa.

An yi amfani ne da Salo na critical analysis, domin bincike ta hanyar yin Nazari kulli domin fitowa da babban hoto, na kowace matsalar da aka tattauna. Ba kara zube yake ba, kuma ba bisa doron emotion yake tafiya ba. Hatta Nuqɗoɗin da aka sa emotion a ciki to an yi shi ne domin cimma wata manufa ta motsa Zukata ko shammaci, ga Maƙiya. Illa yan wurare kaɗan da bashariyya ta yi aikin nata.

Batun manhaji, da madogarar da aka rike wajen yin rubutun kuwa, ga bayaninsu kamar haka :
1. Duk wata matsala da za tattauna a cikin ƙarin haske, to ana fara nemo Matsaya game da ita ne, a cikin Al-Qur’an, kai tsaye, ko kuma ta hanyar kallon Darussan da Al-Qur'an ya zo dasu, domin su zamo Jagora wajen fahimtar na yau.
2. Dogara da Hadisan ma'asumai, da maganar manyan Malamai na addini, musamman Sayyid Qaed, Shaikh Ibraheem Zakzaky, Shahid Sayyid Nasarullah, Shahid Ahmad Yasin.

3. Karanta maƙaloli kala-kala daga bakin masana daban daban, daga sassa daban daban na Duniya, da s**a yi magana ko suke magana a kan wannan rikicin, domin fahimtar matsayarsu, da mahangarsa, tare da ɗorata bisa Mahangar Al-Qur’ani da itira. Domin tantancewa.

4. Saurare da kallon lakcoci kala-kala daga bakin gaggan masana na Duniya dake cikin jami'o'i daban daban a sassa daban daban na Duniya, domin fahimtar tasu matsaya game da wannan rikicin.
5. Bibiya Labarun yau da gobe, bibiya mai zurfi a kafafen yaɗa Labarun Yammatawa da gabastawa, dana musulmi, musamman na yan gwagwarmaya domin sanin me ke faru, domin ya taimaka wajen gane me zai iya faruwa a nan gaba.

6 Amfani da Nazari da Hankali, kafin kaiwa ga matsaya gamsasshiya.

7. Rashin damuwa da reaction ɗin masu karatu. Na yabo ko s**a. Wato rubutun ya kasance ne tamkar wani numfashi da mai shi yake yi, domin ya faɗi matsayarsa a kan abunda ke faruwa. Idan wani ya ji abun ya mai to muwafaqa ce s**a yi. Wanda kuma ya ji bai masa ba, to ba za a damu da masa Raddi ba, koda ya kawo tasa Mahangar, ko yayi s**a. Sai ya zamo ba a Shagaltar da hankali wajen kulawa da me ake cewa ba. An fi damuwa da bayanin waqi’i kawai. Illa dai tare da haka akwai niyyar jin cewa aikin na addini ne. Don haka Allah ya kamata a nufa dashi, tsammanin ko zai karɓa.

Alhamdulillah, cikin Ikon Allah Zukata sun karɓa, Kwakwale sun amfana.

Allah ya tsare karin haske, sai ya zamo daidai a cikinsa ya fi kuskure yawa.

Wannan albarkar samun Jagoranci na gari ne. Jagorancin da ya nuna mana hanya, ya saita mu, ya inganta mana rayuwa, ya gyara mana zuciya, ya tayar damu bacci, har yau gashi baƙaƙe na jin cewa suma sunada ta cewa, a cikin rikicin Duniya.

Allah ya ƙarawa Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky lafiya da nisan kwana. Mun gode Jagora. Mun gode. Mun gode.

A Taƙaice kenan game da Ƙarin Hasken karin haske 🥰

Shamsudeen Hassan
7/10/2024

PRESS RELEASE MUSLIM WORSHIPPERS WERE KILLED IN A MOSQUE IN GEIDAM, YOBE STATE. Available and verifiable information rea...
30/08/2024

PRESS RELEASE

MUSLIM WORSHIPPERS WERE KILLED IN A MOSQUE IN GEIDAM, YOBE STATE.

Available and verifiable information reaching us confirmed that Muslim worshippers were attacked in a mosque in Geidam, Geidam Local Government, Yobe State. The attack was made while the worshippers are praying in a mosque of Fudiyyah Islamiyyah School, Geidam, Yobe State. The school belongs to the adherents of his Eminence, Sayyid Ibraheem Ya’qoub El-Zakzaky (H).

This attack has come at a time when the Inspector General of Police, Kayode Egbetokun, ordered operatives of the Nigeria Police to crackdown on and arrest the adherents of the Islamic Movement, under the leadership of his eminence Sayyid Ibraheem Ya’qoub El-Zakzaky. The order was given by Kayode Egbetokun on Monday, 26 August 2024.

Hours after his order on the same Monday, August 26, 2024, the police raided a Fudiyyah Islamiyyah School, Airport Road, Abuja. The school belongs to the adherents of his eminence, Sayyid Ibraheem Ya’qoub El-Zakzaky (H). During the attack on Monday, the police vandalised school facilities and arrested innocent people living around the school.

The following day, on Tuesday, August 27, 2024, the same police raided the University of Abuja Teaching Hospital, Gwagwalada, Abuja, in search of 2024 Abuja Arba’een mourners.

The attack in Geidam happened around 4 a.m. on the early hours of Friday, August 30, 2024, during midnight and morning prayers. An eyewitness confirmed to us that the attackers killed three worshippers at the mosque, which include Shaheed Ahmad Abdurrahman, Shaheed Muhammad Saleh, and Shaheed Abdullahi Unguwar Karau Kawo. Apart from those killed, numerous people sustained injuries.

