Da'irar Danmaigauta

Da'irar Danmaigauta Domin yadda abubuwan da s**a shafi addini, da'irar Danmaigauta, da Harkar muslumci a Nigeria.

Shahadat Imam Ali (S)We express our heartfelt condolences on the martyrdom anniversary of Imam Ali (S) to all Muslims an...
01/04/2024

Shahadat Imam Ali (S)

We express our heartfelt condolences on the martyrdom anniversary of Imam Ali (S) to all Muslims and freedom-seekers in the world.

Imam Ali's last will:

أوصِيكُمَا وَ جَمِيعَ وَلَدِي وَ أَهْلِي وَ مَنْ بَلَغَهُ كِتَابِي بِتَقْوَى اَللَّهِ وَ نَظْمِ أَمْرِكُمْ وَ صَلاَحِ ذَاتِ بَيْنِكُمْ فَإِنِّي سَمِعْتُ جَدَّكُمَا (ص) يَقُولُ: صَلاَحُ ذَاتِ اَلْبَيْنِ أَفْضَلُ مِنْ عَامَّةِ اَلصَّلاَةِ وَ اَلصِّيَامِ

English

I advise you both and all my children and members of my family and everyone whom my writing reaches to fear Allah, to keep your affairs in order, and to maintain good relations among yourselves, for I have heard your grandfather the Holy Prophet (S) saying, ‘Improvement of mutual differences is better than general prayers and fasting.’

Hausa

Ina muku wasicci, da kuma dukkan 'ya'yayena da iyalaina da dukkan wanda rubutuna ya isa gare shi, da tsoron Allah da tsara al'amurranku da kuma kyautata alaka tsakaninku, don kuwa naji kakanku Manzon Allah (S) na cewa: "Kyautata Tsakani Yafi Sallah da Azumi."

أعظم الله أجورنا وأجوركم بمصابنا بهدم أركان الهدى! وامصيبتاء! اللهم العن قتلة أمير المؤمنين!





31/03/2034

29/03/2024

Karatun Aƙa'idul Imamiyya darasi na ɗaya tare da Sheikh Usama Aminu Ɗanmaigauta.

A ranar 27 ga watan 7, 1903. Turawan mulkin mallaka na ingila s**a aukawa jama'ar Mbormi, a cikin su akoi Sheikh Dahiru ...
28/03/2024

A ranar 27 ga watan 7, 1903. Turawan mulkin mallaka na ingila s**a aukawa jama'ar Mbormi, a cikin su akoi Sheikh Dahiru Attahiru Wanda shine Sarkin Musulmi na sha biyu (12) a daular usmaniyya. Kuma sun biyo shi Daga sakkwato (Sokoto) bayan sun yi barna a chan sakkwato (barna mai yawan Gaske). Sun kakkashe jama'ar musulmi sunyi amfani da muggan mak**ai (sunyi barna).

Toh kuma sai ya fita Yayi hijira domin ya yafi Madina ya rayu a chan (Shehu Attahiru). Toh sai s**a bishi s**a same shi a nan cikin birnin Mbormi. Mbormi gari ne dama, (akoi Modibbo Jibirilla Wanda shine ya kafa shi).

Sunyi kokarin ganin cewa (su turawan) Sheikh Dahiru Attahiru ya mika masu wuya idan Yayi masu haka zasu maida shi kan sarautar sa sannan su bashi ka'idodi, yace shi bai yadda ba!
Dan haka sai s**a ga abunda za su yi kawai insun bar shi ya tafi, toh k**ar ma ba su nuna sun ci kasar ne da yaki ba! Don haka sai s**a auka masa, s**a yi kisan gilla, sun yi dalan gawarwaki, s**a yi barna mai tsananin Gaske, s**ama kona garin sannan s**a Tara gawarwakin ma guri guda (sai da gawarwakin ya kai tudun beni) bayan haka s**a sa soja hau saman gawanwakin ya caka tutar ingila cikin naman mutum (ya caka a cikin gawawan kin ta tsaya tana filfilawa) sannan ya Daga yatsunsa biyu a matsayin "Victory" (sunyi nasara).

Sannan da s**a sauka s**a sa layi s**a cinnawa gawawankin ma wuta mutane s**a kone su s**a bi "Matching" s**a tafi abun su.

A wurin sun dauki Tutar "La'ilaha ilallah" wadda an gado ta tun zamanin Shehu Usman Bn Fodio. Ko wane shugaba in ya hau Jagoranci sai a dauki Tutar a bashi a dauki Qur'ani a bashi (alamar kenan yanzu shine mai jibintar al'amarin musulmi).
Toh wannan Tuta madaukin ta sai Jarumi, don haka da aka auka masu madaukin wannar Tutar aka harbe shi kanya fado sai wani ya k**a Tutar ya riqe! Shima aka harbe shi a haka sai da aka harbi mutum cesa'in da biyu (92) s**ayi Shahada sannan Tutar ta kwanta a Kansu.
Toh sun dau Tutar sun tafi da ita Lokoja, sun dauki Qur'anin sun tafi da

27/03/2024

Rana irin ta yau 17 ga watan Ramadan, Mu'awuya Bin Abu Safiyan (L) ya kashe matar Manzon Allah (S) Nana Aisha (R.a).

