Abdulkadir Usman Ahmad

Abdulkadir Usman Ahmad You are free when you don't care what people think of you

I have reached 100 followers! Thank you for your continued support. I could not have done it without each of you. 🙏🤗🎉
26/12/2023

I have reached 100 followers! Thank you for your continued support. I could not have done it without each of you. 🙏🤗🎉

21/10/2023

Ya Allah kagafarta mana Zunubanmu kasamu chikin gidan Aljannar firdausi.

19/10/2023

Rayuwar matashi a nigeria.
Kafita ka samo 1000, abincin Rana 300, na dare 300, daga gida zuwa kasuwa zuwa 200 dawowa 200.
Shin me zai Tara haryayi tunanin ci gaba.
Allah yasa mu dace.

18/10/2023

Babban abinda ya tabarbara karatu a nigeria (certificate) ya janyo ana karatu irin na jeka nayika.
Allah yasa mu Gane.

14/10/2023

Idan ka ji matsala ko rashin lafiyar da wani yake fama da ita, sai ka rasa ma me za ka ce ko me za ka yi. Sai kuma ka ƙara gode wa Allah da halin da kai kake ciki. Allah ka ba mu ikon cin jarabawar rayuwar duniyar nan, amin.

ABIN DA YAKAMATA KU SANI GAME DA ALAƘAR NIGERIA DA NIGER.Nigeria da Niger, Abokai ne, kuma makusanta, akwai alaƙa ta kus...
04/08/2023

ABIN DA YAKAMATA KU SANI GAME DA ALAƘAR NIGERIA DA NIGER.

Nigeria da Niger, Abokai ne, kuma makusanta, akwai alaƙa ta kusa a tsakanin waɗannan ƙasashe biyu, sau da yawa ma, idan ku ka kalla cikin ɗabi'un su sunyi kusan ɗaƴa, wasu 'ƴan yankin da ke tsakanin bodojin Nigeria da Niger su kan fi zaɓar alaƙa da Niger sama da Nigeria, cikin Niger suke shiga domin gudanar da ayyukan su na yau da kullum, ko kuwa domin kasuwanci, su kan shiga su gama ayyukan su, ko kasuwancin su, da yammaci ko dare su koma gidajen su wajen iyalan su.
Haka zalika suma mutanen yankin bodojin Niger da Nigeria s**an aiwatar da irin hakan, ba don komai ba, sai don sabawa da akayi da juna.

Akwai auratayya da ta shiga tsakanin mutanen waɗan nan ƙasashe guda biyu.
Mafi akasarin mutanen yankin addini iri ɗaya suke yi, hakan yasa suke alaƙa da junan su.

Mutanen yankin kudancin Nigeria ba mu da wata alaƙa dasu ta kusa, sai dai ta nesa, tunda mun kasance ƙasar mu guda da su, ɗabi'un mu ba ɗaya bane da su, sannan akasarin su ma ba addini iri ɗaya muke dasu ba, River Niger ya raba mu (su turawa sun san wannan).

'Ƴan Niger kuwa sune 'ƴan uwanmu, babu wani ruwa ko sahara ko wani abu da ya raba mu, an same mu kusan iri ɗaya, kuma ɗabi'un mu da addinin mu, da cigabanmu, shiyasa turawa s**a raba mu domin haɗewarmu zai basu matsala. Kuma sunyi nasara tunda a yanzu ɗan Nigeria yafi ganin ɗan Kudu a matsayin ɗan uwansa akan ɗan Niger.

Yanzu magana ma ake ta yaƙi tsakanin Nigeria da Niger, tunda dai Nigeria ita take da shugaba a ƙungiyar (ECOWAS), Wai don lalacewa irin ta wasu mutanen mu, har sun ma fara zagin junansu a tiktok takan batun. Wanda wannan abin takaici ne a gare mu.

To ku sa ni, yaƙin da turawan mulkin mallaka suke so su haddasa a tsakan-kanin ƙasashen yammacin Africa, babu abinda zai haifar sai dai maida ƙasashen baya, da taɓarɓarewar abubuwa, musamman a waɗan nan yan ku nan da abin zaifi ƙamari.