Paramedics are still handling the situation, and more details will be made available to the public in due course.

We are still assessing the situation and also analysing these new calculated trends that the Nigeria Police are taking by disguising under attacking Arba'een mourners and abuse the sanctity of Muslims and Islam.

The public may wish to recall that recently, police forcefully removed the hijab of Muslim sisters arrested during 2024 Abuja Arbaeen. After blasphemy on hijab and Islam by the police in Abuja and now abuse to Muslim worshippers and mosques in Geidam, Yobe State.

We condemn this attack and killing of Muslim worshippers in mosque in Geidam, Geidam Local Government, Yobe State, and vow to take necessary action against the perpetuators of this devilish act.


Shaikh Sidi Munir Mainasara
For the Islamic movement, under the leadership of his eminence Sayyid Ibraheem Ya’qoub El-Zakzaky (H),

30 August, 2024

KISAN KIYASHI: Sojojin mamaya na Isara'ila sun kashe Falasɗinawa goma 10, da s**a haɗa da ƙaramin yaro ɗaya da tsofaffi ...
22/02/2023

KISAN KIYASHI: Sojojin mamaya na Isara'ila sun kashe Falasɗinawa goma 10, da s**a haɗa da ƙaramin yaro ɗaya da tsofaffi guda biyu. Aƙalla mutane sama da ɗari ne s**a jikkata.

Hakan ya biyo bayan wani mummunan hari da sojojin mamaya na Isara'ilan s**a kai a birnin da ke yammacin gaɓar kogin Jordan yau Laraba.

.🇵🇸
.✊

Hotuna| Hotunan wasu gidajen Falasɗinawa da sojojin mamaya na Isara'ila s**a kai wa hari da makami mai linzami s**a rush...
26/01/2023

Hotuna| Hotunan wasu gidajen Falasɗinawa da sojojin mamaya na Isara'ila s**a kai wa hari da makami mai linzami s**a rushe, a harin da s**a kai yau Alhamis a garin jenin dake gaɓar yammacin kogin Jordan.




.

A cikin ƴan sa'o'i kaɗan a yau sojojin mamaya na Isara'ila, sun kashe Falasɗinawa tara (9) da s**a haɗa da wata tsohuwa,...
26/01/2023

A cikin ƴan sa'o'i kaɗan a yau sojojin mamaya na Isara'ila, sun kashe Falasɗinawa tara (9) da s**a haɗa da wata tsohuwa, a wani mummunan farmaki da s**a kai a sansanin da ke gaɓar yammacin kogin Jordan, in da wasu aƙalla ashirin (20) s**a jikkata.

Ahmed Manasra grows older behind Israeli occupation prison bars 💔🇵🇸Ahmed, who was arrested as a child at the age of 13, ...
25/11/2022

Ahmed Manasra grows older behind Israeli occupation prison bars 💔🇵🇸

Ahmed, who was arrested as a child at the age of 13, will turn 22 while still in solitary confinement.

ᎻᎪᏢᏢᎽ ᎬᏆᎠ ᎷႮᏴᎪᎡᎪᏦ.𝘈𝘭'𝘶𝘮𝘮𝘢𝘳 𝘗𝘢𝘭𝘦𝘴𝘵𝘪𝘯𝘦 𝘯𝘢 𝘚𝘩𝘢𝘨𝘶𝘭𝘭𝘶𝘯𝘢𝘯 𝘚𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘬𝘢𝘧𝘪𝘯 𝘢 𝘧𝘢𝘳𝘢 𝘩𝘶𝘥𝘶𝘣𝘢𝘳 𝘚𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘢 𝘑𝘦𝘳𝘶𝘴𝘢𝘭𝘦𝘮 𝘗𝘢𝘭𝘦𝘴𝘵𝘪𝘯𝘦.
09/07/2022

ᎻᎪᏢᏢᎽ ᎬᏆᎠ ᎷႮᏴᎪᎡᎪᏦ.

𝘈𝘭'𝘶𝘮𝘮𝘢𝘳 𝘗𝘢𝘭𝘦𝘴𝘵𝘪𝘯𝘦 𝘯𝘢 𝘚𝘩𝘢𝘨𝘶𝘭𝘭𝘶𝘯𝘢𝘯 𝘚𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘬𝘢𝘧𝘪𝘯 𝘢 𝘧𝘢𝘳𝘢 𝘩𝘶𝘥𝘶𝘣𝘢𝘳 𝘚𝘢𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘢 𝘑𝘦𝘳𝘶𝘴𝘢𝘭𝘦𝘮 𝘗𝘢𝘭𝘦𝘴𝘵𝘪𝘯𝘦.


Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin Falasdinawa da sojojin mamaya na Isra'ila s**a kashe a West Bank da birnin Kudus da...
05/07/2022

Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin Falasdinawa da sojojin mamaya na Isra'ila s**a kashe a West Bank da birnin Kudus da s**a mamaye ya karu da kashi 46 cikin dari a farkon rabin shekarar 2022 idan aka kwatanta da na shekarar da ta gabata.

05/07/2022

The Algerian solidarity with Palestine is intrinsic to every Algerian🇵🇸❤️🇩🇿

In solidarity with Palestine, two Algerian athletes raised the Palestinian flag after winning the gold and silver medals in the 800m race during the Mediterranean Games in Oran city. gazaapost.com/en

Address

Sabuwar Unguwa Kofar Kaura Katsina
Katsina
PALESTINE��

Telephone

+2347043477742

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Raunanan Duniya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Muryar Raunanan Duniya:

Share