Tun daga wannan ranar aka latsa ƴan arewa aka ji ashe tuɓus tuɓus suke, aka gane ashe sun fi son dabbobin su akan ƴan'uw...
27/03/2024

Tun daga wannan ranar aka latsa ƴan arewa aka ji ashe tuɓus tuɓus suke, aka gane ashe sun fi son dabbobin su akan ƴan'uwan su, aka gano ashe su ɗin ma dabbobi ne masu magana irin ta mutane.

Wannan kisan da sojoji s**ai a Zaria 2015 shine mabudin duk wani kisan mutane da yawa a ƙasar nan k**a daga wanda za'a yi a ce kuskure ne har wanda ƴan ta'adda ke yi wa rufdugu,

To an san ko ma dai bai wuce su yi Allah wadai in abun ya musu zafi in ko akida ta shigo ciki su ce Allah ya ƙara. Allah dai ya dawo da hankalin mai tafiya.!

Adam ibn Muhammad ✍️✍️

TARIHIN IMAM HASSAN AL-MUJTABA BIN ALI (A.S).An haifi Imam Hassan (A.S) ne a ranar 15 ga watan Ramadan, a shekara ta 2 b...
26/03/2024

TARIHIN IMAM HASSAN AL-
MUJTABA BIN ALI (A.S).

An haifi Imam Hassan (A.S) ne a ranar 15 ga watan Ramadan, a shekara ta 2 bayan hijra. Kamar yadda yazo a Tarikhud-dabari, J-2,
sh-537.

Haihuwarsa a wannan rana keda wuya, sai akaje aka kaiwa Annabi (S) albishir din hakan, Manzo yayi farinciki sosai, kuma yazo ya daukeshi ya rungumeshi, sannan yayi kiran Sallah a kunnensa na dama, yayi ik**a a kunnensa na hagu. Sai yace ma Imam Ali (A.S) wane suna ka zaba masa? Sai Imam Ali (A.S) yace; "Ai bai k**ata in gabaceka ba ya Manzon Allah
(S)".

Sai Manzo yace: "Haka nima ba na gabaci Allah (T) ba". Bayan hakan babu dadewa sai ga wahayi daga
Allah na saukowa inda Allah ya sanar da Annabi (S) cewa: "Hakika Allah ya yiwa abin haihuwa mai albarka suna Hasan".

Shi Imam Hasan da ne ga
Amirul-muminina Aliyu dan Abiydalib (A.S), kuma Mahaifiyarsa itace Sayyada Fatimatu 'Yar Manzon Allah (S), shugabar matan talikai (A.S). Cikin siffofin Imam Hasan (A.S) akwai cewa shi, fari ne
a launinsa, kuma yana da yawan gashi, kuma idanunsa Manya-manya ne, masu siffar k**ala da cika, kuma jikinsa cif-cif yake, shi ba
dogo bane, kuma shi ba gajere ba, wato matsakaici ne.

Kuma yana da k**ar Annabawa.
Kuma ya rayu da Kakansa Manzon Allah (S) tsawon shekaru 6-7, ya kuma ruwaito hadisan da yaji daga kakan nashi masu tarin yawan
gaske. Bayan wafatin Kakan nashi, ya zauna zaman takura tare da Mahaifiyarsa (S.A) na tsawon wata biyu da kwana sha biyar (kwana 75),
ta inda dukkan abubuwan da akai mata na cutarwa da muzgunawan da yakai ga doke mata kirjin da yayi
sanadiyar Shahadarta, duk a
kan idonsa ne yana yaro (A.S).

Kuma ya zauna tare da Babansa Imam Ali (A.S), har yayi wafati ya barshi, a inda ya zama magajin babansaKhalifanci da kuma Ilimi da
dukkanin sirrorin da Imam Ali (A.S) ya gada a wajen Manzon Allah (S).Ya kasance mutum mai
biyayya, kuma jami'in
babansa mai da'a, da juriya.
***

#

INALILLAHI WAINNAILAIHI RAJIUN, Da'irar Danmaigauta  TA YI BABAN RASHIN MATASHI MAI SADAUKARWA, GARZALI ƊAYABU Shia Boy ...
26/03/2024

INALILLAHI WAINNAILAIHI RAJIUN, Da'irar Danmaigauta TA YI BABAN RASHIN MATASHI MAI SADAUKARWA, GARZALI ƊAYABU Shia Boy Danmaigauta , MUNA ROƘON ALLAH SWA YA JIƘANSHI YAYIMASA RAHAMA ALBARKACIN ANNABI DA IYALANSA TSARKAKA.

