Fityanul islam kano state branch

Fityanul islam kano state branch save our islam is our priority

26/05/2021

Fityanul Islam

10/09/2020

IBNU UMAR (R.A) YACE: "Muna Zaune tare da ANNABI (S.A.W)
Watarana, sai ga Wani Tsoho mai mummunar siffa, mai yagaggun sutura, Mai doyin jiki k**ar Mushe, Ya shigo wajen, Ya ratso cikin Jama'a, yana tattaka wuyan Mutane, yana tutture kafadunsu, har sai da yazo ya zauna a gaban ANNABI (S.A.W).
Sai yace wa ANNABI (S.A.W): "Waye ya Halicceka?"
Sai ANNABI yace masa: "ALLAH NE"
Sai yace: "Waye ya Halicci Sammai?"
Sai ANNABI (S.A.W) yace Masa "ALLAH NE"
Sai yace: "Waye ya halicci Qassai?"
Sai ANNABI (S.A.W) yace masa "ALLAH NE"
Budar bakin Mutumin nan sai yace: "TO SHI ALLAH DIN WAYE YA HALICCESHI?"
Jin wannan Kalamin sai ANNABI (S.A.W) yace: "SUBHANALLAH!"
Sai ya rike goshinsa, ya Sunkuyar da kansa Qasa, Shi kuwa wannan Tsohon sai ya tashi ya fita.
Da ANNABI (S.A.W) ya cira Kansa sai yace: "KU KAMO MIN MUTUMIN NAN!"
Sai muka fita neman sa, mukayi ta dubawa bamu ganshi ba.
Sai ANNABI (S.A.W) yace: "IBLEES NE YAZO DOMIN YA SA MUKU KOKWANTO ACIKIN ADDININKU"
IMAM AL-BAIHAQY ne ya ruwaitoshi acikin "DALA'ILUN NUBUWWAH", juzu'I na 7 shafi na 125.
Daga Sayyiduna ABDULLAHI bn UMAR (R.A).Ibnu Hibban da Abu Zur'ah sun inganta shi.
Allah yakara tsare mana imanin mu ya kuma karemu daga sharrin shaidan la'a nanne Bijahi S.A.W. Amiin

09/09/2020
07/09/2020

BARKA

07/09/2020

ZINA;

Hakika ZINA Tana Daga Cikin Mafiya Girman Laifuffuka. Kuma ALLAH Yana Yin Azaba Mai Tsanani Ga Masu Yinta.

Shi Yasa MANZON ALLAH(S.A.W) Ya Ce:

"BAYAN YIN SHIRKA GA ALLAH, BABU WANI LAIFI MAFI GIRMA KAMAR; MANIYYIN DA NAMIJI YA JEFA A CIKIN MAHAIFAR DA BATA HALATTA GARE SHI BA".

Sannan Ya Ce;"LALLAI AZABAR ALLAH TA TSANANTA GA MAZINATA".

ALLAH Yana Faɗar Halayen Bayinsa Muminai, Daga Ciki Sai Yake Cewa:

"SUNE WADANDA BASU KIRAN WANI ABIN BAUTA DABAN TARE DA ALLAH, KUMA BASU KISAN WANI RAI WANDA ALLAH YA HARAMTA SAI DAI DA GASKIYA, KUMA BASU YIN ZINA".

"DUK WANDA YA AIKATA WANNAN(ZINA) ZAI HADU DA AZABA"

"ZA'A NINKA MASA AZABAR A RANAR ALQIYAMAH, KUMA ZAI DAUWAMA A CIKINTA YANA MAI TSANANIN BAKIN CIKI".

"SAI DAI WANDA YA TUBA KUMA YAYI IMANI KUMA YA AIKATA AYYUKA NA KWARAI, TO WADANNAN SUNE WADANDA ALLAH YAKE JUYAR DA MUNANAN AYYUKANSU ZUWA KYAWAWA. HAKIKA ALLAH YA KASANCE SHI MAI GAFARA NE MAI JIN 'KAI".

(Suratul Furqan Ayah Ta; 68 - 70).

ALLAH YA KARE MU DA ZURI'ARMU BAKI DAYA DAGA AFKAWA TARKON ZINA AMEEEEN.

(Daga; Othman Muhammad).

