Hausa Post

Hausa Post Hausa News Updates
(1)

Kwankwaso ya yi Gwamna sau biyu a tsittsinke, yayi Sanata bai taɓa cewa komai a majalisa ba, ya yi Ministan tsaro amma b...
05/08/2023

Kwankwaso ya yi Gwamna sau biyu a tsittsinke, yayi Sanata bai taɓa cewa komai a majalisa ba, ya yi Ministan tsaro amma bai san komai kan tsaron ba - Cewar Ganduje

Me za ku ce?

A cikin kwana 100 da ABBA GIDA GIDA yace zai inganta ilimi, da rayuwar Al,ummah,,yau saura kwana 30.Ko kun ga alamar gya...
05/08/2023

A cikin kwana 100 da ABBA GIDA GIDA yace zai inganta ilimi, da rayuwar Al,ummah,,yau saura kwana 30.

Ko kun ga alamar gyaran kuwa?

LABARI MAI DADIYANZU-YANZU: Sanatocin Najeriya sunyi fatali sunki amincewa da bukatar Tinubu na a tura sojoji don ya*kar...
05/08/2023

LABARI MAI DADI

YANZU-YANZU: Sanatocin Najeriya sunyi fatali sunki amincewa da bukatar Tinubu na a tura sojoji don ya*kar sojojin juyin mulki na kasar Nijar.

Sanatotin sunyi fatali da bukatan shugaban kasar ne a zaman su na yau Asabar, da suke gudanarwa yanzu haka.

✍️ Comr Abba Sani Pantami

A Nan Nijeriya Na San Gwamnan Da A Lokacin Da Yake Kan Mulki 'Yarsa Saboda Jiji-Da-Kai Da Katan Din Ruwan Gora (Swan Wat...
05/08/2023

A Nan Nijeriya Na San Gwamnan Da A Lokacin Da Yake Kan Mulki 'Yarsa Saboda Jiji-Da-Kai Da Katan Din Ruwan Gora (Swan Water) Take Wanka, Amma Bayan Baban Ya Sauka Daga Mulki Talauci Ya Yi Masa Katutu, Daga Karshe Mahaifiyarta Sai Ta Sayar Da Zobo Kafin A Yi Cefane A Gidansu, Cewar Sheik Kabiru Gombe

Sabuwar Kujerar Ganduje
03/08/2023

Sabuwar Kujerar Ganduje

Matashiya Maryam Shetty Kenan Ke Sujaddar Yi Wa Allah Godiya Bayan An Bayyana Sunanta A Matsayin Minista
03/08/2023

Matashiya Maryam Shetty Kenan Ke Sujaddar Yi Wa Allah Godiya Bayan An Bayyana Sunanta A Matsayin Minista

BAYAN MUTUWAR AURENTA: Jarumar Finafinan Kannywood, Hafsat Idris Daga Dandalin Ɗaukar Fim Mai Dogan Zango, Manyan Mata (...
02/08/2023

BAYAN MUTUWAR AURENTA: Jarumar Finafinan Kannywood, Hafsat Idris Daga Dandalin Ɗaukar Fim Mai Dogan Zango, Manyan Mata (Season 2)

Babu Zanga-Zanga A Cikin Tsarin Karantarwar Addinin Musulunci. Idan Kuma Kana Da Hujjar Zanga-Zanga Sai Ka Kawo Mana!, C...
02/08/2023

Babu Zanga-Zanga A Cikin Tsarin Karantarwar Addinin Musulunci. Idan Kuma Kana Da Hujjar Zanga-Zanga Sai Ka Kawo Mana!, Cewar Hafiz Ibrahim Iliyasu

Babu Wata Ribar Azo A Gani A Cikin Aure ~ Inji 'Yar Gwagwarmaya Zainab Naseer AhmadYayin da yawancin lokuta iyaye ke All...
02/08/2023

Babu Wata Ribar Azo A Gani A Cikin Aure ~ Inji 'Yar Gwagwarmaya Zainab Naseer Ahmad

Yayin da yawancin lokuta iyaye ke Alla-Alla su sanya yayan su mata dakunan mazajen su domin gujewa sharrin zamani da kuma lalacewar tarbiyya, sai gashi wata matashiya mai amfani da yanar gizo da ake Kira Zainab Nasir Ahmad, tace mutane ne kawai ke zuzuta aure kai kace akwai wata babbar nasara a cikin sa, sai dai a zahirin gaskiya wannan tunani shirme ne kawai hasalima babu wani abun azo a gani a cikin sa.