SIRRIN SAMUN SAUYI A KOWACE AL'UMMA..     Kowace al'umma tana samu ko yunƙurin kawo sauyi ne kawai, idan ta cika wasu sh...
24/03/2024

SIRRIN SAMUN SAUYI A KOWACE AL'UMMA..

Kowace al'umma tana samu ko yunƙurin kawo sauyi ne kawai, idan ta cika wasu sharuɗɗa guda uku su nek**ar haka:

1-Sharaɗi na farko: shi ne ya zama wannan al'umma din tana da (Mabda'i ingantacce) ma'ana ya zama tana da wani abu da take komawa zuwa gare shi ingantacce, kuma take ganinshi a matsayin wani abu me tsarki kuma abin girmamawa.

2- Sharaɗi na biyu: ya zama wannan al'umma din ta fahimci wannan mabda'in nata, hakikanin fahimta kuma cikakkiyar fahimta.

3- Sharaɗi na uku: ya zama wannan al'umma din bayan ta fahimci mabda'in, ya zama ta yi imani da mabda'in.

Idan al'umma ta cika wadannan sharuɗɗa to duk lokacin da ta yi yunƙuri domin kawo gyara to babu shakka za ta yi nasara, fiye da haka ma, idan al'umma ta cika wadannan sharuɗɗa ba zai yuwu barna da lalacewa su shiga cikinta har su yi mata tasiri ba.

Don haka Idan muka kalli al'ummarmu ta Nigeria a dunkule za mu ga cewa dukkan waɗannan sharuɗɗa guda uku na samun sauyi mun rasa su, ko kuma mu ce duk wadannan sharuɗɗan an hana mu samunsu, wasu kuma muna da su a can baya amma an yi kokarin raba mu da su. Saboda idan muka kalli sharaɗi na farko "mabda'i" kuma muka kalli Nigeria a dunkule, za mu ga cewa ba a kafa ta a kan wani mabda'i ko wani asasi ba, saboda idan muka koma can baya a tarihi za mu ga cewa al'ummu ne kala biyu ( ýan yankin kudu marasa addini da ýan yankin arewa masu addini) aka dauko su aka gwama aka samar da Nigeria. Don haka babu wani mabda'i da aka ɗora Nigeria a kai, ko aka kafata domin shi, kenan mun rasasharadi na farko tun asali don haka sauran sharuddan ma mun rasa su wato fahimtar mabda'i ko imani da shi, saboda su suna biye masa ne sai ya tabbata za su tabbata.

Wannan nigeria kenan a dunkule, sannan idan muka dawo yankinmu na Arewa, za mu ga cewa mabda'i dai muna da shi, shi kuma mabda’in nan ko dai ya zama addini ko kuma ya zama al’adu da tarihi, kuma dama kakaninmu suna da addinin muslunci, kuma sun yi imani da shi, kuma sun fahimce shi daidai bakin gwargwado. Wannan ma shi ne dalilin da yasa, har s**a iya samar da abin da ake cewa Daular Usman Ɗan fodiyo, Kuma s**a yi nasara. Saboda me? Saboda waɗancan sharuɗɗan sun cika. suna da mabda'i kuma sun fahimce shi dai gwargwado kuma sun yi imani da shi, bari mu kalli fuslkacin addini kafin al’adu da tarihi.

A yau babbar matsalar da take damunmu a yankin arewa da ta sa kullum baya muke ci, kuma muke samun cigaban me shiga rijiya shi ne: tun bayan da aka rusa wancan abin da kakaninmu s**a yi na samar da addini da tsarin musulunci, sai aka shigo mana da tunaninnuka sababbi marasa ma'ana wadanda s**a nisanta mu da al'adunmu da ɗabi'unmu na muslunci.

Na farko, wancan addinin da muke ruko da shi an gurɓata shi, ta hanyar bin duk inda addini yake da tasiri a gurɓata shi, babban abin da aka fara gurbtawa su ne malamai, saboda su ne addini yake a hannunsu, kuma su ne ke faɗa a ji. Sannan kuma aka sanya mana tsarin zaɓo wawaye a matsayin shuwagabanni, kowane wawa wanda be san kansa be san ina aka fito ba b***e inda aka nufa kawai sai ya fito takara ya zama shugabanmu, kuma da wannan wawancin nasa ake amfani wajen shigo da tunaninnuka munana da suke nisantar da mu daga al'adunmu, saboda dama hukuma ita ce take da alhakin lura da wadannan abubuwan.