Misali: Abin Allah shi kiyaye, idan yaƙi ya ɓarke tsakanin Nigeria da Niger,
Tabbas za'a illat.

Masha Allah Allah ubangiji ya Kara hada kanmu ya Kara mana zumunci.
18/07/2023

Masha Allah Allah ubangiji ya Kara hada kanmu ya Kara mana zumunci.

18/07/2023

Yayin gabatar da jawabi na ga tsofaffin dalibai na makarantar ADO GWARAM

19/06/2023

Yi qoqari ka shuka alheri a cikin wadannan kwanakin masu daraja da alfarma. Da yawa daga cikin bayin Allah sun yi burin ganinsu amma Allah bai rubuta ba; Kai ma wata rana za su zo ba ka a wannan duniyar.

Jameel Muhammad Sadis

MATAR BAHAUSHE.
16/06/2023

MATAR BAHAUSHE.

15/06/2023

Ganduje ya nemi kotu ta dakatar da Hukumar EFCC daga bincikensa akan bidiyon dala.
Shin meye Ra ayinku kanawa

19/02/2023
25/05/2022

Duk wata masifa da take faruwa a arewa ko akan ‘Yan Arewa mazauna kudancin kasarnan da wahala kaji Shugabannin mu sunce uffan ba. Sobada tsoro da munafukar zuciya.

Amma GAS CYLINDER Yana fashewa a Sabon Gari sai gasu sun zubo babba riga rukuni rukuni sun zo Jaje,
Duk irin Ibtila’i na gobara da rashin Manya mutane da mu kai bai sa su sun zo ba.

Naji Ance Gwamnatin Kano har milliyoyin kudi ta bayar domin tausayawa.

Abu ne mai wahala kaji a kudu wani shugaba yayi haka domin ragewa ‘Yan Arewa mazauna can radadin kashe ‘Yan uwanmu da akai ko tozarci da barnatarmusu da dukiya da ake. Still babu wani Babba daga arewa da yake magana. Amma su na yin magana akan Deborah, shugabanninmu na rawar jiki s**a taya su.

Ido yana kallon ku, ranar bukatarku za ta zo. Shugabanni da masu rike da madafan iko cikin maza da mata. Da masu munafukar zuciya cikin manyanmu na Arewa, da masu bada kariya ga mai batanci.

A hada Munafukan masu daukaka a arewa da influencers.

Wannan lokacin ba Deborah bace ko?

Na dauka HARIRA mai dauke da ciki wata 9 haihuwa ko Yau ko gobe da ‘Ya’yanta 4 Fatima, Khadijah, Hadiza da Zaituna
da a kaiwa kisan gilla Yan uwanku ne. Muna nan Muna Jiran muryarku.




23/02/2022

*LOKUTAN_AMSAR _ADDU'A*

Don Allah ko bazaka karanta ba katura a groups saboda Al'umma su Amfanq da kai

Kowanne lokaci idan mutum yayi addu'a Allah yana karba.
Sai dai Ubangiji cikin baiwarsa
da falalarsa ya ke'banci wasu
lokuta ya sanya musu albarka
da baiwa fiye da sauran lokutai..

Wadannan lokutan sun hada da:

1. DAREN JUMA'A: Wato ranar
alhamis da dare, da kuma
wunin jumu'ar. Ma'aikin Allah
(alaihis salam) yace "babu wani
bawa wanda zai dace yana addu'a acikinta fache sai Allah
ya amsa masa".

