HIMMA TV

HIMMA TV HIMMA TV TASHAR ALUMMA
For inquiries and promotions +2348025606115
(3)

27/01/2025

Assalamu Alaikum Yau Za'a Karanta Ya Arhamar Rahimina, Ya Rabbal Alamina (Kafa Dari)(100), Salati (Goma)(10), Allah Ya Mana Muwafaqa

Gwamnatin Sokoto za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi a wannan watanGwamna Ahmed Aliyu na jihar Sokoto ya amince da fa...
27/01/2025

Gwamnatin Sokoto za ta fara biyan mafi ƙarancin albashi a wannan watan

Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sokoto ya amince da fara biyan sabon mafi karancin albashi na Naira dubu 70 ga ma'aikatan jihar.

Sanarwar da gwamnati ta fitar ta ce ma’aikatan gwamnati za su samu sabon mafi karancin albashin da zai fara daga albashin su na watan Janairu da mu ke ciki.

Sanarwar mai dauke da sa hannun Mista Abubakar Bawa, Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan ya ce biyan kudin zai shafi ma’aikatan gwamnati da ma’aikatan kananan hukumomi a fadin jihar.

Ya ce biyan sabon mafi ƙarancin albashin wani cika alkawari ne da gwamnan jihar ya ɗauka tun a baya.

27/01/2025

Ba a Hukumci Akan Abinda ba, Sani ba
Imam Makinu Abdulkadir Fagge

26/01/2025

Imam Makinu Abdulkadir Fagge

26/01/2025

Ilimi ko wannene yanada Muhimmanci
Imam Makinu Abdulkadir Fagge

26/01/2025

Laifin daban gwaran daban
Imam Makinu Abdulkadir Fagge

26/01/2025

Karatu Yana Bukatar nitsuwa

Trump ya dakatar da bada tallafi ga ƙasashen wajeAmurka ta dakatar da ba wa kasashen waje tallafi nan take k**ar yadda w...
26/01/2025

Trump ya dakatar da bada tallafi ga ƙasashen waje

Amurka ta dakatar da ba wa kasashen waje tallafi nan take k**ar yadda wata takardar gwamnati da ke kunshe da umarnin wadda aka yi satar fitar da ita ta nuna.

Sai dai dakatarwar ba ta shafi bayar da taimakon abinci da bayar da kudade ga harkokin sojin Isra'ila da Masar ba, k**ar yadda takardar wadda BBC ta tabbatar da ita ta nuna.

Ma'aikatar harkokin waje ta Amurkar ce ta bayar da umarnin ga jami'ai da ofisoshin jakadancin kasar na waje.

Matakin ya biyo bayan umarnin da Shugaba Trump ya bayar ne a ranar Litinin na dakatar da bayar da tallafin raya kasashen waje tsawon kwana 90, har zuwa lokacin da za a sake duba tsarin ta yadda zai dace da manufofinsa na kasashen waje.

Amurka ita ce babbar wadda ta fi ba wa kasashen duniya tallafi inda ta kashe dala biliyan 68 a 2023, k**ar yadda alkaluman hukuma s**a nuna.

25/01/2025

PROF SHEIKH UMAR SANI FAGGE

HOTUNA: Dubbaɲ Mabiya Darikar Tijjaniyya Na Duniya A Filin Wasa Na Sani Abacha Dake Birnin Kano.Domin Gabatar Da Maulidi...
25/01/2025

HOTUNA: Dubbaɲ Mabiya Darikar Tijjaniyya Na Duniya A Filin Wasa Na Sani Abacha Dake Birnin Kano.

Domin Gabatar Da Maulidin Shêikh Ibrahim Inyass Al Khaulaq RA.

Daga: Tijjaniyya Media News

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan Kano kuma shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban kw...
24/01/2025

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa tsohon gwamnan Kano kuma shugaban APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban kwamitin gudanarwa na hukumar kula da filayen jirgin sama ta ƙasa, FAAN, sannan ya naɗa tsohon mataimakin gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin shugaban kwamitin gudanarwa na bankin 'Federal Mortgage Bank's, FMBN.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta doke Enyimba International 2-0 a kwantan wasan mako na 14 na gasar firimiya ta ...
24/01/2025

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta doke Enyimba International 2-0 a kwantan wasan mako na 14 na gasar firimiya ta ƙasa da ƙungiyoyin biyu su ka fafata a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata a Kano a jiya Alhamis.

Ɗan wasan gaba na Kano Pillars, Adam Musa Adam Oscar ne ya zura wa Kano Pillars dukkanin ƙwallayen biyu da ta samu a minti na 26 da kuma na 72 na wasan.

Da wannan nasara, Sai Masu Gida ta dawo kan matsayi na 7 a jadawalin matsayin ƙungiyoyin da suke fafatawa a gasar, yayin da Enyimba ke kan matsayi na 8.

