18/02/2022
Al'ummar jihar Kano ta yi Allah wadai da uwar jam'iyyar APC ta Kasa
Kotun daukaka kara karkashin masu shari'a 3 ta zauna a Abuja Alhamis 17/2/2022 domin yanke hukuncin shari'ar da tsagin gwamnatin Kano ta daukaka akan zaben shugabannin jam'iyyar a matakin mazabu da kananan hukumomi da kuma neman sanin ko babbar kotun da ta fara yin shari'ar tana da hurumin yin shari'ar ko bata dashi
A lokacin da suke yanke hukuncin, sun bayyana cewa, su kansu basu da hurumin sauraron wannan shari'ar ballantana babbar kotun da ta fara yin shari'ar, sakamakon haka, ta umarci a koma wajen uwar jam'iyyar ta kasa a sasanta da masu korafin tunda rigimace ta cikin gidan jam'iyya.
Babu inda kotun daukaka karar ta ambata wanda zai zama shugaban jam'iyya a kowane tsagi, haka kuma babu inda ta ambata wanda yayi sahihancin zabe a kowane tsagi ko akasin haka, bisa dalilin ta na rashin hurumin sauraron shari'ar kamar yadda ta fada tun da farko.
Babban abin mamaki da takaici, maimakon uwar jam'iyyar ta APC ta sake neman kowane tsagi domin a sake komawa teburin sulhu, duba da jadawalin da ta fara bujiro da shi tun farkon sulhun, yaci karo da adalcin yin sulhu a tsakankanin masu jayayya, abinda ya jawo bangaren G7 su ka yi fatali da shi kenan.
Sai kawai uwar jam'iyyar ta APC ta dauke kai daga umarnin da kotun daukaka kara ya bayar na a koma wajen ta domin sasantawa, kai tsaye ta dankawa tsagin gwamnati takardar shaidar zama shugaban jamiyya na jihar Kano, duba da yadda tsagin gwamnatin Ganduje su ka bayyana a kafafen sada zumunta na zamani suna cin mutunci da keta alfarmar tsagin G7, jim kadan bayan yanke hukuncin.
Idan ba'a manta ba, uwar jam'iyyar ta janye bada takardar shaidar cin zabe wato satifiket ga kowane tsagi a jihar Kano, duk da tasan wata babbar kotu tayi hukuncin bai wa tsagin G7 nasara, amma uwar jam'iyyar ta gaza mutunta wannan hukunci, kamar yadda ta mutunta sabon hukunci wata kotun a halin yanzu, kai tsaye ya nuna dama akwai wata kullalliya daga ita uwar jam'iyyar domin wofantar da tsagin G7
Idan ba kullalliya ba, me yahana tun farkon hukuncin da babbar kotu ta yi, ba su dauki satifiket sun ba Danzago ba, sai gashi nan take bayan hukuncin kotun daukaka kara, sun dauka sun ba tsagin gwamnati?
Idan kuma sunyi la'akari ne da cewar tsagin gwamnatin Ganduje sun daukaka kara, shine ya hana su ba kowa satifiket din a wancan lokaci, to yanzu ma kowa yasan cewa tsagin G7 su ma zasu iya daukaka kara zuwa kotun Allah ya isa.
Wannan ne dalilin da yasa muke zargin wata kullalliya daga uwar jam'iyyar ta APC
Uwar jam'iyyar tana sane, cewa maganar tana kotu amma ta bujiro da maganar sulhu tun da farko, sai gashi ta gaza daukan wani kwakkwaran matakin sulhu duk da korafin da bangaren G7 s**a gabatar a gaban ta na rashin yin adalci da daidaito a jadawalin da uwar jam'iyyar ta bujiro dashi na yin sulhun, wannan ya nuna ba dagaske sulhun ne a gaban su ba, wata aniya ce ta wofantar da tsagin G7
Duk ta inda uwar jam'iyyar ta bullo jama'a na kallon ta, wannan ne dalilin da yasa al'ummar jihar Kano, basu nuna farin ciki bisa wannan hukunci ba, duk majalasin da ka zauna zakaji ana yin Allah wadai, al'ummar Kano wayayyu ne a siyasance, matukar an zalinci wani bangare, a shirye suke da yin tofin Allah tsine hade da tausayawa wanda aka zalinta, tun daga kan 'yan jam'iyya har wadanda basa yin siyasa, aje a duba tarihi.
Ko shakka babu wannan zai ba jam'iyyar APC matsala babba a kakar zabe ta 2023 inda zai yi wahala ta kai banten ta.