15/05/2023
Wannan ita ce tarbiyya!
Malami na tafiya tare da ɗalibinsa, sai s**a zo wucewa ta wani Lambu, a gefen shiga lambun sai s**a ga wani takalmi duk caɓi ya ɓata shi.
ÆŠalibi ya cewa Malaminsa: bari na É“oye wannan takalmin sai mu koma gefe don ganin yadda halin mai takalmin zai kasance, lalle zamu sha dariya.
Malam ya cewa É—alibinsa: da ka yi masa wasan da zai É“ata masa rai gwanda ka yi masa wanda zai faranta masa rai. ÆŠauki kuÉ—in dake tare da kai, sanya a cikin takalmin, mu koma gefe don ganin irin murnar da mai takalmin zai yi...!!
Jim kaÉ—an wani dattijo ya fito daga lambun, ya nufi wurin da ya ajiye takalmansa, ko da É—aga takalman sai ya ga kuÉ—i a ciki, sai ya faÉ—i a wurin yana Sujjadar godiya ga Allah, yana mai cewa: Ya Allah! Nagode maka daka bani abin zan sayawa matata magani, nagode maka da ka bani abin da zan ciyar da Iyalina.
Malamin da ɗalibinsa suna gefe sai hawaye ke zuba daga idanuwansu. Malami ya cewa ɗalibi: kar ka yadda ka rinƙa yiwa mutane wasan da zai ɓata musu rai domin baka san halin da suke ciki ba.allah yasa mudace 🤲