07/09/2020

HANYOYI GUDA ASHIRIN DA BIYAR (25) NA SAMUN SHIGA ALJANNAH!
1. ANNABI (S.A.W) yace : ''Duk wanda ya Gina ma Allah Masallaci, to Allah zai gina masa gida a cikin Aljannah.
(Bukhari da kuma, Tirmidhi hadisi
na 318)
2. ANNABI (S.A.W) Yace : ''Wanda yayi Salloli biyu na sanyi (Sallar La'asar da Sallar Asuba) zai shiga Aljannah. '' (Bukhari)
3. An karbo Hadisi daga Abu Hurairah (RA) yace : ANNABI (S.A.W) Yace : ''Duk wanda yace : ''SUBHANALLAHI WABIHAMDIHI, SUBHANALLAHIL-AZEEM.'' Sau bakwai (7)
za'a gina masa bene a cikin Aljannah.
''Al-wabilus Sayyib Shafi na 77.''
4. Jabir, Allah ya yarda dashi, yace: ANNABI (S.A.W) Yace : ''Wanda yace : ''SUBHANALLAHIL-AZEEM WA BIHAMDIHI. '' za'a dasa masa bishiyar Dabino a cikin Aljannah.''
5. ANNABI (S.A.W) Yace : ''Duk Wanda Qarshen Maganarsa ta kasance ''LA'ILAHA ILLALLAH.'' zai shiga Aljannah.'' (Abu Dawud)
6. ANNABI (S.A.W) Yace : ''Duk wanda Yace : ''Ya Allah Ina Rokonka, ka Shigar dani Aljannah sau ukku (3) (Allahumma Inniy As'alukal jannah) ALJANNAH ZA TA CE : ''Ya Allah ka shigar dashi Aljannah.''
(Tirmiziy ne ya ruwaita shi)
7. ANNABI (S.A.W) Yace : ''Ya ku Mutane ku watsa Sallama, kuma ku ciyarda da Abinci ga mai jin yunwa, kuma kuyi Sallah lokacin da Mutane ke bacci (da dare) sai ku shiga Aljannah da Aminci.''
(Tirmiziy ne ya ruwaito shi)
8. ANNABI (S.A.W) Yace : ''Lallai Allah yanada sunaye sasa'in da tara (99), Duk wanda yasan Ma'anar su kuma ya kiyayesu Zai shiga Aljannah.
'' (Bukhari)
9. ANNABI (S.A.W) Yace : ''Wa zai Lamunce min Abinda ke tsakanin Habobinsa guda biyu da kuma Abinda ke tsakanin kafafunsa biyu (Wato : Harshen sa da kuma Farjinsa) In Lamunce masa Shiga Aljannah.''
( Sahih Bukhari )
10. An kar6o Hadisi daga Aisha (RAH) tace : ANNABI (S.A.W) Yace : ''Duk wanda ya ga wata kafa a cikin Sahu kuma ya toshe, Allah zai gina Masa gida a cikin Aljannah kuma zai daukaka darajarsa a cikin Aljanna.'
Allah yasa mu dace. Amiin

26/08/2020

SHARUDAN JAM'I DAN WAZIFA DA ZIKIRIN JUMA'A.

Daga Muhammad Hussaini (Yaseen)

Kamar yadda muka sani wazifa da zikirin juma'a wajibi ne ga dukkanin 'yan Tijjaniyya kuma acikin mutane akeyi ma'ana jam'i, toh akwai sharadin cewa duk wanda yashiga wannan darika ta MANZON ALLAH, Jam'i zainayi muddin bawani dalili mai karfi Wanda Addini ya yarda cewa uzurine.

1. Idan mutane sun hada gari, toh bashakka suyi jam'in wazifa da zikirin juma'a.
2. Karka walakanta ko ka ki haduwa ayi jam'i dakai domin hakan zai jawo kayi asara na Lada mai yawa.
3. Kuma sharadine ko ayi sahu sahu ko kuma ayi halqa ma'ana cycle ko zagaye ko four angle.
4. Kuma sharadine mutum yana bayyanawa, karyayi shuru a wajen wazifa ko zikirin juma'a, amma banda mata dominsu muryarsu al'aurace.
5. Kuma kar ahadu maza da mata a wajen wazifa ko zikirin juma'a don shaidan zai iya shigarda wani abu cikin lamarin, sannan ALLAH yahana haduwan maza da Mata domin haka Babu wannan a cikin Addini da Darika.

