Zauren dalibai littafin izziya

Zauren dalibai littafin izziya Aslm alaikum yan uwana dalibai wanna zauren dalibai ilimi yan uwana adunga turamana duk karatun littafin fikhu

09/10/2024
05/10/2024

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Abdullahi Zakariya, Mubashir M Zubair, Fiddausi Hussaini, Arhmard Ardermu, Itz Babban Yaro, Zaharaddeen Hamisu Sulaiman Hamizu, Khalifa Ahmed Assalafy, Yunuss Shu Waram

13/08/2024
Yaa Haiyyu Yaa Qaiyyum !     Allah Ka zaunar da Kasarmu Nijeriya lafiya da aminci, Ka taimaki Shuwagabanninmu kan abinda...
03/08/2024

Yaa Haiyyu Yaa Qaiyyum !

Allah Ka zaunar da Kasarmu Nijeriya lafiya da aminci, Ka taimaki Shuwagabanninmu kan abinda shine yardanKa, Ka shiryar mana duk baragurbin cikinsu damu baki ɗaya, Ka bamu damuna mai albarka, Aamin

Allaah ya jikanki da rahma
25/07/2024

Allaah ya jikanki da rahma

🥰🥰🥰
19/07/2024

🥰🥰🥰

KARFIN ZUCIYAR UWA A KAN ƳAƳANTAWato ita uwa, karfin zuwa da aka bata, karfin zuciya da dauriya da aka bata, kaso mafi y...
19/07/2024

KARFIN ZUCIYAR UWA A KAN ƳAƳANTA

Wato ita uwa, karfin zuwa da aka bata, karfin zuciya da dauriya da aka bata, kaso mafi yawa duka an bata ne akan ƴaƴan ta ba akan taba,

Da juriyar ta, da rikicin ta, da nacin ta, suna bayyana ne akan ƴaƴan ta,

Idan da yanzu zaka gamu da mace a hanya tana tafiya, haka kawai Bakasan taba Batasan kaba, ka rufeta da duka zata fita da gudu tana kururuwa amma in ɗanta karufe da duka ba zata gudu ba, jama'a munfahimta,

Haka kawai tana tafiya ka wanke ta da mari za tayi ihu ta nemi ɗauki wataƙil ta ruga da gudu amma in ɗanta ka taɓa tsayawa za tayi, saboda karfin zuciyanta akan ɗanta ba daidai bane da akan kare kanta,

Koh kaza ce, ƴaro ɗan shekara biyu da yake rarrafe zai iya korar kazar daga inda take kuma ta gudu, amma in ƴanƴanta ne ko Ubansa Bazai koreta ta gudu ba, hakane ko ba haka ba, hakane,

Idan ƴaƴanta ne, idan ƴaƴanta ne ko babansa bai isa ya koreta ta gudu tabar ƴaƴanta ba, amma in itace tsuran ta yaro mai rarrafe zai koreta kuma ta gudu,

Wannan haka tinkiya take, haka kariya take, haka a kuya take, haka saniya take,.

Idan barewa taga abinda zai farauce ta zaki, da gudu take fita iya ranta amma in ɗanta zaibi tsayuwa take ko zai kasheta, itafah uwa haka take, da haka kuma kaga ka girma,

Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum Hafizahullah

The Ancient 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum.
18/07/2024

The Ancient 4,500-Year-Old Tunic at the Egyptian Museum.

IBNUL ƘAYYUM CIKIN MADÅRIJIS-SÅLIKIN YACE: Allah maɗaukakin sarki yana fushi in ba”a roƙarsa” shi kuma ɗan Adam yana fus...
18/07/2024

IBNUL ƘAYYUM CIKIN MADÅRIJIS-SÅLIKIN YACE: Allah maɗaukakin sarki yana fushi in ba”a roƙarsa” shi kuma ɗan Adam yana fushi ne idan ana roƙonsa.

Wannan maganar ta Bajimin Malami tayi dai-dai da faɗin Annabi Sallallahu alaihi Wasallama inda Yace: من لم يسأل الله يغضب عليه Duk wanda baya roƙon Allah” Allah yana fushi da shi.