Tace "mutane sai suyi ta zambatar yarinya idan takai matakin aure kuma batayi ba, wannan dalili ne yasa sai kaga wasu mazan ma na tunanin kamar alfarma s**ayi miki in s**a tunkare ki da zummar aure."

A cewar ta, "shifa aure abu ne daya kacal na rayuwa, kuma ba kowa ne zaiyi shi ba, tace a gaskiya ya kamata a daina musguna musu akan cewa wai lallai sai sunyi aure."

Ta kuma kara da cewa, ba kuma wai don mace tayi aure hakan na nufin cewa tafi wadanda basuyi bane, duk daya suke.

Daga karshe sai ta kara jaddada cewa ba shakka babu wani abun azo a gani a cikin aure.

Menene ra'ayinku akan hakan?

YANZU-YANZU: Majalisar Dattawa Ta Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Yi Hakuri Ta Dakatar Da Zanga-Zangar Da Take YiDaga Comr A...
02/08/2023

YANZU-YANZU: Majalisar Dattawa Ta Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Yi Hakuri Ta Dakatar Da Zanga-Zangar Da Take Yi

Daga Comr Abba Sani Pantami

Yanzu haka Sanata Ali Ndume ne ya wakilci shugaban majalisar dattawan Najeriya, wurin tattaunawa da kungiyar kwadago NLC a cikin farfajiyar majalisar dokokin Najeriya.

A yayin tattaunawar Sanata Ali Ndume ya bawa kungiyar hakuri tare da kira a gare su da suyi hakuri su janye yajin aikin, tare da musu alkawarin majalisar dattawan Najeriya za ta shiga tsakani don ganin an shawo kan matsalolin da s**a addabi al-ummar Najeriya.

Musulmai Sun Fi Yin Amfani Da Abinda Ĺìťťàfìñ 'Bible' Ya Ce Fiye Da Ķìŕìśťòçì, Cewar Reno Omokiri
02/08/2023

Musulmai Sun Fi Yin Amfani Da Abinda Ĺìťťàfìñ 'Bible' Ya Ce Fiye Da Ķìŕìśťòçì, Cewar Reno Omokiri

KASAR NIJER TA DAUKO HANYAR SAMUN 'YANCI DAGA MULKIN MALLAKAIna daga cikin wadanda s**a zargi Sojan da ya jagoranci kifa...
01/08/2023

KASAR NIJER TA DAUKO HANYAR SAMUN 'YANCI DAGA MULKIN MALLAKA

Ina daga cikin wadanda s**a zargi Sojan da ya jagoranci kifar da Gwamnatin Demokaradiyya a Nijer General Abdourahmane Tchiani a matsayin karen farautar Faransa, to amma bayan da naga abubuwa sun fara bayyana a zahiri da kuma tattaunawar da nayi da wasu daga Nijer, na fahimci wannan Sojan ba karen farautar Faransa bane

Don haka na fita daga cikin masu ganin Sojan a matsayin karen Farautar Faransa, asalima yana so ne ya jaddada kudurin Muhammad Bazoum na yanke alaka gaba daya tsakanin Nijer da Faransa don Nijer ta samu 'yanci, sannan har ya fara aiwatar da hakan ta hanyar rufe dukkan kamfanonin Kasar Faransa masu hakar sinadarin Uranium wanda ake hada makamashin Nukiliya da shi

Kuma sai gashi hatta su fararen hula dake Nijer din sun fara nuna cikakken goyon bayansu akan Sojojin da s**a kwace mulki, saboda suma sun gaji da mulkin mallakar da Faransa take musu

A yanzu haka, sanarwa ya fito daga Shugaban Kasar Algeria cewa zasu bawa Sojojin Nijer agaji idan ECOWAS da Faransa s**ace zasu kaddamar da hari, Algeria itace Kasa na biyu ko uku a karfin Soji a wannan nahiya tamu ta Afirka

Shi wannan tsarin Mulkin Demokaradiyya tun asali bai dace da Kasashen Afirka ba, adon turawa ne, mulkin Soja ba abin aibi bane idan Sojojin sun kasance masu kishi gaskiya da rikon amana