Wandannan kadan daga ciki kenan ALLAH yasa mudace ameen.

23/08/2020

SABUWAR SHEKARA

Kungiyar Fityanul Islam Ta Kasa Sheikh Dr, Muhammadul Arabi Abul Fath (RA), Na Taya Daukacin Al'ummar Musulman Duniya Murnan Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci 1442.

Shugaban Kungiyar Na Kira Ga Al'umma Dasu Yawaita Gudanar Da Ayyukan Alkhairi A Rayuwar Su Na Yau Da Kullum, Su Tuba Da Aikata Duk Wani Aikin Da Shari'ar Musulunci Ta Hana.

Daga Baya Yayi Addu'an Allah Ya Mu Lafiya Da Zaman Lafiya, Ya Kiyaye Masifun Dasu Faruwa A Cikin Da Wajen Kasar Mu Najeriya.

Allah Ya Kiyaye Mu Da Sharrin Dake Cikin Wannan Shekaran, Alkhairin Dake Cikin Yaa Allah Ya Sadamu Dashi. Amiin
Haka kuma RARIYA tana kara kira ga 'yan uwa musulmi da su yi kokari wajen aikata alkairi a koda yaushe, don samun tsira a duniya da lahira.

Allah Ubangiji Ya sada dukkan al'ummar Musulmi da alkairan dake cikin wannan shekara, ya tsare mu da fitunun dake ciki.

30/07/2020



Kungiyar Fityanul Islam Ta Sake Shiryawa Domin Tattatara Sadakan Fatun Layya Na 2020

✍️ Rayyahi Sani Khalifa

Wannan kungiya mai albarka ta sake shiryawa domin tattara sadakar fatun layya na 2020 daga wajen al'umma musulmi musamman mabiya darikar tijjaniyya, k**ar yanda mafiya yawan al'umma s**a gani a shafukan sada zumunta cewa kungiyar Fityanul Islam na neman sadakar fatun layya k**ar yadda aka sana neman taimako a wurin al'umma domin gudanar da ayyukan ci gaba na gina makarantu da gidajen marayu da tallafin karatu da samar da tsare tsare na cigaban zamani ga al'ummar musulmi, musamman tijjanawa.

Ga duk mai niyyar bada wannan sadakar a kowani gari yake a fadin Najeriya ya kai babban masallacin juma'an garin su ya damka a hannun yan agajin fityanul Islam. Saboda kusan ko'ina a Najeriya muna da wakilai yan'agaji k**ar yanda kuka sani.

TSOKACI AKAN FITYANU DA IRIN MATSAYINTA A DARIKAR TIJJANIYYA

Ita dai wannan kungiya tana da rassa da shuwagabanni a kusan dukkan jahohin Najeriya, saboda haka tana da cikakken Structure ko tsarin da zata iya shirya jagorancin shawo kan matsalolin da s**a shafi darikar tijjaniyya. Kungiyar fityanul Islam ce kungiyar da mafiya yawan gwamnatocin jahohin Arewa s**a sani kuma suke alaka da ita a madadin wakiliyar al'ummar darikar Tijjaniyya gaba daya. Wannan kungiya nada cikakken tsarin da zai iya kawo sauyi ga matsalolin tijjaniyya amma sai dai rashin kudi da rashin hanyar samun kudin shiga ya hana kungiyar kawo wani cikakken shiri akan ci gaba, mu kuma k**ar yanda aka sanmu tijjanawa bamu iya bara da fadanci wajen masu mulki da shugabanni ba, dan haka bamu samun kudi.

Wannan dalili yasa muka ga ya dace mu fito mu nemi tallafi daga wajen yan uwa domin a samu abin da za'a gudanar da wannan hidima. A bara mun yinirin wannan yunkurin na tattara sadakar fatin layya kuma an dan samu kadan kasancewar a baran aka fara shirin amma bana insha Allahu an fadada abin, don haka yanzu muna kira da babban murya ga al'ummar musulmi musamman yan darika da su bada sadakan fatun layyansu ga wannan kungiya domin samar da cigaba ga tafiyan tijjaniyya.

Don Neman Karin Bayani

08039613999
07067762022
08038567388

Fityanu Media
Fityanul Islam Of Nigeria
28/07/2020

30/07/2020

volantry association

26/07/2020

TSAYA KA KARANTA;

Wata Rana MANZON ALLAH(S.A.W) Ya Shigo Masallacinsa Sai Ya Tarar Da Wasu Mutane Suna Ta Zance Suna Dariya.