2. WATAN RAMADHAN: gaba
dayansa lokaci ne na amsar
addu'a.

3. LAILATUL QADARI: Shima
lokacin amsar addu'a ne.

4. TSAKAR DARE: Musamman ma sulusin karshensa.. Lokaci ne da Allah yake gwanjon rahamarsa ga bayinsa.

5. LOKACIN DA AKE KIRAN
SALLAH, DA KUMA TSAKANIN
KIRAN SALLAH DA TADA IQAMAH.

6. LOKACIN DA AKA IDAR DA
SALLOLIN FARILLAH.

7. LOKACIN DA AKA GAMA
KARATUN ALQUR'ANI, KO
WA'AZI KO WATA KOYARWA TA
ILMI: Shima lokacin karbar addu'a ne.

8. LOKACIN DA ZAKARA YAYI CHARA. Shima lokacin amsar
addu'a ne.

9. LOKACIN TAFIYA TA ALHERI:
k**ar tafiya hajji, sada zumunci, jihadi, ko fatauci.
Shima lokacin amsar addu'a.

10. RANAR ARFA: awannan
ranar, da wanda yake Makkah,
da wanda yake gida, duk Allah
yana amsar addu'arsu.

11. LOKACIN ZUBAN RUWAN
SAMA_ Shima ana amsar addu'a acikinsa.

12. LOKACIN DA AKA TSAIDA
SAHUN YAQIN DAUKAKA
KALMAR ALLAH.. Shima ana
amsar addu'a cikinsa.

13. LOKACIN DA MUTUM YAYI
SUJJADAH. Shima ana amsar
addu'a cikinsa.

14. LOKACIN DA MUTUM YA
FARKA DAGA BARCI: musamman idan mutum ya karanta "sub'hanallah wal'hamdulillah, wa la'ilaha'illal-Lah wallahu akbar" (QAFA 10). Duk abinda ka roka Mustajabah.

Don Allah duk wanda yakaranta yatura a groups 3 tunatarwa ga wanda basuyi like ɗin wannan page suyi like ko following Sabiida faɗakarwa na gaba

ALLAH YA SA MU DACE.

16/02/2022

HAKURI 'IRIN NA ANNABI AYYUB.

Allah T yabawa annabi ayyub arziki na dukiya da 'ya'ya maza har 7 da 'ya'ya mata kwatankwacinsu, sai Allah yayi nufin ya jarabci bawansa kuma annabinsa ayyub, sai kasuwancinsa s**a karye, yayansa s**a mutu, gidansa ya rushe, dabbobinsa s**a mutu sannan Allah ya jarabceshi da rashin lafiya ajikinsa.

Lokacin da rashin lafiya ta tsananta gareshi mutane s**a gujeshi don tsoron karsu gogi kalan rashin lafiyan, s**a fitar dashi wajen gari ba wanda yatsaya tareda shi sai matarshi tana masa hidima tana kula dashi, takanje tayi aiki a gidaje don tasamu kudin dazata kula da kanta da mijinta.

Bayan wani lokaci sai mutanen gari s**a kyamaceta tsoron kada su gogi cutan mijinta a jikinta har yakai babu wanda zai dauketa aiki.

Ance annabi ayyuba ya rayu tareda wannan cuta tsawon shekara 18 yana hakuri bai taba kai kuka ga kowa ba, lokacin da matarsa taga yanayi ya tsananta a garesu sai tace, ya annabin Allah ka roki Allah ya yaye maka wannan bala'i, sai yace shekara Nawa mukayi acikin jin dadi? Tace 80, yace inajin kunyar Allah saboda banyi rayuwar da takai na jin dadinaba da Allah yayimin acikin wannan bala'i.

Sai matarsa lokacin data rasa mafita ta yanke shawaran siyar da Rabin gashinta don tasamu abincin da zasuci, lokacin data kawo abincin annabi ayyub ya tambayeta ina tasamu bata fada ba, washe gari ta siyar da gashinta saura takara samo musu abinci s**aci.

Lokacin da kanta ya yaye sai annabi ayyub yaga babu gashi sai ya fahimta meke faruwa, sai yaji kunyan ubangiji kar yaroki shi yabashi lafiya sai yace k**ar yadda Qur'ani yazo dashi.
"ربي إني مسني الضر وأنت أرحم الراحمين"
Ya Allah ni cuta ta sameni kuma Kaine mafi jinkan masu jinkai.

Sai al'amari yazo daga wurin Allah madaukakin sarki cewa, "أركض برجلك هذا مغتسل بارد و شراب"
Ka shuri kasa da kafarka ruwa mai Sanyi zai fito nasha da wanka.

04/02/2022

Kukasance da gidan badamasi domin chanchare kodimon nishadi tare da raha
# Falalu a dorayi

28/01/2022

Kalma 1 ga wannan Zaƙaƙurin Makafci.

