Dillaliya

Dillaliya Dillaliya Jarida ce da aka samar dan cigaban harshen Hausa da kuma samar da sahihan labarai cikin s

Yadda Ambasada Hajiya Samira Bala Usman ta karbi shaidar zama Tauraruwar Hausa da hadin kan Hausawan DuniyaDaga Ibrahim ...
25/05/2025

Yadda Ambasada Hajiya Samira Bala Usman ta karbi shaidar zama Tauraruwar Hausa da hadin kan Hausawan Duniya

Daga Ibrahim Muhammad

Sakamakon kyakkyawar shaida ta irin gudummuwa da al'umma s**a shaidi Hajiya Samira Bala Usman na bayarwa ga ci gaban al'umma, "Gidauniyar Hausa da hadin kan Hausawan Duniya Charity" ta tabbatar mata da ba ta matsayin Tauraruwar Hausa da ci gaban Hausawan Duniya, a yayin wani taro da aka gudanar na Gidauniyar a jihar Kano.

Da take zantawa da 'yan jarida bayan karbar shaidar na tabbatar mata da matsayinta na Tauraruwar Hausa da hadin kan Hausa, Hajiya Samira Bala Usman ta bayyana mutukar murna da farin cikinta game da wannan shaida da aka ba ta na zama daga cikin shugabanni a Gidauniyar Hausa da Hausawan Duniya Charity.

Ta ce Gidauniyar ta Hausa da hadin kan Hausa tana da himma, kwazo da kishi wajen samawa Hausawan Duniya hadin kai da cigaba a tsarin tafiyar da rayuwar su a duk inda suke.

Ta kara da cewa, ta yi mutukar gamsuwa sosai da irin tsare -tsare da Gidauniyar take yi masu dimbin ma'ana wajen tallafa wa mgina ci gaban al'umma, musamman kokarin da take yi wajen hana barace-barace da tallafa wa marayu m da kuma mhada kan al'ummar Hausawa a duk inda s**a samu kansu a duniya, kowa ya san dan'uwansa sannan suna kuma bunkasa al'adu da harshen Hausa wacce ta watsu a duniya.

Ambasada Hajiya Samira Bala Usman, Tauraruwar ta Hausa da Hausawan Duniya, ta kara da nuni da cewa dama ita wannan Gidauniyar ta Hausa da hadin kan Hausawa ta Duniya tana da jajircewa wajen ta ga cigaban al'ummar Hausawa, su ma da s**a zama daga mambobinta za su ba da irin tasu gudummawa sosai domin cigaba da ganin ana samun nasarar hada kan al'ummar Hausawa a ko'ina a kowace kasa a fadin Duniya.

Ambasada Hajiya Samira Bala Usman, Tauraruwar Hausa da hadin Kan Hausawan Duniya ta gode wa dukkan wadanda s**a zo don taya ta murna a wannan matsayi da kuma yin kira ga dukkan 'yan kungiyar su ci gaba da ba da misali na kyakkyawan hadin kai a tsakanin su don gina ci gaban Gidauniyar.

Hoto: Ambasada Hajiya Samira Bala Usman, Tauraruwar Hausa da hadin kan Hausawan Duniya

20/05/2025

Stop waiting, start living! "Master Your Life @ 30" is officially here to ignite your empowerment and fill your journey with hope. This isn't just a book, it's your blueprint for success in your 30s and beyond.
> Dive into the vibe with my TikTok video! 👇
> Your transformation starts here:
> https://selar.com/113pa3
> https://a.co/d/fenvVOK
>









MEYE RA'AYIN KU KAN WANNAN LABARIN?Abin da ya sa muka dakatar da  nuna  Fima-Fiman Hausa masu dogon zango 22Cewar Abba A...
19/05/2025

MEYE RA'AYIN KU KAN WANNAN LABARIN?

Abin da ya sa muka dakatar da nuna Fima-Fiman Hausa masu dogon zango 22

Cewar Abba Almustapha.

Daga Ibrahim Muhammad

Hukumar tace Fima-fimai ta jihar Kano ta dakatar da nuna wasu manyan Fima-fimai guda 22 masu dogon zango. Shugaban Hukumar, Abba Al-mustapha ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran Hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman, ya raba wa manema labarai.

Ya ce Gwamnatin jihar Kano ta ɗauki matakin ne a kokarinta na tabbatar da ana bin dokar tace fima-fimai sau da kafa, tare da ƙara dora masana’antar Kannywood a kan saiti.