Sai Ya Ce Musu:"Amma Da Ace Kuna Tunowa Da Mai Yanke Jin Dadi(Mutuwa) Da Wannan Ya Shagaltar Daku Daga Wannan Abin Da Nake Gani.

Ku Yawaita Ambaton Mutuwa Domin Wallahi Babu Wata Rana Da Zata Wuce Face Sai KABARI(Yayi Ma Kansa Kirari) Yana Cewa:

"NI NE GIDAN BAQUNTAKA! NI NE GIDAN KADAITAKA!! NI NE GIDAN TURBAYA!!! KUMA NI NE GIDAN TSUTSOTSI!!!"

Idan Aka Zo Binne MUMINI a Cikin Kabarinsa, Sai Kabarin Yace Masa:

"MARHABAN WA AHLAN.. WALLAHI KA KASANCE DAGA CIKIN MAFI SOYUWAR MUTANE A GARE NI A CIKIN MASU TAFIYA A DORON 'KASA.. YANZU IDAN AN BINNE KA A CIKI NA, NI NE SUTURARKA NI ZAN AIKATA MAKA SAKAMAKON IRIN ABINDA KA KASANCE KANA AIKATAWA NE".

Nan Take Za'a Fadada Masa Kabarinsa Har Iyakar Ganinsa, Kuma Za'a Bude Masa 'Kofa Zuwa Gidansa Na Aljannah.
*****
Amma Idan Aka Zo Za'a Binne KAFIRI Ko FAJIRI(Mai Aikata Manyan Laifuka) Sai Kabarinsa Ya Ce Masa:

"BA'A MARABA DA KAI, KUMA BA'A MURNA DA ZUWANKA, KUMA WALLAHI KANA DAGA CIKIN MUTANEN DA NAFI 'KINSU DAGA MASU TAFIYA A DORON 'KASA, YAU ZA'A BINNE KA A CIKINA, NI NE SUTURARKA, KUMA ZAN AIKATA MAKA SAKAMAKON IRIN AYYUKAN DA KA KASANCE KANA AIKATAWA".

Nan Take Sai Kabarin Ya Matse Shi, Har Sai 'Kasusuwan Haqarqarinsa Sun Shige Cikin Junansu.

(Sai MANZON ALLAH(S.A.W) Ya Sanya Yatsunsa Cikin Junansu a Bisa Misali).

Sannan Za'a Turo Masa Wasu Manyan MACIZAI GUDA SABA'IN(MASU MIYAGUN KAMANNI).; DA ACE 'DAYAN CIKINSU ZAI HURA 'KASAR DUNIYAR NAN DA BAKINSA, DA HAR ABADA DUNIYAR NAN BA ZATA TA'BA TSIRO DA CIYAWA BA.

ZASU YI TA SARANSA, SUNA CIZONSA HAR ZUWA LOKACIN DA ZA'A TAFI FILIN HISABI".

(- Imam Tirmizy Ne Ya Fitar Da Hadisin, Sannan Ibnul Jawzy Ma Ya Kawo Shi a Cikin Babi Na Biyu a Cikin Littafinsa Mai Suna; AHWALUL QUBOUR).

Inna Lillahi.....

YA ALLAH! KA AZURTA MU DA KYAKYKYAWAN 'KARSHE DA CIKAWA DA IMANI, KA KARE MU DAGA AZABAR KABARI DON ALFARMAR SHUGABA(S.A.W).

24/07/2020

...Tunanina Ya 'Kure Babu Abinda Yayi Saura, a Cikin Nazarin Ko Menene Ribar Musulmi In An Tabbatar Da Cewa; Iyayen Annabinsa Na Wuta.

"IMANIN ƊAYANKU BAYA CIKA SAI NA KASANCE MAFI SOYUWA A GARE SHI AKAN IYAYENSA DA ƳAƳAYENSA DA DUKKAN MUTANE" - Haka ANNABI MUHAMMADU(S.A.W) Ya Ce.

