Ungogo legislative

Ungogo legislative Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ungogo legislative, Digital creator, Ungogo, Kano.

15/04/2024

Eid Mubarak
To All Muslim Ummah

10/11/2023

Alhmadulillah Gawuna Allah Ya Taya
Riko

001 kano State
18/10/2023

001 kano State

SHEKARU 63 NA KUNCI, TAKAICI, AZABA DA BAKIN CIKI. 😭Babu dan Najeriya mai hankali musamman ma dan Arewa da wannan rana z...
01/10/2023

SHEKARU 63 NA KUNCI, TAKAICI, AZABA DA BAKIN CIKI. 😭

Babu dan Najeriya mai hankali musamman ma dan Arewa da wannan rana zata zame masa ranar murna, acikin shekaru 63 muka zama bayi ababen wofantarwa daga shugabanninmu, akaita zubar da Jinanenmu, akaita sace ahalinmu mata da mazajenmu, akaita sace dukiyoyinmu, aka maida mu barayi saboda kagaggen talaucin da s**a sanya mana.

Abun bakin ciki, cikin shekaru 63 muka zama madamfara, mazambata, 'yan ta'adda, mabarata, 'yan tamore kuma cikakkun karnukan farautan masu jajayen kunnuwa.

Bazan murna ba, domin 'yancin bai bani abunda zan nuna cikin annashuwa ba sai kaburburan ahalinmu, tunanin rashi da batan da makusantanmu s**ayi da rasa muhallanmu da dan abunda zufanmu ya tara mana.

Abunda ke kara bani hawaye idan na kallan irin matsanciyar Yunwa data addabin 'yan uwanmu a kasa mai tarin arzikin ma'adanai da yawan jama'a.

Kaico da isowarmu wannan rana daba ta alfahari ba.

ALLAH KASA ZUCIYOYIN MU SU TAFI AKAN IRIN WANNAN TAFARKIAn manta kuɗaɗen da yawansu ya haura Naira miliyan goma sha biyu...
16/09/2023

ALLAH KASA ZUCIYOYIN MU SU TAFI AKAN IRIN WANNAN TAFARKI

An manta kuɗaɗen da yawansu ya haura Naira miliyan goma sha biyu a cikin Adaidaita sahun da yake tuƙawa, bayan yaga kudin sai ya koma inda ya sauke fasinjan ko zai ganshi amma bai tarar dashi ba, sai ya kai kudaden wajen mahaifiyarsa ya gaya mata cewa manta kuɗaɗen akayi a Adaidaita ɗin sa, nan take mahaifiyarsa tace yaje ya gayawa Mahaifinsa inda nan take Mahaifin yaron yace su koma su sake dubawa ko za'a ga mai kuɗin, da ba'a gani ba sai s**a ajiye kuɗin a gida, basu taba ko sisi ba duk da cewa jiya da kyar s**a samu garin kwakin da s**a ci a gidan nasu k**ar yadda Mahaifin yaron ya fada...

Sunji ana cigiya a gidan Rediyon Arewa dake kano, inda nan da nan s**a ɗauki lambar wayar da aka bayar s**a kira ...

A takaice dai yaron da iyayensa sun mayarwa da mutumin da ya manta kudaden abunsa, inda shi kuma ya basu kyautar Naira dubu dari hudu...

Wannan yaro ya kyauta.....

Copied from Rabiu Biyora

Alhaji Musa Iliyasu Kwankwaso na APC ya yi nasara a Kotu kan kujerar Majalisar Tarayya ta Kura da Madobi da Garun Malam.
10/09/2023

Alhaji Musa Iliyasu Kwankwaso na APC ya yi nasara a Kotu kan kujerar Majalisar Tarayya ta Kura da Madobi da Garun Malam.

INNA LILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UNAllah ya yiwa Sheikh Giro Argungu rasuwa, bayan jinya da ya samu a daren jiya Talat...
06/09/2023

INNA LILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN

Allah ya yiwa Sheikh Giro Argungu rasuwa, bayan jinya da ya samu a daren jiya Talata, bayan ya kammala tafsirin Magriba zuwa ishaa.