Don haka sai al'ummarmu ta zama k**ar wata abar farauta ta bangare uku, ɓangaren turawan yamma, da bangaren wawaye shuwaganni, da bangaren makwadaitan malamai, saboda su dai turawa burinsu shi ne kada mu cika waɗancan sharuɗɗa saboda kada mu fita daga ƙangin bautarsu, su kuwa shugabanni abin da ya dame su kawai shi ne me za su samu me za su tara wa iyalansu a kasashen waje?! Don haka kullum sata suke da lalata kasa, a cikin haka kuma sai suke amfani da malami, saboda su turawa sun karanci mutumin Afrika ko Nigeria ta arewa sun gano cewa mutum ne mai son addini da mutunta shi, kuma yana mutunta wanda ya sanya rigar addini a cikin jama'a, sai ya zama shugabani suna amfani da hakan wajen sanya malamai su dinga ba ƴan kasa hakuri, suna tara laifin duk wata barna da rashin cigaba ga Allah (t) da cewa ai Allah ne ya kawo ba shuwaganni bane, wannan shi ne abin da ake ce wa: ( التماهي والتخادم بين علماء الدين والسلطة الحاكمة) "Wato cuɗanni-in-cuɗe ka tsakanin malamai da masu mulki" wannan ne ya sa duk lokacin da wani ya fito domin nuna cewa hukuma ta yi ba daidai ba, ya k**ata a yi mata bore, sai kaji malamai sun dira a kansa sun ce ai haramun ne yi wa hukuma bore, misalan irin haka bayyanannu ne ga duk wani dan Nijeriya a yanzu.

Don haka abin da ke faruwa shi ne malamai sun zama yan siyasa dumu-dumu! Sai ya zama duk wata izza da malami yake da ita an kwace ta hanyar mayar da shi makwadaici ko dan siyasa. Wannan ya sa su da kansu malaman s**a yi watsi da hakikanin manufofin addini s**a cusa kansu cikin siyasoshi, kuma dama addini ne yake da alhakin samar da wadancan sharuddan ta hanyar malamai, saboda su ne ke da alhakin wayar da kan mutane da bas u mafita. Saboda haka sai ya zama an rusa mana mabda'inmu wato addininmu ta hanyar lalata malamai a fakaice, kenan ba mu da mabda'i.
Wannan bisa kaddara cewa addini shi ne zai zama mabda’i kenan!

TARIHINMU DA ADDININMU
Abu na biyu da ya k**ata ya zama mabda'inmu wanda shi ma aka raba mu da shi, shi ne al'adunmu na Hausawa da tarihinmu, kuma duka kiyaye su yana a hannun hukuma ne, amma tunda tunda tsarin da aka sa mana na zabo shugaba wawaye yake tsayar mana a matsayin yan takara kuma shuwaganni, wannan ya sa sam ba su damu ba. saboda yanzu ko jami'o'i ka je kana karanta harshen hausa ko asalin Hausawa za ka ga sam babu wani bayani tak**aimai dangane da hausawa, saboda zantuka ne za ka gani na mutanen yamma suna bayanai masu cin karo da juna dangane da asalin bahaushe ko mutanen arewa, wanda hakan ke son ya bayyana wa ɗalibi ko mai bincike cewa bahaushe fa ba shi da wani asali. Kuma ai ba wai ba mu da tarihin bane, a'a muna da shi, kuma ba wai ba mu da asali bane, a'a muna da shi, sun yi aiki tukuru ne domin lalata shi ta hanyar sanya tarihimu wanda ake karantarwa a makarantu da jami'o'i ya zama duka ra'ayoyi ne da rubuce-rubucen turawa, to ya kake tunani idan ya zama makiyinka shi ne zai rubuta tarihinka?!

Kuma a nan za mu fahimci, zancen nan na hikima da ake cewa: "duk wanda ba shi da jiya, ba shi da yau kuma ba shi da gobe" abin nufi duk wanda ba shi da tarihi mai kyau to fa zamaninsa ma ba zai yi kyau ba, haka gobensa ma. Wannan kuma shi ke kara jefa nigeria cikin mummunan halin da take ciki, musamman yankin arewa, mutumin arewa ba shi da wani abu a yanzu da zai kalla na tarihi da zai yi alfahari da shi. Sawa'un a bangaren addini ko a ɓangaren al'adu, duka an nuna masa cewa ba su da wata kima shi kuma ya amsa ya yarda.

Haka abin yake idan muka kalli al’adunmu su ma an raba da su sai yan wadanda ba a rasa ba, sabod al’adunhausawa yanzu sun zama kauyanci da rashin wayewa acikin al’ummunmu, kuma hakan ya kasance saboda kawo mana sababbin al’adun turawa na zamani.

A bisa wannan, mutanen arewa ba su da mabda'i, ko kuma mu ce suna da mabda'i, amma an lalata shi, an rusa shi kuma an raba su da shi.

To idan ya zama ba mu da mabda'i Kaga ba maganar fahimtarsa, saboda duk abin da babu shi ba za a yi maganar fahimtarsa ko rashin fahimtarsa ba. Kuma duk wata al'umma da bata da mabda'i, to lallai ba fa zata taɓa yin nasara ba, kullum zata ci gaba da lalacewa ne.

A daidai wannan gabar ne Allah ya albarkaci wannan yanki da wani malami mai tunani da zurfin hangen nesa, masanin zamaninsa da addini, Sheikh Ibrahim Al-Zakzaky (H), wanda ya zama shi kullum kiransa shi ne al'ummar wannan yankin ta koma zuwa ga tarihinta, kuma ta koma zuwa ga abin da ta gada, saboda tasirin da hakan yake da shi wajen zaburantarwa da yunkurawar duk wata al'umma zuwa ga cigaba da cin nasara da wayewa.