Babu Wani 'Da Na Gari Da Zai So Ace Iyayensa Na Wuta. Ƙurewar Butulci Ta Tuƙe Akan Mai Yiwa Iyayensa Fatan Azaba. Haka Babu 'Da Nagari Da Zai So Mai Ingiza Iyayensa Zuwa Mummunar Makoma Ko Da Kuwa Sun Cancanceta. Haka Babu 'Da Nagari Da Zai 'Ki Mai Son Iyayensa Da Yi Masu Kyakkyawar Fata. Wannan Duk Haka Batun Yake a Kowace Irin Zamantakewa.

In Mun Haɗe Zantukan Baya, Zamu Gane Irin Mummunar Ma'anar Da Yankewa Mahaifan ANNABI(S.A.W) Makoma Yake Bayarwa Akan Mai Aikata Hakan.

WANNAN RAYUWA TA YAU: ALLAH DAI YA FITAR DA MU.

(Daga; Othman Muhammad).

23/07/2020

Some Murid recites their morning and evening litanies (Lazim) in less than 2 minutes and wazifa (if alone) under 3 minutes as if they're fast as Jinn or Jet Lee.

You were created purposely for worship and nothing else. So where are you going that makes you talk to Allah with feverish haste?

Take your time and do it well with sincerity then, Allah will give you what ever you seek for, that is Ma'arifah

~ Wadman Waduud

23/07/2020

IMAM HASSAN Ya Amso Daga Abban Shi IMAM ALIY(R.A) Ya Ce:

MANZON ALLAH(S.A.W) Ya Ce: MALAIKA JIBRILU Yana Zantar Mani Cewa: "Hakika ALLAH Ya Sauko Da Wani Mala'ika Zuwa 'Kasa, Mala'ikan Nan Yana Tafiya Har Ya Zo Wajen Wani Mutum Yana 'Kwankwasa 'Kofar Wani Gida. Sai Mala'ikan Nan Ya Ce Mashi: Me Ya Kawo Ka Wannan Gida???

Sai Mutumin Ya Ce: 'Dan'uwana Ne Musulmi Na Zo In Ziyarce Shi Saboda ALLAH. Sai Mala'ikan Nan Ya Ce: ALLAH Babu Abinda Ya Kawo Ka Sai Wannan???

Sai Mutumin Nan Ya Ce: ALLAH Babu Abinda Ya Kawo Ni Sai Wannan. Sai Mala'ikan Nan Ya Ce: To Ni 'Dan Aiken ALLAH Ne Zuwa Gare Ka, ALLAH Ya Ce In Gaishe Ka Kuma Ya Ce: ALJANNA TA WAJABA GARE KA. Kuma Duk Musulmin Da Ya Ziyarci Musulmi To Ba Shi Ya Ziyarta Ba NI Ya Ziyarta, Kuma Sak**akonsa a Wajena Ita Ce ALJANNA".

(Alzuriyya Aldahira Alnabawiyya),

Ya ALLAH Ka Yarda Mu Rika Yin Ziyara Domin Neman YardarKa.

(Daga; Othman Muhammad).

