05/12/2023
Rundunar sojin kasa ta bada hakuri game da jirginta da ya yi ruwan bamabamai kan yan mauludi bisa kuskure a Kaduna
Shugaban rundunar sojin kasa Laftanar Janar Taoreed Lagbaja da tawagarsa sun ziyarci garin Tudun Biri karamar hukumar Igabi jihar Kaduna, inda mutanen garin s**a gamu da iftila'in bam da ya fada bisa yan mauludi suna tsaka da gudanar da bikin a kauyen na Tudun Biri.
A ziyarar da shugaban rundunar sojin kasar ya kai, ya ce sun zo ne don su jajanta tare da bada hakuri game da wannan iftila'in da ya faru a cikin kuskure.
Ya ce yankin nasu na zagaye da yan bindiga, hakan ne ya sa bayan samun wasu bayanai game da yan bindigar rundunar ta yi niyar kai masu hari don darkake su, cikin tsautsai jirgin ya sauka kan wadannan mutanen da ba su ji ba su gani ba, inda ya tabbatar wa al'ummar garin da cewa za su gudanar da kwakkwaran bincike a kan jami'ansu da kuma na'urorin da s**a yi amfani da su dan kauce ma sake afkuwar irin haka
Ya kuma yi ta'aziya ga shugaban Jama'atu Nasarul Islam reshen jihar Kaduna da sauran malaman addinin Musulunci baki daya
Lagbaja ya kuma ziyarar makabartar da aka rufe waɗanda iftila'in ya rutsa da su don yi masu addu'a, sannan kuma ya ziyarci asibitocin da aka kai wadanda s**a jikkata don duba su
Za a iya tuna cewa Katsina Daily News ta rawaito cewa dama tun da farko rundunar sojin sama NAF ta nisanta kanta da kai wannan harin inda ta ce tun kafin iftila'in ya afku, ta share sama da awanni 24 ba tare da ta tada jirgi ya kai hari kan yan bindiga ba.