A cewar sanarwar, “An dauki matakin ne biyo bayan tattaunawa da manyan jami’an Hukumar tare da dogon nazari da aka yi domin kawo ƙarshen ƙorafe-ƙorafen ake yawan karba dan ƙara inganta ayyukan Hukumar tare da masana’antar kannywood”.

Sunayen fima-fiman da aka dakatar sune:
1. Dakin Amarya
2. Mashahuri
3. Gidan Sarauta
4. Wasiyya
5. Tawakkaltu
6. Mijina
7. Wani Zamani
8. Labarina
9. Mallaka
10. Kudin Ruwa
11. Boka Ko Malam
12. Wa ya san Gobe
13. Rana Dubu
14. Manyan Mata
15. Fatake
16. Gwarwashi
17. Jamilun Jiddan
18. Shahadar Nabila
19. Dadin Kowa
20. Tabarma
21. Kishiyata
22. Rigar Aro

Shugaban hukumar tace fima-fiman na Jihar, Abba Al-mustapha ya ƙara da cewa, doka ce ta bai wa Hukumar damar tace duk wani fim tare da lura da ayyukan masana’antar kannywood, matsawar suna da rijista da Hukumar a ko'ina suke, don haka ya shawarci masu ɗaukar nauyin fima-fiman da su tabbatar da bin wannan doka da dakatar da saka fima-fiman a gidajen talabijin da kafar sadarwa ta zamani.

Haka kuma ana sanar da su cewa su miko fima-fiman ga Hukumar domin tantance su, tare da ba su shaidar inganci ta tacewa nan da mako daya mai zuwa, wato daga Litinin 19 ga watan Mayu zuwa 25 ga watan Mayun 2025, domin gujewa fushin doka.

Hukumar ta nemi hadin kan dukkannin gidajen talabijin da Hukumar da ke lura da kafafen yada labarai ta kasa (NBC), kan su ci gaba da taimaka mata domin samun nasarar abin da ta saka a gaba na tsaftace Jihar Kano da masana’antar Kannywood.

Hoto: Shugaban hukumar tace Fima-fimai ta jihar Kano, Abba Almustafa.

Wasu tsofaffin sojoji da s**a gama aiki sun fada siyasa karkashin tsarin KwankwasiyyaDaga Ibrahim MuhammadWasu tsofaffin...
18/05/2025

Wasu tsofaffin sojoji da s**a gama aiki sun fada siyasa karkashin tsarin Kwankwasiyya

Daga Ibrahim Muhammad

Wasu tsofaffin sojojin Najeriya da s**a ajiye aiki su 24 sun tsunduma harkar siyasa ƙarƙashin tafiyar tsarin Kwankwasiyya, kuma sun ce sun rungumi tsarin ne don su bayar da tasu gudummawa a zaben 2027 don ganin jagoran Kwankwasiyya, Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso ya m nasara a tafiyar sa ta siyasa.

Sojojin sun bar aiki ne a watan Junairu na na bara bayan cika shekara 35 suna aikin soja, kuma sun bayyana goyon bayansu ga tafiyar tsarin Kwankwasiyya.

A ziyarar da s**a kai wa Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso a gidansa ƙarƙashin jagorancin Shugaban hukumar ba da tallafin Karatu ta jihar Kano, Dakta Kabiru Getso Haruna, ya bayyana ziyarar tsafaffin sojojin a matsayin babbar nasara ga tafiyar tsarin Kwankwasiyya.

A jawabinsa, Sanata Dakta Rabi'u Musa Kwankwaso ya yaba wa sojojin bisa sadaukarwar da s**a yi lokacin da suke kan aiki. Ga shi sun ɗauki lokaci mai tsawo sun sadaukar lokacin aiki soja, yanzu kuma suna so su sake sadaukarwa a tafiyar Damakwaradiyya, wannan abin a yaba musu ne.

Alhaji Muhammad Dankwairo ya yaba wa kokarin Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir kan bunkasa cigaban ilimiDaga Ibrahim Muhamm...
18/05/2025

Alhaji Muhammad Dankwairo ya yaba wa kokarin Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir kan bunkasa cigaban ilimi

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf da cewa, yana cika alkawarurrukan da ya ɗauka tun a yaƙin neman zabe a fannoni daban daban-daban a faɗin jihar. Alhaji Muhammad Hussain
Dankwairo, "Injiniya Mashkur", Manajan Daraktan na kamfanin "Mashkur International concept" ne ya bayyana hakan da yake zantawa da 'yan jarida.