21/07/2020

FALALAR KWANAKI GOMA NA FARKON WATAN ZUL HAJJI.
Daga Umar Chobbe.
An karbo Hadisi Daga ibn Abbas (R.A) ya ce Annabi (SAW) ya ce: Ranar daya ga watan zulhijja ita ce ranar da Allah (swt) Ya gafarta wa Annabi Adam (A.S). Duk wanda ya azimci wannan rana Allah(SWT) Zai gafarta masa kowane irin zunubi tsakaninsa da Shi.
(2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) Ya fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi. Wanda ya azimci wannan rana yana da lada kwatankwacin wanda ya raya shekara da ibada .
(3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Ya karbi addu’ar Annabi Zakariyya (A.S) Ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan rana Allah (SWT) Zai karbi adduo’in sa.
(4) Ranar hudu ga Zulhijja ita ce ranar da aka haifi Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya azimci wannan rana Allah Zai kare shi daga talauci da musibu.
(5) Ranar biyar ga Zulhijja ita ce ranar da aka haifi Annabi Musa (A.S). Duk Wanda ya azimci wannan rana Allah (SWT) Zai kare shi daga munafunci ko azabar kabari.
(6) Ranar shida ga Zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Ya Yi budin alkhairi ga Annabi (SAW). Duk wanda ya azimci wannan rana Allah Zai dube shi da rahama, kuma ba Zai azabtar da shi ba.
(7) Ranar bakwai ga Zulhijja ita ce ranar da Allah (SWT) Zai sa a rufe kofofin wuta, ba za a bude su ba har sai wadannan kwanaki goma sun wuce. Duk wanda ya azimci wannan rana Allah Zai rufe masa kofofi talatin na tsanani a rayuwar sa, a bude masa kofofi talatin na sauki.
(8) Ranar takwas ga Zulhijja ita ce ranar da ake cewa, ranar tarwiyya. Duk wanda ya azimci wannan ranar, babu wanda ya san adadin sa sai Allah.
(9) Ranar tara ga watan Zulhijja ita ce ranar hawan Arfa. Allah Yana gafartawa duk Alhazan da ke wurin Arfa. Wanda kuma ba ya wurin aikin Hajji, idan ya azimci wannan ranar, Allah Yana gafarta masa zunubansa na shekarar da ta gabata, da kuma shekarar da ke tafe.
(10). Ranar goma ga Zulhijja ita ce ranar layya. Duk wanda Allah Ya horewa abin da zai yi layya, idan ya yanka dabbarsa, digon jini na farko da zai fara diga a kasa zai zama gafara gare shi da
iyalin sa. An so wanda zai yi layya da wanda ba zai yi ba ya kame bakinsa sai bayan an dawo daga sallar idi, ya ci abinci ko wani abu daga cikin layyarsa. Allah Zai ba shi lada wacce ta fi Dutsen Uhud girma da nauyi. Kuma ana so ya raba naman sa kashi uku. Kashi na farko sadaka, kashi na biyu kyauta, kashi na uku kuma domin iyali.
Allah Ya Bamu Ikon Azumtar Dukkan Wadannan Ranakun, kuma Ya sada mu da falalar da Ya tanadar ga masu Ibada a wadannan ranaku. Ameen

20/07/2020

HUKUNCIN YIN ASKI DA YANKE FARCE A KWANAKI GOMAN FARKO NA WATAN ZUL HAJJI GA MAI NIYYAR YIN LAYYA

Bismillahir Rahmanir Rahim

Was-Salãtu wassalãmu Alaa RasulilLãh, wa Ala ĂliHi wa SahbiHi wa man wãlãH.

Bayan haka:

An so kada mutumin da yake da niyyar yin layya ya yi aski, ko yanke farce, tun daga farkon watan Zul Hajji har sai ya yanka abin layyarsa, ma’ana: da zaran watan Zul Hajji ya k**a, an so ya kame kada ya yi aski, kada kuma ya yanke farce; saboda Hadisin da Sayyida Ummu Salamah (Allah ya ƙara yarda da ita) ta ruwaito na cewa, Manzon Allah (SallalLãhu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya ce: (Wanda duk ya ga watan zul Hajji, yana kuma da niyyar yin layya, to kada ya yi aski, ko ya yanke farcensa har sai bayan ya yanka abin layyarsa)..

Sai dai wannan hanin ba na haramci ba ne k**an yanda jamhur din malamai s**a s**a tafi a kai, a wurin Imam Malik, da Imam as-Shafi'iy (Allah ya ƙara yarda da su) rashin askin da yanke farcen Mustahabi ne, ma’ana abu ne da aka so; saboda wani Hadisin da Sayyida A'isha (Allah ya ƙara yarda da ita) ta ruwaito mai cewa: "Da hannuna na ɗaure hadayar Manzon Allah (SallalLãhu alaiHi wa Alihi wa sallam), sannan ya aika su ta hannun mahaifi na, Manzon Allah (SallalLãhu alaiHi wa Alihi wa sallam) bai haramta wani abu da Allah ya halatta masa ba har dai ya yanka abin hadayarsa." kuma kowa ya sani cewa Annabi (SallalLãhu alaiHi wa Alihi wa sallam) ya yi layya a wannan shekara..

Da haka ne malamai s**a ce : hanin da yake cikin wancan Hadisi na farko ba hani ne na haramci ba.. Saɓanin yanda Imam Ahmad bn Hanbal (Allah ya ƙara yarda da shi) ya ɗauke shi a matsayin hani na haramci.. WalLahu a'alam.