1. Mawaƙi ne
2. Marubuci ne
3. Darecta ne
4. Music producer ne
5. Sound Engineer ne
6. Rapper ne
7. Lyricist ne
8. Video edita ne
9. Comedian ne
10. MC ne
11. Motivator ne
12. Radio presenter ne
13. Shine Shugaban Kamfanin Algaita Dubstudio.

Hallau kuma yana fassara Fina-fina zuwa harshen Hausa, sannan yana hawa murya samada 13 shi kadai.

A rayuwata ban taɓa ganin ɗan Baiwa samada wannan ba.

Jinjina ga Oga Buzo Danfillo.

Daga naku Ãbûbäkår Êkâ.
Gabatarwa:- @

22/01/2022

Madallah da Aiki Nagari.
Kyaftin din Super Eagles na Najeriya, Ahmed Musa, ya bayar da gudunmawar dalar Amurka 1,500 domin kula da wani babban masallacin birnin Garoua na kasar Kamaru inda 'yan wasan musulmi s**a gudanar da
Ibadar Sallah. Allah Ya Saka Masa da Alkairi.

Ya kara masa suttura da albarka. Amin.

14/01/2022

Y A U J U M A’ A
MU YAWAITA SALATIN ANNABI
Mai salatin Annabi (SAW) zuciyar sa kullum tsarkaka take, sannan hanya ce da zata kai bawa ya samun Aljannah tun kafin mutuwarsa.

Yiwa Annabi (SAW) salati na tunatar da bawa abin da ya shigemar duhu, Ko ya manta shi. Sannan salati a gareshi kesa ka fita daga cikin marowata a gun ALLAH.

Salati shine abin da idan kana yinsa ka tsira. Ubangiji Jallah Wa Alah ya bamu ikon yi. Amin.

Allahumma Salli ala Muhammadin wa'ala Ali Muhammadin, k**a sal-laita 'ala Ibrahima wa'ala Ali Ibrahima, innaka Hamidun Majid. Allahumma barik 'ala Muhammadin wa 'ala all Muhammadin, k**a barakta 'ala Ibrahima wa'ala Ali Ibrahima, innaka Hamidun Majid."
Jum@tMbrk &

Kyakykyawan labari Allah ya shiga lamuran talakawan sa
12/01/2022

Kyakykyawan labari
Allah ya shiga lamuran talakawan sa

09/01/2022

Rayuwar Shaikh Ahmad Bamba Abar Kwaikwayo Ce Ga Sauran Malamai

Daga Indabawa Aliyu Imam

Daga sanda aka sanar da rasuwar Shaikh Ahmad Bamba, ba iya Kano ba, Najeriya ce ta girgiza, duk inda ka je yabon sa ake yi ana masa addu'o'i. Haka WhatsApp Status duk hotunansa ake gani. Ko'ina ka le'ka a dandalin Facebook alhininsa ake ana addu'ar Allah ya jikan sa ya gafarta masa.

Kowa yabon sa yake yana ambatar alkhairi a kansa. Babu d'an Izala, Tariqa ko Shi'a kowa jimamin rasuwarsa yake yi, wanda dattako da nagartarsa ce ta haifar da hakan. Na tabbata kowanne Malami zai so ya sami irin kyakkyawar shaidar da Shaikh Ahmad Bamba ya samu bayan rasuwarsa. Shi Shaikh Ahmad Malami ne wanda ya saita alakar rayuwarsa kan karantar da mutane addinin musulunci musamman hadisan Annabi SAW. Duniya ba ta gabansa, ya kan fad'i gaskiya a ko'ina ba tare da tsoron abin da zai je ya dawo ba. Malami ne wanda ke kwatanta gaskiya da adalci, ba ruwansa da ta'assubanci ko kungiyanci. Wannan ya sa kowanne musulmi ke kaunar sa kuma ke masa addu'ar dacewa da Aljannah.

Shaikh Ahmad na daga Malaman da ke fada wa shugabanni gaskiya. Sannan Malami ne mai riko da sunnar Annabi SAW kuma yana girmama sha'anin Ma'aiki SAW matuka. Ga shi Allah ya ba shi dacewa da babbar ranar ta juma'a. Ubangiji ka ji kansa ka gafarta masa ka kyautata namu karshen.