Wasa dai tsakanin Ƙungiyoyin biyu wasa ne na hamayya da ake wa laƙabi da Zobia Derby, kuma wannan suna an samu shi ne daga kalma ‘zo’ daga harshen Hausa da kuma ‘bia’ daga kalmar harshen igbo.

23/01/2025

TAFSIRIN AL QURAN MAI GIRMA TAREDA MLM Gwani Mustapha Ibrahim Sani Wanda Ake Gabatar wa Duk Ranar Alhamis magriba Zuwa Isha e A Masallacin dangi

Shin me zaku iyya cewa game wannan Bawan Allah
23/01/2025

Shin me zaku iyya cewa game wannan Bawan Allah

'Allah Ya sakawa Abba Gida-gida da alheri', Dan Bilki ya yabawa Gwamna Yusuf kan kula da almajirai a Kano Fitaccen mai s...
23/01/2025

'Allah Ya sakawa Abba Gida-gida da alheri', Dan Bilki ya yabawa Gwamna Yusuf kan kula da almajirai a Kano

Fitaccen mai s**ar gwamnatin jihar Kano ta NNPP kuma ɗan jam'iyyar APC, Abdulmajid Dan Bilki Kwamanda ya yaba wa Gwamna jihar, Abba Kabir Yusuf bisa kwashe almajirai da kuma kula da su.

DAILY NIGERIAN HAUSA ta rawaito cewa a kwanan nan ne dai gwamnan ya bada umarnin kwashe almajirai da ƙananan yara marasa galihu daga tituna da kwararo-kwararo na jihar.

Gwamnan ya bada umarnin ajiye su a sansanin alhazai na jihar Kano, inda ake kula da su da kuma basu karatu.

Da a ke tattaunawa da shi a wani faifen bidiyo da ya yadu a kafafen sadarwa, Kwamanda ya yaba wa gwamnan bisa wannan mataki.

A cewar Kwamanda, "ka san wani abu a gwamnatin Abba? Allah Ya saka masa da alheri. Wallahi abu daya ya yi yanzu nake ganin sa da kima. Kuma duk zargin da na ke masa na ya sa an cutar da ni, Allah Ka sani, na yi wannan magana dan kai, na yafe masa.

"Sabo da ba dan wani abu ba, je ka can sansanin alhazai ka ga almajiran nan da aka k**a. Billahillazi ka je ka ga abinci mai kyau ake ba su da katifu da gidan sauro. Ni ganau ne ba jiyau ba.

"Ko yau din nan da na je, na ga ana dafa musu ruwan zafi daya bayan daya su na wanka. Dan haka Abba Allah Ya saka maka da alkhairi. Haka ya k**ata ai musu,"

Kwamanda ya kuma shawarci gwamna Abba da ya umarci dukkan ƙananan hukumomi 44 na jihar da su rika yin irin wannan aikin na kula da almajirai.

Ya jaddada cewa "wannan abu da Abba ya yi, zai iya samun afuwar Ubangiji," in ji shi

Tinubu ya amince da kafa kwalejin ilimi a Abuja da za a saka mata sunan saShugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da...
22/01/2025

Tinubu ya amince da kafa kwalejin ilimi a Abuja da za a saka mata sunan sa

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da kafa Kwalejin Fasaha ta Tarayya a Gwarinpa, daya daga cikin manya-manyan rukunin gidaje a babban birnin kasar.

DAILY TRUST ta ruwaito cewa, za a kuma sanya wa sabuwar makarantar sunan shugaban kasar.

A wata wasika mai dauke da kwanan watan 16 ga watan Junairu 2025 kuma zuwa ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ministan ilimi, Dr. Tunji Alausa, ya ce gwamnatin tarayya ta amince da kafa Bola Ahmed Tinubu Polytechnic, Gwarinpa domin bunkasa fasahar kere-kere, sana’a da kasuwanci da horarwa daidai da manufofin kasa kan ilimi.

Ministan ilimi, a cikin wasikar da ya sanya wa hannu, ya bukaci Wike da ya ba da wurin da ake son a samar da ginin wucin gadi da na dindindin a Gwarinpa don samar da makarantar.

Dukkaɲ Ƙungiyòyin Addinai Dake Ƙasar Nan Ƙur'áɲi Ya Haɗa Mu Wajé Guda Dòmin Babu Wanda Bai Yi Imani Da Kur'áɲi Ba A Ciki...
22/01/2025

Dukkaɲ Ƙungiyòyin Addinai Dake Ƙasar Nan Ƙur'áɲi Ya Haɗa Mu Wajé Guda Dòmin Babu Wanda Bai Yi Imani Da Kur'áɲi Ba A Cikinmu, Dòn Haka Ne Za Mu Gayyato Mahadatta Sama Da Dubu Talatin Daga Kowane Bangare Dòmiɲ Yin Taro A Abuja Kafin Azumi, Inda Za A Ji Sautikan Alarammomi Daban-Daban, Inji Shéikh Bala Lau

Menene ra'ayinku?

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HIMMA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Videos

Share