Don haka sai ya zama shi kullum kiransa shi ne al'ummar wannan yanki ta haɗu wato ta haɗa kanta, ta yi watsi da inda ta samu sãɓãni, amma inda aka haɗu a haɗu a yi aiki tare domin dawo da kimar wannan al'umma, ta hanyar mayar da ita zuwa ga tarihinta, kuma dama tarihin nata shi ne addini, saboda idan aka koma zuwa ga tarihi hakan yana nufin an koma zuwa ga addini ne, idan aka koma zuwa ga addini to hakan yana nufin al'ummar arewa ko Hausawa sun riki mabda'i, idan aka riki mabda'i (addini) kuma aka yi imani da shi, daga nan kuma sai a yi kokarin fahimtarsa. Idan aka fahimci mabda'i, to daga nan ne al'umma zata fara motsi zuwa cigaba.

Kuma lallai wadanda s**a kwace mana waɗancan abubuwa guda uku sun fahimta dakyau haɗarin wannan aikin da wannan shehin malamin (H) ya dauko, saboda in dai ya kai gaci to babu makawa al'umma zata ýantu kuma zata kai zuwa ga inda take burin kaiwa a cigaba da wayewa, kuma saboda haka ne wannan shehin malami ya hadu da abin da yake haduwa da shi har gobe na dauri kala-kala da kashe iyali da rusa gidaje da muhallan addini.

Saboda haka ne s**a yi kokarin bakanta sunansa a idon mazauna wannan yanki ta hanyar bakanta akidar da yake a kai da nuna cewa shi maƙiyi ne ga kasa yana so ya rusa ta!
To Nigeria ce fa, dama ai ba mu muka ƙirƙire ta ba, kuma ba saboda mu aka ƙirƙire ta ba, to sai me in ta rushe? Wannan bisa kaddara cewa abin da suke faɗa gaskiya ne cewa rusa kasa yake son yi. Sai dai a haƙiƙa shi yana so ya kauda abin da turawa s**a kafa ne ya dawo da abin da muka gada na al'adu da addinai, wato abin da yake kokarin kawarwa shi ne lalataccen tsarin da aka kawo domin amfanuwar yahudawa da turawan yamma, sai ya maye gurbinsa da tsarin da zai taimaki mazauna yanki da kasa.

Muhammad Ishaq Ɗanmaigauta

Yarjejeniyar: Dinke baraka tsakanin mazhabobin Musulunci..Doka ta daya:"Musulmai al'umma ce guda daya, suna bauta wa Uba...
23/03/2024

Yarjejeniyar: Dinke baraka tsakanin mazhabobin Musulunci..

Doka ta daya:

"Musulmai al'umma ce guda daya, suna bauta wa Ubangiji daya, suna kuma karanta littafi daya, suna kuma bin Annabi daya, a kuma duk inda suke alkiblarsu daya ce, lallai Allah ya girmama su da sunan Musulunci, a wani bayani da yake a bayyane tamkar bayyanar rana, bai k**ata a sauya shi da waninsa ba, bayan Allah ya zaba mana shi: (Shi ne ya sanya maku suna Musulmai), saboda haka, babu bukatar kowane irin suna, ko sifa da s**a yi kutse, wadanda suke rarraba kawuna ba sa hadawa, suke kuma nesanta al'umma da juna, ba sa kusanto da su.. Banda wadanda suke karfafa da bayyana manhaji, masu karfafa ayyukan Musulunci, su ma din, da sharadin kada su zama an canja sunan Musulunci da su, ko su zama suna gasa da sunan da Allah ya kira mu da shi, k**an yada su a farfajiyar Musulunci, don su kawar da sunan da ya hade mu gaba daya, musamman abubuwan da batattun jam'iyyun da s**a kaurace wa hadin-kan al'umma, da wasu 'yan tsirarun sunaye da wasu tsirarun batattu suke sifantawa".

Taron Makka 2024, a gefen dakin Allah mai alfarma, karkashin kungiyar رابطة العالم الإسلامي

23/03/2024
22/03/2024

Tafseer: Day 16

Suratul Baqara (Aya ta 78—82)

Daga Sayyid Ibrahim ZakzakyH)



10/9/1445 (20/3/2024)

Sayyida Khadija (SA)A zamanin jahiliyya ana kiran Sayyida Khadija (Allah Ya yarda da ita) da Tsarkakakkiya saboda tsanan...
21/03/2024

Sayyida Khadija (SA)

A zamanin jahiliyya ana kiran Sayyida Khadija (Allah Ya yarda da ita) da Tsarkakakkiya saboda tsananin kyawun ɗabi'u da tsaftarta. Haka kuma ana kiranta da Uwargidan matan Quraishawa, ana yi mata laqabi da Umm Hind.