10/12/2021
10/12/2021

Su Tawaga manya,
Bai je sokoto jaje ba, yaje lagos
Bai je kano jaje, yaje Lagos
Bai je katsina jaje ba, yaje Lagos

Indai fadar Allah wadai ce, kullum ita ce a fatar bakin Shugaba. Ya fade ta yafi sau 1000 Idan abu ya faru a arewa.

Babban namijin kokarinsu shine su tura tawaga su saka babbar k**ar tsofaffin maroka su yi muku jaje. Shi kuma yana gida ya turo muku da Allah wadai ta bakin ‘Yan baka.

Ni dai ganina da Shugaban sama ya tura tagawar yin jaje sun wakilce shi wajan kaddamar da littafi. Shi kuma ya tafi jaje inda masifa ta afku.

02/03/2021

BAYANI GAME DA MUQABALA

Gobnatin Jahar Kano karka shin jagorancin Dr Abdullahi Umar Ganduje ta Sanya ranar muqaba da Abduljabba Shiekh Nasiru Kabara

Zaa gabatar da wannan muqabala k**ar haka:

Ranar lahadi 7-03-2021 da misalin karfe 9:00 na safe, A fadar Mai Martaba sarkin kano Alhj. Aminu Ado Bayero

Muqabalar zata samu wakilci daga bangarori mabambanta k**ar haka:

1. Kadiriyya
2. Tijjaniyya (Faira)
3. Izala (Ahlussunna)

Manyan Gidajen radio da jaridu da sauran kafafen sadarwar da zasu haska sun hadar da:

1. Shafin Bbc hausa
2. Shafin Daawatulhaq (Https://Facebook.Com/dharulilmfoundation)
3. Africa Tv
4. Sunnah Tv
5. Freedom Radio
6. Guarantee Radio
7. Rahama Radio

Da sauran Manyan jaridun kasar nan

Za'a iya samun Muqabalar bayan an kammala a Telegram na Daawatulhaq dake kasa 👇

Https://t.me/Daawatulhaq

Allah ya ganar damu gaskiya ya bamu ikon bin ta yasa ayi lafiya a gama lafiya.

Daawatulhaq
28-02-2020

Kasance da Www.daawatulhaq.com domin samun karatuttukan malaman sunnah a saukake

ISTIGFAAR!!!RASULULLAH (S A W ) YACE duk Wanda ya lazimci yin istigfaari Allah zai  Sanya Masa mafita daga kowanne kunci...
19/02/2021

ISTIGFAAR!!!

RASULULLAH (S A W ) YACE
duk Wanda ya lazimci yin istigfaari Allah zai Sanya Masa mafita daga kowanne kunci, da kuma yayewa daga kowani bakin ciki ,ya kumu azurtashi ta yadda baya tsammani

Aciki hadisi KUDISI Allah yace:
Ya ku bayina ! Lallai ku Kuna yin laifi dare da Rana , nikuma Ina gafarata; kunemi gafarata , zan gafarta muku
"Muslim"

Astaghfirullah Al Azeem Al lazi la ilaha illa huwal hayyul Qayyum wa atubu ilaih

Allah yai gafara garemu da iyayenmu da alummah baki daya.

JUMATMBRK &

*ABUBUWA BAKWAI (7) DAKE SA MALA'IKU**SUYIMA ADDU'A*.1± Lokacin da kake jiran sallah a masallaci..2± Lokacin da kake sal...
01/02/2021

*ABUBUWA BAKWAI (7) DAKE SA MALA'IKU*
*SUYIMA ADDU'A*.

1± Lokacin da kake jiran sallah a masallaci..
2± Lokacin da kake sallah a sahun farko..
3±Fadin Ameen bayan karatun fatiha..
4± Sallar subhi acikin Jam'i..
5± Yin addu'a ga dan uwanka musulmi
abayan idonsa..
6± Ciyarwa fisabilillah..
7± Koyar da mutane
Alkhairi.

With excellence
31/01/2021

With excellence

If you don't know anything about someone's experience, don't make a wrong story
13/01/2021

If you don't know anything about someone's experience, don't make a wrong story

Address

Garun Malam

Telephone

+2348069368301

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Abdulkadir Usman Ahmad posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Abdulkadir Usman Ahmad:

Videos

Share


Other Garun Malam media companies

Show All

You may also like