Muna Addu'ar Allah ya jikan Malam, hakika duniyar musulunci tayi babban rashi.

Gwamnatin jihar Gombe ta kammala kashi na farko na raba tallafin kayan masarufi ga mabuƙata a jihar. Kayan na cikin tall...
28/08/2023

Gwamnatin jihar Gombe ta kammala kashi na farko na raba tallafin kayan masarufi ga mabuƙata a jihar.

Kayan na cikin tallafin da gwamnatin tarayya ta bai wa jihohi don rage raɗaɗin janye tallafin man fetur.

25/05/2023

Surely Gawuna Is Coming....
Masoya a Kwantar da Hankali

04/03/2023

Gawuna yan Ungogo Suke Fata
Maye Ra'ayin ku akai

05/02/2023

Ungogo
Muna Goyon Bayan Gawuna a Matsayin Gwamnan Kano

Kamar tsaro, aikin inganta lafiya ba na gwamnati bane ita kadai shi yasa ake bukatar masu hali masu zuciya domin a hadu ...
22/09/2022

Kamar tsaro, aikin inganta lafiya ba na gwamnati bane ita kadai shi yasa ake bukatar masu hali masu zuciya domin a hadu a inganta lafiya a Jihar Kano.

Kalaman gwamnan jihar kano kenan Dr. Abdullahi Umar Ganduje yayin kaddamar da katafaren ginin asibiti, sashen kula da masu ciki da kananan yara a asibitin Waziri Gidado dake Bachirawa Karamar Hukumar Ungogo wanda Alh. Abdullahi Muazu ya gina tare da sadaukar dashi ga gwamnati.

Gwamna ya yaba da namijin kokarin dan kasuwar mai kishin cigaba tare da kira da sauran al'uma dasuyi koyi da irin wannan aikin alkhairi.

Haka Shugaban Karamar Hukumar tare da kwashinan lafiya sun bude mak**ancin wannan aiki a Asibitin PHC Tudun Fulani inda kungiyar MSF ta fadada asibitin ta hanyar gina sabon block na kula da masu ciki da kananan yara domin inganta lafiya a matakin farko a Karamar Hukumar dama Jihar Kano. Shugaban Karamar Hukumar Ungogo Engr. Dr. Abdullahi Garba Ramat ya nuna jin dadinsa da godiya ga wannan kungiya tare da tabbatar da yin aiki kafada kafada dasu domin kawo ci gaba a fannin lafiya a Karamar Hukuma.

Gwamna ya samu rakiyar mai masaukin baki Engr. Dr. Abdullahi Garba Ramat, takwaransa na Dala, Commissioner na Lafiya dana kananan hukumomi, da sauran manyan jami'an gwamnati

Operation murkushe kayan Gwari totally!!!Shugaban Ungogo Local Government  Engr Abdullahi Garba Ramat ya jagoranci Karba...
19/09/2022

Operation murkushe kayan Gwari totally!!!

Shugaban Ungogo Local Government Engr Abdullahi Garba Ramat ya jagoranci Karbar daruruwan yan jam’iyar kayan gwari wanda ya hada Shugabannin Yan Kwankwasiyya zuwa APC, sannan ya kaddamar da rabon tallafi na mazabar Rijiyar Zaki wanda masu riqe da muqamai na mazabar suke shiryawa kowanne wata a garin dagatai.

Yayin gabatar da jawabinsa, Shugaban ya yaba da irin kokarin da yan' wannan mazaba sukeyi, tare da kara masu karfin gwiuwa.

Cikin wadanda Engr. Ramat ya karba daga tsarin kwankwasiyya sun hada da jagorori irinsu

1. Abdullahi Ibrahim Rimingata wanda ake kira (Criminal Barrister) a siyasa. Shine Jagoran Jamiyyar N.N.P.P ne na garin Rimingata da mazabar Rijiyar Zaki , Tsohon Ma'ajin Jamiyyar P.D.P ne na mazabar Rijiyar Zaki a 1999 zuwa 2003 Sakataren jamiyyar P.D.P na mazabar Rijiyar Zaki 2003 to 2007. A yanzu haka Secretary na jamiyyar P.D.P Kwankwasiyya

