IKARA TV NEWS

  • Home
  • IKARA TV NEWS

IKARA TV NEWS An bude shafin Ikara TV News a 7 ga watan JANUARY 2023 don wallafa wa hausawa labarai

‘Yan Najeriya miliyan 70 za su samu N75,000 kowanne..Gwamnatin tarayya ta kammala shirye-shiryen raba tsabar kudi Naira ...
20/01/2025

‘Yan Najeriya miliyan 70 za su samu N75,000 kowanne..

Gwamnatin tarayya ta kammala shirye-shiryen raba tsabar kudi Naira 75,000 ga ‘yan Najeriya miliyan 70 a wani yunkuri na rage radadin wahala.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin jama'a, Hon. Aliyu Audu, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, ya bayyana cewa matakin ya dace da kudurin gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu na magance matsalar talauci a kasar.

Audu, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC ta kasa kuma tsohon mamba a kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar APC, ya bayyana cewa Tinubu ya bayar da isassun hujjoji na nuna kwazo a cikin watanni 19 kacal da ya yi yana mulki.
✍️ IKARA TV NEWS

DA DUMI-DUMI: Turji ya nemi yan uwansa yan bindiga su kai masa dauki su kuma sun mayar masa da martani cewa ba za su kai...
20/01/2025

DA DUMI-DUMI: Turji ya nemi yan uwansa yan bindiga su kai masa dauki su kuma sun mayar masa da martani cewa ba za su kai masa daukin ba...

Turji na cikin mawuyacin hali bayan da ya nemi daukin sauran manyan gaggan yan bindiga su kai masa dauki sakamakon luguden wutar da gamayyar Sojojin Najeriya ke yi masa amma kwamandoji yan bindigar s**a yi kunnen shegu da rokon nasa inda s**a ce ba za su tallafa masa ba a halin yanzu saboda su ma ta kansu suke

Me kuke fata?

Mahajjata daga Nijeriya za su biya Naira milyan 8.4 kudin aikin hajji a shekarar 2025
20/01/2025

Mahajjata daga Nijeriya za su biya Naira milyan 8.4 kudin aikin hajji a shekarar 2025

LABARI MARAR DADI: Tinubu ya amincewa kamfanonin sadarwa MTN, AIRTEL, GLO da 9MOBILE da su kara kudin Data 1GB ya koma 4...
20/01/2025

LABARI MARAR DADI: Tinubu ya amincewa kamfanonin sadarwa MTN, AIRTEL, GLO da 9MOBILE da su kara kudin Data 1GB ya koma 479.17 tura Message ta Sim Naira 6.67 kiran minti daya kuma Naira 18.33.

Me zaku ce?

13/01/2025

Dubban gidaje ne yanzu haka s**a zama toka a Los Angeles inda masu kashe gobara ke cewa aikin da suke na komawa baya duk da tallafin da suke samu daga tawagar Injiniyoyi da ke aikin katse dukkanin na’urorin da ka iya ingizawa ko kuma ta’azzara wutar dajin

Shugaba Tinubu ya amince da haramta aikata badala a rundunar sojin Nijeriya
12/01/2025

Shugaba Tinubu ya amince da haramta aikata badala a rundunar sojin Nijeriya

12/01/2025

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Aminu Magaji, Abdullahi Abubakar

08/01/2025

Follow for follow, follow 👉🏻
IKIKARA TV NEWSlease 🙏

Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, yayi gargadi ga 'yan majalisun zartaswa na Jihar Kano.Abba Kabir, ya bukaci ...
08/01/2025

Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, yayi gargadi ga 'yan majalisun zartaswa na Jihar Kano.

Abba Kabir, ya bukaci mambobin majalisar da su bijirewa duk wata jarabawar da za ta haifar da rashin aminci da rarrabuwar kawuna a majalisar ministocinsa.

Haka zalika gwamnan ya tunatar da kwamishinonin al’adunsa akan su Kara rike amana da gaskiya da mutunta juna a majalisar ministocin.

Haka kuma ya sha alwashin daukar matakin hukunta duk wani dan majalisar da ya yi watsi da ka’idojin da ya ginda ya cikin Gwamnantinsa.