Sayyida Khadija ta rayu da Manzon Allah (SAW) tsawon shekaru ashirin da hudu da watanni. Bai auri kowacce mace ba sai bayan rasuwar ta (Amincin Allah su tabbata a gareta).

Ta kasance daga cikin zaɓaɓɓun matan da Allah Ta’ala ya zaɓa. Daga Imam Ali (SA): Manzon Allah (SAW) ya ce:

إنّ الله اختار من النساء أربعاً: مريم وآسية وخديجة وفاطمة

Ma'ana:

Mafiya ɗaukaka cikin mata su hudu ne: Maryamu, Asiya, Khadija, da Fatima.

Sayyida ta rasu tana ƴar shekara 65 a duniya.

Amincin Allah ya tabbata a gareki ranar da aka haifeki da ranar da ki kayi wafati da kuma ranar da k**e tashi rayayyiya.!

اَلسَّلامُ عَلَيْكِ يا مَنْ سَلَّمَ عَلَيْها جَبْرَئيلُ، وَبلَّغَهَا السَّلامَ مِنَ اللهِ الْجَلِيلِ، فَهَنِيئاً لَكِ بِما أَوْلاكِ اللهُ مِنْ فَضْل، وَالسَّلامُ عَلَيْكِ وَرَحْمَةُ اللهِ وَبَرَكاتُهُ.





10/Ramadan/1445
20/03/2024

20/03/2024

Tafseer: Day 15

Suratul Baqara (Aya ta 74—77)

Daga Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)



9/9/1445 (19/3/2024)

Wafatin Sayyida Khadija Da Abubuwan Da S**a Biyo Baya! Sayyida Khadija uwar gida ce a wajen Muhammad Rasulallah (Saww) k...
20/03/2024

Wafatin Sayyida Khadija Da Abubuwan Da S**a Biyo Baya!

Sayyida Khadija uwar gida ce a wajen Muhammad Rasulallah (Saww) kuma a ranar 10 ga watan Ramadan Allah ya mata rasuwa (Ta Koma Zuwa Ga Allah), shekara 10 bayan ai'ko wato shekara uku kafin hijirar Annabi (Saww) daga Makka zuwa Madina .Ta rasu bayan ɗan rashin lafiya da tayi. Shi zama na jaje yana daga cikin haƙƙoki na Ahlulbait, kuma ya k**ata ya zama muminai su kasance suna farin ciki da farin cikin Ahlulbait sannan suyi bakin ciki da bakin cikin su.

Imam Ja'afar Assadiq (As) Yana cewa; magoya bayan mu yanki ne daga gare mu, (wato Shi'ar mu ɓangare ne gare mu) an halicce su ne da sauran taɓon da aka halicce mu, abin da duk ya ɓata mana rai suma ze ɓata musu! Abin da ya faranta mana rai ze faranta musu.
Kamar yadda muka yi bayani a 10 ga Ramadan, cikin irin wannan shekara ne ita Ummul Muminin Khadijatul Khubra tayi wafati! Bayan Abu Ɗalib ya koma ga Allah da kwana Arba'in da Biyar (45) ita ma Allah ya mata rasuwa!

Ita Sayyida Khadija Manzon Allah (S) ya aure ta a matsayin Budurwa ce ba Bazawara ba Maƙiya ne s**a shigo da shubhat dan su tauye daraja da girma wanda Allah (T) ya bata, Manzon Allah bai auri wata mata ba a lokacin da yake raye ba se bayan Wafatin ta, Sayyida Khadija ita ce ta haifa masa Ƴaƴa ciki harda Sayyida Zahra (As) Shugaban Matan Duniya da Lahira.

Kuma ita Sayyida Khadija ita ce farkon mace wanda ta fara karɓan musulunci, bayan Manzon Allah ya dawo daga kogon Hira da shi da ƙaninsa Amirul Muminin Aliyu (As) ya bayyana mata cewa ga sakon da aka isar mishi ya isar wa Al'umma anan ya kira ta kuma ta amsa masa sakon Alla. Shi kuma Sayyidi Aliyu daman tuntuni shi Musulmi ne ya yi imani da Manzon Allah (S) tun kafin saukar wahayi.
Sayyida Khadija ta taka rawa mai girman gaske a rayuwar Manzon Allah da tarihin musulunci, matace tsayayya jaruma wacce ta taimakawa Manzon Allah akan abin da Allah ya aiko shi akai. Dukiyar ta sadaukar wajen taimakawa Annabi da musulunci.

Ita kaɗaice Allah ya wanzar da zuriyar Manzon Allah ta tsatson ta sune Ahlulbait. Ance lokacin da ta kwanta rashin lafiyar da bata tashi ba, tace Ya Rasulullah ina rokon ka da cewa ka ɗauki wannan zamantakewan aure da muka yi na shekaru in na taƙaita wani haƙƙin ka wanda ban maka ba, ina rokon ka yafe min. Sai Manzon Allah yace Tun da na aure ki ban taba ganin wani abu ba sai Alkhairi daga gare ki, wannan shedane daga Sadiƙul Musaddik Muhammad Rasulillah (S).