2. Jamilu Ashiru Rimingata wanda ake kira (Rossy) Jagora ne na kwankwasiyya kuma Exco na local government a NNPP, kuma tsohon dan takarar Kansila a mazabar Rijiyar Zaki

3. Garba Adullahi Rimingata wanda ake kira da (Garba Sabga) Shima jagora ne kuma ma'ajin jamiyyar NNPP kwankwasiyya a yanzu haka

4. Salisu Bala wanda ake kira da (Tunde) Shima jagora ne kuma Shugaban yankasuwa na jamiyyar kwankwasiyya

Mutum 215 yan jam’iyar APC ne s**a rabauta da tagomashin naira dubu biyar biyar, bamboo da butoci ga masallatai wanda masu mulki na mazabar s**a samar karkashin Jagorancin Kansilan Mazabar wanda shine House leader na Karamar Hukuma Babangida Idris

Taron ya samu halartar Hon Badaru Umar dan takar majalissar jaha a Ungogo, da sabon commissioner Hon. Garba Yusuf Izala, chairman APC kano central Hon. Shehu Aliyu Ungogo , mai bawa Gobna shawara kan harkar majalissa Hon Tasiu Yellow Panisau, tsohon dan majalissar jaha Hon Bachirawa Farouk Mohammed , Hon Gambo Adamu, caucus chairman da sauran manya manya jagorori.

Chairman ya shedawa Al’umma cewa zaici gaba da zagay

Taron Rabon Bada Tallafin Kudi Kimanin Naira Miliyan Biyu ( 200 000 0) Da Robar Ruwa Da Butoci na Kimanin Mutum Dari Hud...
18/09/2022

Taron Rabon Bada Tallafin Kudi Kimanin Naira Miliyan Biyu ( 200 000 0) Da Robar Ruwa Da Butoci na Kimanin Mutum Dari Hudu (400) Mata Da Maza Dakuma Karbar Wasu Yan Tsohuwar Tafiyar Jamiyyar NNPP Masu Yawan Gaske Wanda S**ayi Hijira Zuwa Jamiyyar Apc a Mazabar Rijiyar Zaki

A yau lahadi ne Megirma Shugaban Karamar Hukumar Ungogo Engr Abdullahi Garba Ramat Dakuma Kwamishinan Ruwa na Jahar Kano Hon Garba Yusif Da Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Ungogo Kuma Dan Takarar Majalisar Dokoki ta Jahar Kano Hon Badaru Muhammad Umar da Sauran Wasu Daga Cikin Jiga Jigan Jamiyyar Apc na Karamar Hukumar Ungogo S**a Hallaci Gagarumin Bikin Bawa Mata da Maza Tallafi na Kudi Kimanin Naira Miliyan Biyu( 200 000 0) Dakuma Robar Ruwa Da Butoci Ga Kowacce Chapter Kimanin Chapter Samada 30 Domin Yin Ibada .

Taron Yagudana ne Acikin Kwaryar Mazabar Rijiyar Zaki a Karkashin Jagorancin Sakataren Mulki na Karamar Hukumar Ungogo Hon Baffa B Chiroma Cln (Jagoran matasa) Da Zababben Kansilan Mazabar Kuma Shugaban Majalisar Kansilolin Karamar Hukumar Ungogo Rt Hon Babangida Speaker Ugg Da Sauran Jiga Jigan Yan Jamiyyar Apc Rashen Mazaba Da Karamar Hukumar Ungogo Baki Daya.

Taron Mai kimanin Kwamutoci Goma Yasami Damar Tarbar Manyan Baki Daga Kowanne Bangare Na Karamar Hukumar Ungogo Kamar Haka :

Tsohon Dan Majalisar Jaha Mai Wakiltar Ungogo Kuma SA (House Assembly) Hon Tasi'u Yellow Panisau, Hon Shehu Aliyu Ungogo Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Ungogo, Hon Ibrahim Shehi, Shugabar Mata na Jamiyyar Apc Rashen Karamar Hukumar Ungogo, Malam Bilya Asasco Bachirawa, Hon Ado Amo Zaura Tsohon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Ungogo, Hon Bagoburi Shugaban Dattijan Jamiyyar Apc , Hon Farouk Bachirawa Tsohon Wakilin Ungogo a Majalisar Jahar Kano, Salisu Muhammad R Zaki Tsohon Kantoman Karamar Hukumar Ungogo.