Daga
IKARA TV NEWS

SUBHANALLAH: Masu Garkuwa Da Muțañe Sun Kashe Šhi A Yayin Da Ake Shirin Karbo Shi Kan Kudin Fansa Naira Milyan 20 Bayan ...
08/01/2025

SUBHANALLAH: Masu Garkuwa Da Muțañe Sun Kashe Šhi A Yayin Da Ake Shirin Karbo Shi Kan Kudin Fansa Naira Milyan 20

Bayan sun yi garkuwa da shi na tsawon sati biyu, sun yanke kuɗin fansa ₦40,000,000, inda da kyar s**a yarda a kan za a bada ₦ 20,000,000.

An yi ƙoƙarin zuwa karɓo shi jiya, yau muke samun labarin sun ķàśhe shi.

Allah Ya jikanka Alhaji Adamu Garba Mandi Ga-ga Ikara, Kaduna.

Hukumar EFCC da ke yaki da cin hanci a Nijeriya ta kori jami’anta 27 bisa laifin zamba da rashin da’a
06/01/2025

Hukumar EFCC da ke yaki da cin hanci a Nijeriya ta kori jami’anta 27 bisa laifin zamba da rashin da’a

Hadimar gwamnan Kaduna ta tsallake rijiya da baya.Mahara sun yi yunƙurin kashe Rachael Averick.Ta bayyana yadda ta sha d...
05/01/2025

Hadimar gwamnan Kaduna ta tsallake rijiya da baya.

Mahara sun yi yunƙurin kashe Rachael Averick.

Ta bayyana yadda ta sha da ƙyar daga hannun miyagu.


Ƴan sanda sun tseratar da mutum 18 daga harin masu garkuwa da mutane a KatsinaKarin bayani: https://rfi.my/BIF7
05/01/2025

Ƴan sanda sun tseratar da mutum 18 daga harin masu garkuwa da mutane a Katsina

Karin bayani: https://rfi.my/BIF7

05/01/2025

Yi tagging mutanen da masu SANA'A za su ƙaru da content ɗin su a 2025.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sake nada kwamishinoni biyu da ya sauke mukamai tare da nada mashawarta da wasu mukamai
05/01/2025

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sake nada kwamishinoni biyu da ya sauke mukamai tare da nada mashawarta da wasu mukamai

Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi ya ce yawon saɓa wa Allah da ’yan fim ke yi ya sa suke mutuwar fuju’a.
14/12/2024

Sheikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi ya ce yawon saɓa wa Allah da ’yan fim ke yi ya sa suke mutuwar fuju’a.

YANZU YANZU: 2027 Babban gangancin da mutanen Nigeria zasu Yi Shine Su zaɓe Wani ɗan takara a matsayin Shugaban kasa Wan...
14/12/2024

YANZU YANZU: 2027 Babban gangancin da mutanen Nigeria zasu Yi Shine Su zaɓe Wani ɗan takara a matsayin Shugaban kasa Wanda ba kwankwaso ba, Arewa zata iya Samun Mafita idan kwankwaso Ya Zama Shugaban kasa

Professor Wole Soyinka

Jaridar. Wakiliya ta rawaito cewa Fitaccen Marubucin nan na duniya dan asalin kasa Nigeria Professor wole soyinka ya bayyana jagoran Jam'iyar NNPP engr Dr Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin mutumin da zai fi kowa kokari wajen magance matsalolin Arewacin Nigeria

Wole soyinka ya bayyana cewa duk rashin tsaron dake faruwa a Arewacin Nigeria akwai matsalar rashin ilmi da alumma suke fama dashi , domin babu wani mai ilmi da zai dauki bindiga ya ringa kashe fararen hula wadanda basu jiba basu gani ba,

Shi kuwah kwankwaso taken tafiyarsa shine kowa yayi ilmi domin ya dogara da kansa , ilmi shine hasken rayuwa , sannan kaff cikin yan siyasar Arewacin Nigeria babu wanda yake burin ganin 'ya'yan talakawa sunyi ilmi sun zama wani abu a Nigeria kamar kwankwaso

Dan haka wannan tsari na kwankwaso shine tsarin da yafi kayatar dani

Inji Professor Wole soyinka

ya bayyana hakan acikin Tattaunawar da yayi da gidan talabijin na TVS Nigeria

IKARA TV NEWS
Mamman Dogon-koli

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when IKARA TV NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to IKARA TV NEWS:

Videos

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Videos
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share