Manzon Allah ya ƙara da cewa ban san komai daga gare ki ba sai taimako da jure dukkan cutarwar Maƙiya da s**a mana, kuma kin ba da duniyar ki (Sadaukarwa) gaba ki ɗaya don addinin Allah ya tabbata, don haka ba abin da zan ce sai dai Allah ya saka da Alkhairi. Kuma tun daga nan duniya Manzon Allah ya mata bushara da zai bata makullin aljanna.

Sai Sayyida Khadija tace ya Rasulallah ina ma wasiyya da wannan! Sai ta nuna Sayyida Zahra domin nan da wani lokaci kaɗan zata zama baƙuwa kuma marainiya a baya na, kuma kada wata mata Bakurashiya ta cutar da ita! Kada wani ya doketa kuma kada wani ya ɗaga murya akan ta! kuma bana son taga wani abin bakin ciki tare da ita!!!

Sayyida Khadija Itace farkon mace da ta gasgata Annabi, kuma itace wacce ta fara sallah a bayan Annabi aka yi jam'i da ita, Kuma itace farkon mace da ta jajirce wajen kare Manzon Allah da dukiyarta wajen yaɗa wannan addini da taimakon raunana, Kuma ita ce farkon mace da imanin ta yakai na k**ala, domin k**ar yadda muka yi bayani tana daga cikin mata hudu wanda Manzon Allah yayi bayanin Imanin su kammalalle ne.

Manzon Allah (S) yake cewa: Mazaje da dama sun kammala a imanin su da mutumtaka ɗin su, amma a mata guda huɗu ne s**a samu wannan kammala; Na Farko itace Sayyida Asiya matar Fir'auna, na Biyu itace Sayyida Maryam Mahaifiyar Annabi Isa, na Uku itace Sayyida Khadija matar Annabi, na Huɗu itace Sayyida Fatima (As) ɗiya ga Khadija, Manzon Allah yace wannan mata sun kammala a imanin su kuma sun kammala a mutumtaka ɗin su, sun kammala a kyawawan ɗabi'unsu.

Wani ɓangare daga jawabin Sheikh Adamu Tsoho Jos wanda ya gabatar a ranar 10 ga watan Ramadan shekara 1441/2020 a Hussainiyyatu Sheikh Zakzaky (H) Jos.
Da wannan Jawabin yau Shekaru hudu kenan daidai.

https://t.me/+SnRZ_3Ug4lE4YTky

.

18/03/2024

Tafseer: Day 14

Suratul Baqara (Aya ta 63—73)

Daga Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)



8/9/1445 (18/3/2024)

18/03/2024

Ba muna kiran mutane ne su zo su yi Shi'a ba, Ba rarraba ya dame mu ba.

DOLE MU YARDA DA MUSULUNCIN KOWA. Inji Sheikh Yaƙub Yahaya Katsina.Daga: Hassan Abubakar Ahmad Katsina In kaji Mutum yac...
18/03/2024

DOLE MU YARDA DA MUSULUNCIN KOWA. Inji Sheikh Yaƙub Yahaya Katsina.

Daga: Hassan Abubakar Ahmad Katsina

In kaji Mutum yace mana 'yan Arewa yana nufin mu Musulmi, haka zalika in kaji yace mana Hausa Fulani yana nufin mu Musulmi. Duk ma'anar ɗaya ne, kuma duk lokacin da aka tashi ɗaukar mataki a kanmu, k**ar yanzu wannan abun da yake faruwa na 'yan Kidinafin, da Talauci, tsararren abune da aka tsara domin wannan al'ummar tasu dake wannan yanken na Arewa.

Tsararren abune aka tsara 'yan Siyasa s**a tsara kuma suke zartarwa, amma kaga yafi shafar mu, mu al'ummar Musulmi. Na'am ya shafi wasu wurare ya shafi wasu jama'a, amma yafi shafarmu. Sannan in a kazo zancen Ƙasa babu Addini, in kuma a kace za a yi Ƙasa babu Addini to mu mun koma bayane. Sabodamu Addininmu shi ne abunda za a gani a gane, shi ne Mu, shi ne ɗa'armu, kuma rayuwarmu. Da komi namu.

To in a kazo zancen Ƙasa sai ace banda Addini, a lokaci guda kuma wasu waɗanda ba Addininmu ɗaya ba, su kuma tsarin ya yi masu daidai saboda haka sai su mori tsarkin hankali kwance amma bazasu iya korar Kafurcin ba. Addininmu ya ja mana k**ar yadda suke cewa.

To mai makon mu zauna yadda muke mu dinga yiwa juna kallon daban-daban, k**ar yadda Sayyid Khamene'i Hafizafullah yake cewa: "Kaji Muslimi yana rigima tsakanin riƙe ƙirji a cikin Sallah da rashin riƙe ƙirji, to in maƙiya s**azo hannayen zasu datse baki ɗaya". Da mai riƙon gaban da mai sakin gaban duk datsewa zasuyi, ina ruwan Kafuri.