Saikuma Kungiyoyin Yan Media Da Mafarauta

Ungogo legislative

Gwamatin Jihar Kano Zata Kashe  N1.2bn Wajan Gyaran Titunan Cikin Garin Kano.Hanyoyin sun hadarda;*Audu bako Way*Sani Ma...
18/09/2022

Gwamatin Jihar Kano Zata Kashe N1.2bn Wajan Gyaran Titunan Cikin Garin Kano.

Hanyoyin sun hadarda;

*Audu bako Way
*Sani Marshal Road
*Mission Road
*Hotoro Tsamiyar Boka Road.
*Layin Kaura Goje.
*Sheikh Hassan-Layin Gidan Biredi-Sani Bello Road.
*Kwanar Jaba-Kwana Hudu-Gayawa Bridge Road.
*FCE-Kofar Famfo
*Gwarzo Road
*Sheikh Jafar Road
*Muhammadu Buhari Road.
*New Hospital Road
*Sabo Bakin Zuwo Road.
*Lamido Crescent.
*Route to Cancer Treatment Centre. *Dakata Road.
*DanHassa-Eastern Bypass.
*'Yan Mota-Kofar Mazugal.
*Abagana Street Fagge.
*Aminu Kano Way-Kofar Ruwa.
*Festing-Bompai.
*France Road.
*Igbo Road.
*Gwammaja-Wapa
*Kurna Babban Layi
*Madaki Street Yolawa
*Sabon T**i Mandawari
*Kwanar Dala-Gidan Malam Aminu Junction
*Lafiya Road.

-Malam Muhammad Garba
Hon. Commissioner For Information, Kano State.

'Yar Shugaban ASUU Ta Kammala Karatu A Jami'ar Chicago Dake Kasar AmurkaMe za ku ce?
17/09/2022

'Yar Shugaban ASUU Ta Kammala Karatu A Jami'ar Chicago Dake Kasar Amurka

Me za ku ce?

Ina masu son su taka rawa a ciki shirin  ? ga dama ta samu, domin taka rawar Jarumi Tajuddeen kuyi slide • domin ganin s...
17/09/2022

Ina masu son su taka rawa a ciki shirin ? ga dama ta samu, domin taka rawar Jarumi Tajuddeen kuyi slide • domin ganin script. Sai ku dauki video ku fada mana suna, lamban waya, inda ake zama, shekaru, duk a cikin video din sai ku taka rawar yanda yake ajikin script.
Daga nan sai ku tura mana wannan video din zalla ta
WhatsApp: 07024224474, banda kira, banda tura wani abu daban.

Wani Dan chana ya kashe wata Matashiya mai Suna Ummita a KanoYadda abin ya faru….Mr Geng dan kasar china da Ummukulsum B...
17/09/2022

Wani Dan chana ya kashe wata Matashiya mai Suna Ummita a Kano

Yadda abin ya faru….

Mr Geng dan kasar china da Ummukulsum Buhari sun yi soyayya,amma daga bisa ni ya sami labarin tayi aure (k**ar yadda ya fada)

Dan haka yayi fushi yaje gidan ta ya haura ta taga ya kashe ta a unguwar su dake Jan bulo kuma aka kaita asibitin UMC anan ta rasu

Ummukulsum ne sunan ta amma an fi kiran ta da Ummita ,ta gama digiri a fannin aikin gona daga jami’ar Kampala dake Uganda yanzu haka tana bautar kasa a Sokoto

Jami’an immigration da yansanda ne s**a kwace shi daga mutanen da s**a fara sassama shi a yankin Jan bulo kusa da layin Lawan Kyankyan
Yanzu haka yana hannun yansanda

Allah ya jikan ta yayi mana maganin matsalolin mu.