A mulkin Soja babu jan lokaci wajen aiwatar da abubuwa, sannan akwai tsaro, idan talaka ya samu tsaro ya je gona ya noma abincin da zaici ya rayu to bai da wata matsala

Kasar Mali tana daga cikin Kasashen da Sojoji s**ayi juyin mulki kuma s**a yanke alaka tsakaninsu da Faransa, yanzu haka al'amura sun fara daidaita a Mali

Yanzu abinda ya bayyana a garemu shine ECOWAS ne karyan farautar Faransa da take so ta tura yaran mutane Yaki a zubar da jini, don haka mu saka Nijer a addu'ah, Insha Allahu ba za'ayi Yaki ba, kuma Insha Allahu Nijer zata samu 'yanci daga mulkin mallakar Faransa

Muna rokon Allah Ya rusa mugun shirin Faransa a nahiyar Afirka

Girman Mazakuta, Tsawon Mazakuta, Fadin Mazakuta, Karfin Mazakuta Duk Zaka Samu Acikin Kankanin Lokaci Idan Kayi Wannan ...
29/07/2023

Girman Mazakuta, Tsawon Mazakuta, Fadin Mazakuta, Karfin Mazakuta Duk Zaka Samu Acikin Kankanin Lokaci Idan Kayi Wannan Hadin Magani Mai Sauki

Karfi da girman azzakari domin gamsar da amarya 👇👇 MAGANIN KARFIN MAZA A SAUKAKE BA TARE DA WATA ILLA KO MATSALA GA GANGAR JIKIN MUTUM BA....

Ashe Makashinka Yana Nan Tare Dakai. 🇳🇪🥲Wannan Maganar Gaskiya Ce.Allah Yayi Mana Tsari Da Makiya Ameen
27/07/2023

Ashe Makashinka Yana Nan Tare Dakai. 🇳🇪🥲
Wannan Maganar Gaskiya Ce.
Allah Yayi Mana Tsari Da Makiya Ameen

Halin da ake ciki a kasar Niger a yanzu haka.Har yanzu shugaban kasa Bazoum yana hannun sojojin da ke kokarin yin juyin ...
26/07/2023

Halin da ake ciki a kasar Niger a yanzu haka.

Har yanzu shugaban kasa Bazoum yana hannun sojojin da ke kokarin yin juyin mulki a kasar, kuma fadar shugaban kasar na cigaba da tafiyar da shafukan ta na sada zumunta.

Har zuwa yanzu babu wata sanarwar da ta bayyana cikakken halin da ake ciki a fadin kasar baki daya.

Abubuwa guda biyu ne kawai aka tabbatar, na farko shine jaridar "Air-Info Agadez" ta ruwaito cewa har zuwa yanzu shugaban kasar Bazoum bai sanya hannu kan takaddar ajiye mulki ba.

Na biyu shine shugaban ECOWAS Bola Tinubu, ya tura tawagar jami'an tsaro na musamman da kuma shugaban jamhuriyar Benin Patrice Talon, da wasu tawagar tsoffin Gwamnonin Najeriya sun isa Yamai domin fara tattaunawa da sojin kasar Niger da suke tsare da Bazoum.

Wasu gidajen Rediyo da talabijin na kasar suna cigaba da gudanar da shirye-shiryen su kamar yadda s**a saba.

Har zuwa yanzu sojojin da ke cigaba da tsare Bazoum basu ce uffan ba, bayan sunce za su gudanar da jawabi yau da misalin karfe 8 na dare.

Abunda ya kamata mu cigaba da yiwa mutanen Niger shine, mu cigaba da musu Addu'a, Allah ya kare su daga makircin da ake kokarin kulla musu. Wata kila zuwa cikin dare ko zuwa da safe su bayyana halin da ake ciki a kasar.

AZUMIN TARA DA GOMA GA WATA KAYI AZUMI GOBE DA JIBI TARA GA WATA DA GOMA GA WATA TASU'A Da ASHURA
26/07/2023

AZUMIN TARA DA GOMA GA WATA

KAYI AZUMI GOBE DA JIBI TARA GA WATA DA GOMA GA WATA TASU'A Da ASHURA

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share