Saleh Kaura

19/07/2020

'KISSA;

An Ruwaito Cewa; Wata Rana Wata Mata Ta Zo Wurin IMAMU AL-HASSANUL BASARIY(R.A), Ta Ce;

"'Diyata Ce Ta Rasu Kuma Gashi Hankalina Bai Kwanta Ba, Ina Son Inganta a Cikin Mafarkina Domin Sanin Halin Da Take Ciki",

Sai IMAMUL-BASARIY(R.A) Ya Sanar Da Mahaifiyar Yarinyar Nan Adadin SALATIN Da Zata Karanta Wata 'Kila Ta Ga Halin Da 'Yarta Take Ciki, Ya Sanar Da Ita SALATIN, Sai Kuwa Ta Je Ta Karanta, Sai Ta Ga 'Yarta Sanye Da Tufafin Wuta Da Ankwa a Wuyanta Da Kuma Mari a 'Kafafuwanta, Sai Matar Nan Ta Ji Tsoro, Ta Firgice,

Sai Ta Sanar Da IMAMU HASSANUL BASARIY(R.A), Ya Nuna Damuwarsa Matuqa a Gareta, Ana Cikin Wannan Halin Ne Ba'a 'Dauki Lokaci Mai Tsawo Ba Sai IMAMU HASSANUL BASARIY(R.A) Yayi Mafarkin(Wannan Yarinyar) Tana a Cikin Aljanna Akan Gado(Na 'Kasaita) Ga Kuma Kan Sarki(Irin Wanda Sarakuna Ke Sanyawa a Kawunansu) Akan Wannan Baiwar ALLAH.

Sai Ta Ce;"Ya IMAMU! Ko Ka Gane Ni Kuwa???"

Sai Ya Ce;"A'a Baiwar ALLAH Ban Gane Ki Ba",

Sai Ta Ce;"Ai Ni Ce Wannan Matar Da Ka Sanar Da Mahaifiyata SALATI Don Ta Ganni a Cikin Mafarkinta",

Sai IMAMU AL-BASARIY(R.A) Ya Ce Da Ita;"To Menene Sababin/Sirrin Al'amarinki???"

Sai Ta Ce;"Wani Bawan ALLAH Ne Ya Zo Gittawa Ta Makabartarmu Sai Yayi SALATI Ga ANNABI(S.A.W) Yayi Hadiyyar Ladan Salatin Gare Mu(Mamatan) Kuma Ya Kasance a Cikin Makabartarmu Akwai Mutane 'Dari Biyar Da Sittin(560) Da Suke a Cikin Tsananin Azaba Sai Aka Yi 'Kira; A 'Dauke Mana Azaba Sanadiyyar SALATI Ga ANNABI(S.A.W) Da Wannan Bawan ALLAH Yayi Da Niyyar Hadiyya a Gare Mu".

ALLAHUMMA SALLI ALA MUHAMMADIN WA'ALA AALIHI WA SAHBIHI WA SALLIM!

(Don Ganin Wannan Hikayar Sai a Duba;

*. IHYAA ULUM AD-DEEN- IMAM ABU HAMID AL-GHAZALI Volume 4, Shafi Na 492.

*. AT-TAZKIRATI FI AHWALIL MAUTA WA UMURIL AKIRATI - MUHAMMAD BN F***J AL-MALIKIYYIL QURDABI, Shafi Na; 67).

Ya ALLAH! Don Albarkar Tulin Sirrin Dake Tattare Cikin SALATI GA ANNABI(S.A.W), ALLAH Ka Nisanta Tsakaninmu Da Wahala Kowacce Iri Ce Anan Duniya Da Kuma a Gobe Qiyama Ameeen.

19/07/2020

Idan kana tsammanin Allah bai baka komai ba to ka kalla wannan hoton dan kasan irin kyautar da Allah yayi maka, ba tare da ka biya shi ba, abinda kawai yake bukata a wajenka shine ka gode masa, dan haka kar ka wuce ba kayi 'COMMENT' da 'ALHAMDULILLAH' ba.

18/07/2020

MA'ANONIN SALATUL FATIH INGANTACCE NE

Inji Kwamitin Fatawa Na Kasar Saudiyya

A Cikin Jerin Fatawowin Kwamitin Fatawa Na Kasar Saudiyya Wato ( فتاوى اللجنة السعودية ) A Cikin Juzu'i Na 66 Shafi Na 7 A Fatawa Mai Lamba 4551 An Ce Ma'anonin Salatil Fatih Ingantacce Ne.