Kungiyar IZALA ta tara kudi Naira miliyan dari da bakwai ta dalilin tattara fatun layya (₦107,704,484.25)✍️Ibrahim Baba ...
24/08/2022

Kungiyar IZALA ta tara kudi Naira miliyan dari da bakwai ta dalilin tattara fatun layya (₦107,704,484.25)

✍️Ibrahim Baba Suleiman

Kungiyar wa'azin musulunci mai kira a kau da bidi'a a tsaida sunnar Annabi Muhammad mai tsira da aminci, ta tara naira miliyan dari da bakwai da dari bakwai da hudu da naira dari hudu da hudu da kwabo ashirin da biyar (₦107,704,484.25) na tattara fatun layyan da ya gabata na shekarar 1443/2022.

A bana Jihar da tafi ko wace jiha kawo kudi itace jihar Sokoto inda ta tara Naira miliyan goma sha uku da dubu dari takwas da tamanin da shida da naira hamsin kacal (13,886,050,00)

Jihar kaduna ita tayi na biyu inda ta tara fatun Naira miliyan goma sha uku da dubu dari uku da talatin da tara da naira dari shida kacal. (₦13,339,600.00).

Jihar Kebbi ita tayi na uku inda ta tara fatun Naira miliyan goma da dubu dari da sha biyar da naira dari biyu da tamanin kacal. (₦10,115,280,00)

Haka lamarin ya gudana a dukkan jihohin Naijeria talatin da shida harda Abuja.

A cikin bayanan sa shugaban IZALA na kasa, Sheikh Abdullahi Bala Lau ya yabawa al'ummar kasar matuka wajen bada hadin kai a wannan aikin tare da tabbatar da gudanar da kudaden k**ar yadda yak**ata, ya kuma yabawa tare da jinjina ga kwamitin tattara fatun layyan da kwamandojin agaji da s**a tura wakilai a ko wace jiha kuma s**a jajirce wajen ganin aikin ya gudana yadda ake bukata.

A baya angina katafaren masallaci da gidan shan magani gami da katafaren masaukin baki a cikin birnin Abuja duka da kudaden fatun layyan da jama'a ke badawa.

Allah ya sakawa duk wanda ya sanya jarinsa a wannan aiki da gidan Aljanna. Amin

JIBWIS NIGERIA 🇳🇬
[email protected]
25-Muharram-1444H
23-August--2022

04/08/2022

UNGOGO LOCAL GOVERNMENT

A iya sanin ka da shugabanni dake Rike da local government din nigeria baka taba ganin shugaba irin na ungogo ba duba da irin ayyukan da yake a wannan local government din idan mukai duba da yadda yake samar wa natasa da mata abin yi tabbasa abin Alfahari ne shugaba ya san ciwon matasan sa saboda matasa sune kashin bayam Al'umma,
Shine chairman din da yake Rabo a local government dinsa k**ar senator ko wani member ya Raba
1.Motoci
2.mashina
3.filaye
4.Rumar kasuwa
5.tallafin dalibai
Dadai sauran su
Abin koyi ne ga shugabanni tun daga matakin jaha har zuwa kasa

Muna maka fatan Alkairi k**ar yadda ake maka kirari
Ramat Silar Alkairi
Ramat Nakowa ne
Allah ya cigaba da dafa maka ya shige maka gaba
Ameen

Rubutawa
Ungogo legislative
08145345864

01/08/2022
ABIN AL’AJABI!!!Wani matashi ya je ya yaye rufin masallacin nan don ya gina musu sabo a kauyen Kanoke cikin karamar huku...
30/06/2022

ABIN AL’AJABI!!!

Wani matashi ya je ya yaye rufin masallacin nan don ya gina musu sabo a kauyen Kanoke cikin karamar hukumar Kiyawa a Jihar Jigawa.

Daga baya aka gano cewa dan damfara ne, ya kwashe rufin da kofofi da tagogin masallacin ya siyar.

Kakakin ‘yan sandan jihar Jigawa DSP Lawal Shi'isu Adam ya ce sun k**a matashin inda s**a gurfanar da shi a gaban kotu.

📷 Adamu Kiyawa

Address

Ungogo
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ungogo legislative posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ungogo legislative:

Videos

Share


Other Digital creator in Kano

Show All