Ya ƙara da cewa daga cikin muhimman manufofin Gwamnatin Abba Kabir Yusuf akwai bunkasa cigaban harkar ilimi, tun daga tushe, don ilimi ne kashin bayan duk wani cigaban al'umma da Gwamnan kuma yake mutukar kokari wajen aiki tukuru don ganin ilimin zamani da na addini na kyautatuwa da a yanzu cikin shekaru biyu ake ganin tasirin hakan.

Alhaji Muhammad Hussain Dankwairo ya ce a zuwan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi kasafin makudan kudade a kan cigaban harkar ilimi, ana ta gudanar da ayyuka daban daban-daban tun daga kai yara makarantu a ƙasashen waje domin karo karatun da gyaran makarantu da sake buɗe wasu makarantun Sakandire na kwana da manyan makarantu da aka yi da Gwamnatin baya ta rufe, yanzu ana cigaba da gudanar dasu .

Ya ce, malaman makarantu tun daga kan na Firamare da Sakandire shaida ne a kan yadda wannan Gwamnatin ta zo take kyautata walwala da albashinsu da sama wa dalibai kujerun zama a azuzuwa da samar da kayan aiki ga malamai duk domin kyautata bada ilimi mai inganci ga yara .

Alhaji Muhammad Dankwairo ya ce, ko a yan kwanakin nan mai girma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sahale za a bai wa malaman makarantu rancen kudi domin sayen ababen hawa don rage masu wahalar tsadar sufuri da za su rika biya a hankali cikin sauƙi.

Sannan an tabbatar da wasu malamai da a baya ke aikin wuccin gadi aka mayar da su na dindindin, aka kuma raba littattafai da kayan aiki ga dukkan sakatarorin ilimi da ke fadin kananan hukumomi 44 na jihar Kano da za su raba a dukkan makarantun jihar Kano gaba ɗaya.

Manajan Daraktan kamfanin Mashkur "International Concept ", Alhaji Muhammad Hussain Dankwairo ya ce, irin wannan jajircewa da Gwamna Abba Kabir Yusuf yake na gina ci gaban jihar yana da muhimmanci al'umma, musamman da suke kishin cigaba su ba shi hadin kai da goyon baya da taya shi da addu'a a kan Allah ya ci gaba da bashi nasara akai.

Hoto: Alhaji Muhammad Hussain Dankwairo.

Cibiyar "Beautiful Gate Centre" da haɗin gwiwar babban Sakataren Ma'aikatar jinkai na Tarayya, sun rarraba kekunan gurag...
18/05/2025

Cibiyar "Beautiful Gate Centre" da haɗin gwiwar babban Sakataren Ma'aikatar jinkai na Tarayya, sun rarraba kekunan guragu 100 a Kano

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Babban Sakataren Ma’aikatar jinkai na Tarayya, Alhaji Adamu Ƙofar Mata tare da hadin gwiwar "Beautiful Gate Handicapped People’s Centre"Jos sun raba kekunan guragu ga mutane 100 masu buƙata ta musamman ƙarƙashin ƙungiyar ci gaban Ƙofar Mata.

A yayin bikin rabon da aka gudanar a Unguwar kofar Mata, Kwamishinan kimiyya da fasaha na jihar Kano, Hon.Yusuf Ƙofar Mata ya yaba wa ƙoƙari da karamcin Sakataren din-din-din na Ma'aikatar jinkai na tarayya, Alhaji Adamu Ƙofar Mata, wanda ya zo da aikin da haɗin gwiwar "Beautiful Gate Centre"

Ya ce an yi wannan ƙoƙari ne ta hanyar zabo masu buƙata ta musamman daga Ƙofar Mata da kewayenta, kuma an yi nasarar ba su kekuna masu kafa uku guda 100, wanda hakan ya nuna cewa mutane da dama za su a ci gajiyar shirin.

Ya ce a madadin al’ummar unguwannin Ƙofar Mata, Zango, Zage, Dorayi A da B sun yi matukar godiya da irin wannan shiri da "Beautiful Gate Handicapped people's centre " da Sakataren dindindin na Ma'aikatar jinkai ta Ƙasa, Alhaji Adamu Ƙofar Mata. Suna kuma fatan sauran jama’a a cikin al’umma za su ci gaba da ba da gudumawa wajen ci gaban al’umma da ɗan abin da suke da shi domin kowane mutum yana da abin da zai ba da gudummawarsa ga ci gaban al'ummarsa, ko da nasiha mai kyau ne.