Ashe kenan aiki ya rage ga bawa ya zaɓi wa zai roƙa” wanda in aka roƙe shi zai fushi ko wanda in ba’a roƙe shi ba zai fushi. A cikin Suratu (Nahali) Allah madaukakin sarki cewa Yai: Abinda ke wurin ku ne yake ƙarewa” Wanda yake wurin Allah tabbatacce ne baya karewa” Da sannu zamu sakanyawa waɗanda s**ai haƙuri ladansu da mafi kyawun abinda s**a aikata.

مَا عِندَكُمْ يَنفَدُ وَمَا عِندَ اللّهِ بَاقٍ وَلَنَجْزِيَنَّ الَّذِينَ صَبَرُواْ أَجْرَهُم بِأَحْسَنِ مَا كَانُواْ يَعْمَلُونَ

Tun da abinda ke wurin bayi ne yake ƙarewa abinda yafi dacewa shine a roƙi wanda nasa baya ƙarewa sai dai yai ta tabbata” Allah kenan.

A cikin Suratu (Ghåfir) ma cewa yai: Ubangiji Allah maɗaukakin sarki Yace ku kira shi” (Kira na Bauta dana buƙata) Duk wanda ya girman kai ga barin roƙo na/Bauta min da sannu zan shigar da shi wutar jahannama yana ƙasƙantacce.

( وَقَالَ رَبُّكُمُ ادْعُونِي أَسْتَجِبْ لَكُمْ ۚ إِنَّ الَّذِينَ يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ )
غافر (60)

WANNAN YASA AL'IMÅMU SA'ADÍY RAHAMATULLAHI ALAIHI CIKIN TAFSIRINSA YACE:

هذا من لطفه بعباده، ونعمته العظيمة، حيث دعاهم إلى ما فيه صلاح دينهم ودنياهم، وأمرهم بدعائه، دعاء العبادة، ودعاء المسألة، ووعدهم أن يستجيب لهم، وتوعد من استكبر عنها فقال: { إِنَّ الَّذِينَ يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ } أي: ذليلين حقيرين، يجتمع عليهم العذاب والإهانة، جزاء على استكبارهم.

Wannan Na daga cikin Tausayin Allah ga bayinsa” kuma wannan ni'imar Allah ce me girma” ta yadda ya kira bayi zuwa ga abinda gyaruwar duniyarsu ce da addininsu” Ya umarcesu da su kira shi” kira na bauta” da kira na buƙata” kuma yai musu alkawari zai amsa musu (in sun kira shi)

ZANGA-ZANGA BA ITA BA CE MAFITA!Mun wayi gari da kiraye-kiraye daga mutanen mabambanta akan lallai jama’a su fito zanga-...
18/07/2024

ZANGA-ZANGA BA ITA BA CE MAFITA!

Mun wayi gari da kiraye-kiraye daga mutanen mabambanta akan lallai jama’a su fito zanga-zanga musamman matasa a wannan ƙasa, don irin halin da mutane da yawa suke ciki na tsanani da rashin tabbas!

Abin mamaki, cikin masu irin waɗannan kiraye-kirayen har da wasu malamai da masu dangantakan su da malumta! Har wani ke cewa “Yadda democracy take lalura, haka ma zanga-zanga tsarin Mulki ya bayar da dama mutane su fito su ce ba su yarda ba…”

Ba dogon rubutu zan yi bai sai dai, in yi ɗan tsokaci a takaice:

1. Allah Ya Madaukaki Ya ce:

﴿وَإِذا جاءَهُم أَمرٌ مِنَ الأَمنِ أَوِ الخَوفِ أَذاعوا بِهِ وَلَو رَدّوهُ إِلَى الرَّسولِ وَإِلى أُولِي الأَمرِ مِنهُم لَعَلِمَهُ الَّذينَ يَستَنبِطونَهُ مِنهُم﴾ [النساء: ٨٣]

“Kuma idan wani lamari ya zo musu game da zaman lafiya ko tsoro, sai su yaɗa shi. Da a ce sun mayar da shi zuwa ga Manzo da shuwagabanni daga cikinsu, da lallai wadanda suke bin diddigin al’amura da sun sani (a yaɗa kor kar a yaɗa)…”

Wannan Ayah jigo ce a duk abinda za ka yi don kaucewa da na sani, da aika-aika.