Ya Dan Uwa Ahlul Zikr Idan Yau Ka Fara Jin Wannan Maganan Kar Ka Wuce Ba Kayi Liking Da Sharing Ba...

18/07/2020

LISANUL-FAIDHA(Maulanmu Shehu Dahiru Usman Bauchi(R.A) Yana Cewa;

"Duk Wanda Ka Ga Bai Shiga 'DARIQA Ba, Ba Wai Shi Ne Ya'ki Ba(a Karan-Kansa), A'a An 'Ki Ne, MISALI; Idan Aka Kafa Rumfa(In Ana Wani Taro) Sai Aka Ware Wani Waje(Daban) Aka Ce Wannan Gefen V.I.P(Very Important Person) Ne, Aka Sake Ware Wani Wuri(Daban) Aka Ce Shi Kuma Wannan Na Yaku-Bayi Ne; Don Haka Kowa Idan Ya Zo a Wurin Da Aka Tanadar Masa Zai Zauna, Da Ace Wani Wanda Baya Daga Cikin V.I.P Ya Zo Yana So Ya Je Ya Zauna Inda V.I.P Suke, 'Yan Sandan Da Suke Wajen Taron Za Su Tambaye Shi; Ina Takardar Ka Na V.I.P Idan S**a Tambaye Shi Ya Nuna Musu Shike Nan Sai Su Nuna Masa Wajen Zamansa, Idan Babu Wani Shaida Na Cewa; Shi Yana Cikin V.I.P Kuma Sai Su Nuna Masa Wajen Yaku-Bayi Su Ce Masa Ga Wajen Zamanka Can,

Wai Shin Shi Mutumin Ne Ya'ki Ko Kuma An 'Ki Ne(Ya Shiga Wurin)??? AMSA Shi Ne; An 'Ki Ne, Don Haka 'DARIQA Ma Haka Take Sai Wanda Fadar ALLAH Ta Karrama Yake Kar6ar 'Dariqar a Wajen Waliyan ALLAH, Ya Ri'ke Har 'Karshen Rasuwarsa.

ALLAH Ya Rayamu Muna Cikin 'Dariqar SHEHU TIJANI(R.A) Ya Kashe Mu a Cikinta Ya Tashe Mu a Cikinta Don Alfarmar MA'AIKI(S.A.W)".

Allahumma Ameeeen SHEHU(R.A)!!!

Muna Addu'ar ALLAH(S.W.T) Ya 'Karawa SHEHU(R.A) Lafiya, Da Nisan Kwana, Ya Bamu AlbarkarSA(R.A),

ALLAH Ya Kar6i Rayukanmu Muna Cikakkun Tijjanawa(Na Haqiqa) Don Alfarmar SAYYIDUL-WUJUDI(S.A.W) Ameeeen.

(Daga; Othman Muhammad).

14/06/2020

Allah ya kawo karshen masifun dake faruwa a arewacin najeriya. Albarkan Manzon Allah saww. Amiin

02/06/2020

INNA'LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!

Allah Yayiwa Ma'ajin Agajin Fityanul Islam na Karamar hukumar Zaria Mal. Zakariyya'u Adamu Rasuwa.

Za'ayi Jana'izar a Gidan su dake Limancin Iya, Gidan Masa ko Gidan Maulidi dake cikin Birnin Zazzau da Misalin Karfe 08:00pm na Daren Yau

Allah Yajaddada Rahama a gareshi, Yasa Aljannace Makomarshi, Ya yafemasa dukkan Zunubansa..........Ameen

31/05/2020

ABIN ALFAHARI;

Sheikh Dr, Muhammad Nazifi Bichi Jami'in Tsaro A Bangaren Hukumar Qasa baƙi ɗaya, Doctor a ilimin Arabia (Ph,D) Babban Malamin Addinin Musulunci ne kuma Shehi ne a Dariqar Tijjaniyya Murabbi a Faila Ibrahimiyya Lecturer a Jami'ar Bayero da FCE Bichi
Allah ya qara lafiya da nisan kwana, ya kiyaye dukkan sharri na zahiri da badini, ya qara daukaka darajar Albarkan Manzon Rahma (saww) Amiin

Daga Ahmad Mai Zare Nguru

19/05/2020

Address

Kano State Zaria Road Naibawa
Kano
A.GKURA

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fityanul islam kano state branch posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category


Other Newspapers in Kano

Show All