Saundra Yilgwan Darektan yaɗa labarai na "Beautiful Gate Handicapped people's centre " Jos, yayin da take zantawa da manema labarai ta ce, bikin rabon kekunan masu ƙafa uku na haɗin gwiwa ne tsakanin " Beautiful Gate Handicapped people's centre" da sakataren dindindin na Ma’aikatar jin kai da kula da bala’o’i, Dakta Yakub Ƙofar Mata don ba da kyautar kekunan guda 100 ga nakasassu a Ƙofar Mata da kewaye.

Ta ce irin haɗin gwiwar da s**a yi da sakataren na dindindin, wanda shine ya nemo mutanen da ke buƙatar kayayyakin sannan ya ba su jerin sunayen domin su samar da kayan ga waɗanda s**a ci gajiyar kuma sun ba su kekunan guda 100.

Sundra ta ce, suna ba da kayan kyauta ne ga waɗanda s**a ci gajiyar tallafin, saboda sun lura cewa mai buƙata ta musamman wasu daga cikin su da kyar suke zama, kuma ba su da lokacin zuwa makaranta ko wani abu, don haka abin da za su iya yi shi ne a ba agaji. Abin da ake bukata na farko shi ne ƙarfafa musu gwiwa, shi ya sa s**a bayar da wannan, an samar da dukkan kayayyakin a ofishinsu da ke Jos, sannan kuma kudin da suke hada kowane ɗaya ya kai N160,000

Jami'ar sashen watsa labarai ta "Beautiful Gate Handicapped people's center" Jos, Sandra Yilgwan ta ce ƙungiyar mai zaman kanta ce, kuma ta Kiristaci ce, amma ba sa nuna bambanci don haka ne ma ya sa kashi 80 cikin 100 na masu cin gajiyar shirin Musulmi ne, har ma suna da ma'aikata musulmi. Ba su damu da irin addinin da kake ba ko imanin ka ko kuma sashen da ka fito. Shekaru 20 kenan da kafa cibiyar da yanzu haka sun raba kekunan guragu sama da 40,000 kyauta da sauran kayayyaki ga masu buƙata ta musamman.

Hoto daga Sandra Yilgwan.

🚀 Unlock the Divine Power of Dhul-Hijjah! 📖✨ Are you ready to transform your worship and maximize blessings in the sacre...
14/05/2025

🚀 Unlock the Divine Power of Dhul-Hijjah! 📖✨

Are you ready to transform your worship and maximize blessings in the sacred month of Dhul-Hijjah? 🌙🕋

Introducing "The Ultimate Guide to Worship in Dhul-Hijjah"—your key to unlocking the true essence of these blessed days! 🔑📘 Excerpted from the renowned Mafatih al-Jinan, this book is your ultimate companion for spiritual elevation.

🌿 What’s Inside?
✅ Recommended acts of worship for the 10 sacred days (prayer, fasting, charity & more!)
✅ Deep dive into Arafah Day & Eid al-Adha—how to maximize rewards
✅ Special devotions for Ghadeer Day & Mubahala—unlock hidden spiritual treasures!
✅ Step-by-step guidance for beginners & seasoned worshippers alike

This isn’t just a book—it’s a roadmap to divine closeness! 🕌❤️

🔗 Grab your copy NOW: https://selar.com/733k54

Don’t let Dhul-Hijjah pass you by—elevate your worship, earn endless rewards, and draw nearer to Allah! 🌟

























💬 Tag a friend who needs this!👇

📲 Share & Repost for Barakah! 🤲

Embark on a transformative spiritual journey with "The Ultimate Guide to Worship in Dhul-Hijjah: Unlocking the Power of Sacred Practices." This comprehensive book is your key to unlocking the true essence of the blessed month of Dhul-Hijjah. It is an excerpts from the famous book Mafatih al-Jinan.Im...

Ciwon suga shi ya fi kai mutane Asibiti a Nijeriya, in ji wani rahotoA yankinku wace cuta ce ta fi kai mutane Asibiti?Wa...
06/05/2025

Ciwon suga shi ya fi kai mutane Asibiti a Nijeriya, in ji wani rahoto

A yankinku wace cuta ce ta fi kai mutane Asibiti?

Waɗannan ne cutukan da 'yan Najeriya s**a fi zuwa asibiti saboda su, a cewar ƙungiyar ƙananan likitoci ta Najeriya (Nigerian Association of Resident Doctors).

Kun lura da hakan kuwa?