2. Abu ne tabbatacce cewa za a samu zalunci da tauye haƙƙoƙin mutane daga shuwagabanni, amma kuma da Sahabbai s**a tambayi Manzo ﷺ ko za su yi fito-na-fito da irin waɗannan shuwagabannin sai ya ce: "Ku yi haƙuri..." Sai ya hana fito-na-fito da shuwagabanni duk da zaluncinsu har ya ce: "Ko da ya doki bayanka, kuma ya ƙwace dukiyarka", don muhimmancinsu, ko da akwai zalunci, da kuma illar da rashin su kan jefa mutane!

3. Al-Imam AlHasan Albasriy ya ce: "Ita wannan fitina idan ta fuskanto, duk wani malami ya na sanin ta, in kuma ta wuce sai kowane jahili ya gane ta!

Wannan ya yi k**a da halin da da yawan matasa ke ciki a ƙasar nan, da wasu masu nasabtuwa zuwa ga ilimi, na yadda sun kasa gane cewa wannan kiraye-kirayen na zanga-zanga da bore, da tutsu, fitina ce da in ta zo Allah kaɗai Ya san yadda za a ƙare!

ALQUR'ANI    Ibnul Qayyim (R) yace: "Alqur'ani magani ne na abinda ke cikin ƙiraza, yana tafiyar da abinda shaiɗan ke je...
14/07/2024

ALQUR'ANI

Ibnul Qayyim (R) yace: "Alqur'ani magani ne na abinda ke cikin ƙiraza, yana tafiyar da abinda shaiɗan ke jefawa a cikin su na waswasi da sha'awa da gurɓatattun nufi"

إغاثة اللهفان 181/1

Mutane bazasu gusheba da Alkhairi muddin basu yi hasadar juna ba ,maana suna cikin sharri  muddin sun rike Hasada
11/07/2024

Mutane bazasu gusheba da Alkhairi muddin basu yi hasadar juna ba ,maana suna cikin sharri muddin sun rike Hasada

حتى وإعراب ما بعدها
10/07/2024

حتى وإعراب ما بعدها

YI GUUM DA BAKIN KA!!!Gida ne zaka saya? Yi guum da bakin ka. 🙊Sabuwar mota ce zaka saya? Yi guum da bakin ka. 🙊Aure zak...
10/07/2024

YI GUUM DA BAKIN KA!!!

Gida ne zaka saya?
Yi guum da bakin ka. 🙊

Sabuwar mota ce zaka saya?
Yi guum da bakin ka. 🙊

Aure zaka yi?
Yi guum da bakin ka. 🙊

Hutu zaka tafi?
Yi guum da bakin ka. 🙊

Course zaka tafi?
Yi guum da bakin ka. 🙊

Promotion ne ka samu?
Yi guum da bakin ka. 🙊...

Kashi 99% na dalilin da ya sa mafarkan mu basu zamo wa gaskiya, a lokacin da muna gaf da ganin haske, shine muna buɗe bakunan mu ga mutanen da basu dace ba a lokacin da bai dace ba

Bai dace ba muna muna bayyana nasarorin mu ko kuma wassu ayyukan mu da muka sanya a gaba ga wassu waɗanda suke Abokai ne na bogi. Hassada da kambun baka na mutanen mu Ya ishi wargaza mana wassu lamuran..., tun kafin mu su kasance. Don haka yi guum da bakin ka🙊.

Yawancin abokan ka, suna buƙatar ci gaban ka, ammana ba wai sama da su ba.

Yauwa wani tunatarwa!

Hatta wassu daga cikin ƴan gidan ku da dangin ka, suna da wata gaba da kai a ɓoye, ammana basu isa su hana abinda Ubangiji Ya yi nufi a kanka ba.

Mu ankara, mu tuna cewa da ace kifi ya yi guum da bakin shi, ƙugiyar masunci da ba zata k**a shi ba.

Allah Ya mana jagora ☺️ ☺️ ☺️

 Duk Abin da Zamuyi Mu Tabbatar Annabi ﷺ Shine Role model din mu
10/07/2024



Duk Abin da Zamuyi Mu Tabbatar Annabi ﷺ Shine Role model din mu

Address

Hong

Telephone

+2347063226444

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zauren dalibai littafin izziya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zauren dalibai littafin izziya:

Share

Category