An gudanar da bita ga limaman jihar Kano domin  nusar da su irin matakan da ake  bi  wajen gudanar da ayyukan da Gwamnat...
02/05/2025

An gudanar da bita ga limaman jihar Kano domin nusar da su irin matakan da ake bi wajen gudanar da ayyukan da Gwamnati take yi
In ji Hon. Ibrahim Waiya

Daga Ibrahim Muhammad.

Ma'aikatar yada labarai da al'amuran cikin gida ta jihar Kano ta gudanar da taron bita na kwanaki biyu ga limaman Juma'a na jihar Kano da niyyar kara bunkasa kyakkyawan alaka da ke tsakanin su da Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf ta karkashin Ma'aikatar.

Da yake zantawa da 'yan jarida bayan kammala taron bitar na kwanaki biyu Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da al'amuran cikin gida, Hon.Ibrahim Abdullahi Waiya ya bayyana cewa a matsayin Ma'aikatar da take da hakki wajen yada labarai da sanar da al'umma abin da ya shafi ayyuka da tsare-tsaren abubuwa da Gwamnatin jihar Kano take gabatarwa da kokarin samar da dangantaka tsakanin kowane rukuni na al'umma a madadin Gwamnatin Abba Kabir Yusuf s**a ga dacewar yi wa Limamai irin wannan bita.

Ya ce, bitar za ta kara samun fahimtar juna ta nusar da su kan abin da ya shafi ayyuka na Gwamnati domin samun ilimi na yadda al'amuran Gwamnati ke gudana yadda za su iya sanar da mutane yasda abubuwa ke gudana.

Ya kara da bayyana bitar da cewa wata gada ce aka shimfida da akalla za ta zama an yi kokarin tsuke tsayin dangantaka da ke tsakanin Gwamnati da dukkan rukunin al'umma kuma za su cigaba da kulla tattaunawa da limaman daga lokaci zuwa lokaci tsakanin su, wannan kawai farawa aka yi.

Hon. Ibrahim Abdullahi Waiya ya ce sun daukar wa kansu gabatar da tattaunawa da dukkanin rukuni na al'umma don tabbatar da cewa an dinke duk wata baraka ta rashin samun fahimta a kan abin da yake gudana a Gwamnati karkashin jagorancin Alhaji Abba Kabir Yusuf.

Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da al'amuran cikin gida Ibrahim Waiya ya bayyana malamai da cewa mutane ne mahimmai masu daraja da ya zama wajibi ga al'umma su mutunta su da girmama su domin suna sanye da riga muhimmiya da ba a iya sayen ta a kasuwa, riga ce da take siffanta su a matsayin magada Annabawa, mutane ne da ake sa ran duk abin da zai fito daga bakinsu da ayyukansu ya zama abin da zai nusar da al'umma ne, ya zama na shiriya kar ya zama abin da zai rikita lissafi ko ya zama abin da zai iya tayar da fitina ko wani abu makamancin haka a tsakanin al'umma.

Ya ce ya kamata malamai su fahimci muhimmancin da suke da ita a cikin al'umma, ba sa son duk abin da zai taba kimar su, suna kishinsu sun damu da su suna son su tabbatar duk abin da za su aikata da abin da za su fada ya yi daidai da koyarwa ta addini ba son rai ba.

Ya ce Gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da girmama su da kulla kyakkyawan alaka da su, su zama tsani wajen fadakar da al'umma irin abubuwan da ake yu a Gwamnatance domin mutane su fahimci yanda aikin Gwamnati yake da yadda ake gudanar da wasu abubuwa.

Kwamishinan ya ce shi ya sa s**a kawo mutane daban-daban s**a wayar musu da kai a taron bitar kan abin da ya shafi harkoki na mulki a tsari na Dimokuradiyya, su gane ya ake kasafin kudi, kuma wane abubuwa Gwamnati ta ke shigowa da su sababbi wajen kyautatawa da samar da kyakkyawar shugabanci a cikin al'umma na rage abin da ya shafi almundahana da dukiyar mutane.

Hon.Ibrahim Abdullahi Waiya ya ja hankalin Limaman da aka yi wa bitar da cewa bai dace wasu malamai su rika amfani da mimbarinsu wajen yin abubuwa na siyasa ba, Kowane Malami ya kamata ya bar ra'ayinsa na siyasa a zuciyarsa, idan ya hau mimbari ya fahimci cewa, yana wakiltar dukkanin rukuni ne na al'umma ba tare da nuna ra'ayi na siyasa ba.

Hoto:
Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da al'amuran cikin gida, Hon. Ibrahim Abdullahi Waiya.

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dillaliya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dillaliya:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share