Sheikh ɗin ya ci gaba da cewa: "Ɗan Allah mu yarda da Musuluncin kowa". In Mutum yace La'illa'wa'illah Muhammadun Rasulullah Sallallahu Alaihi Wa Alihi Wasallam to mu yarda da Musuluncin sa. Muyi haƙuri mu yarda da Musuluncin sa, saboda ko mun koreshi bai koru ba a gurin Allah (Swt). Kuma in anje Lahira bamu da Wutar da zamu sanyashi. Idan ba wanann mukayi ba za a ci gaba da da zaluntarmu. Inji Sheikh ɗin.

Ya ƙara da cewa: "Miye amfanin mu yardar da Musuluncin junanmu"? Da anzo wajena akace man ƴan kaza ba daidai sukeyi ba, ko ba kan daidai suke ba, sai ince mashi k**a gabanka 'yan uwana ne, saboda sun sheda La'illa'wa'illah Muhammadun Rasulullah. Shima in a kazo a kace mashi ɗan Shi'ar nan kaza da kaza shima sai yace k**a gabanka 'yan uwana ne. Tamabya a nan itace, bamu samu ci gaba ba?

Idan kuma maƙiyi ne ya taso mana da makami yan uwanmu bazasu kawo mana gudunmawa da ɗauki ba? In shi aka kawo mawa bazamu kai mashi gudummawa da ɗauki ba? Zamu baiwa juna gudummawa da kuma ɗauki, to ba mun samu ci gaba ba? To mu daure mu yarda da Musuluncin kowa. Mu daina yaudarar ka wukanmu, fassararka ka riƙe ka iya shima yana da irin tashi fassarar, to waye zaiyi mana alƙalanci gobe ƙiyama? Allah. Sai kun gama zage-zage sai anje gobe Ƙiyama ka ganku a Aljanna zaune waje ɗaya kaga ai duk sai kuji kunya ko? Inji Sheikh ɗin.

Ba a na nufin kabar abunda kakeyi kayi na wani ba, a'a ka kaleshi a matsayin Musulmi ɗan uwanka, abunda ake buƙata kenan...

_____Sheikh ɗin ya gabatar da wannan ɗan tsokacin ne a ranar Alhamis 14/March/2024M. A wajen Tafsirin Alqur'ani mai girma zama na Biyar (5) na shekarar 1445H_2024M.

Hassan Ɗan Sister Katsina
Rubutawa 5/Ramadan/1445H.
https://t.me/+rQatVH-ZAdU2NDNk

TAFSEERIN ALKUR'ANI MAI GIRMA DAGA DA'IRAR KADUNA AYAU LAHADI.KADUNA PRESS✍️Yau ma  k**ar kullum, Almajiran Shakih Ibrah...
18/03/2024

TAFSEERIN ALKUR'ANI MAI GIRMA DAGA DA'IRAR KADUNA AYAU LAHADI.

KADUNA PRESS✍️

Yau ma k**ar kullum, Almajiran Shakih Ibraheem Zakzaky (H) na Da'irar Kaduna sun zauna zaman Tafseer.

Wakilin 'Yan uwa na Da'irar, Kaduna Malam Aliyu Umar Tirmizy ne ya gabatar da Tafseerin, inda ya tashi a Aya ta Talatin da takwas cikin Suratul Ahzab

بسم اللّـه الرحمـٰن الرحيم

وإذ تقول للّـذىٓ أنعم ٱلله عليه و أنعمت عليه أمسك عليك و زوجك وٱتّق لله وتخفى فى نفسك ما ٱللـّه مبديه و تخسى ٱلنـّاس وٱللـّه أحق أن تخشـٰه فلمـّا قضـىٰ زيدمّنها وطرًا زوّاجنـٰكها لكى لا يكون على المؤمنين حرجٌ فىٓ أزواج أدعيآءهم إذا قضوا من هنا وطراً وكان أمر ٱلله مفعولاً(٣٧)


Wanda Malamin ya yi Tafseerin Ayoyin har zuwa Aya ta

سنـة ٱللـّه فى ٱلّذىن خلوا من قبل و لن تجد لسنة ٱللـّه تبديلاً(٦٢)

Anyi taron lafiya an kammala lafiya, ga wasu daga cikin hotunan da mu ka dauko a wurin.

KADUNA PRESS✍️
07/08/1445
17/03/2024

Kotu Ta Umurci Hukumar Ƴan Sanda Ta Biya Diyyar Almajiran Sheikh Zakzaky Huɗu Da S**a Yiwa Kisan Gilla A Sakkwato.Daga B...
18/03/2024

Kotu Ta Umurci Hukumar Ƴan Sanda Ta Biya Diyyar Almajiran Sheikh Zakzaky Huɗu Da S**a Yiwa Kisan Gilla A Sakkwato.

Daga Bilal Nasir Umar Sakkwato.

A Yau Litinin 18 ga watan Maris shekara ta 2024 Federal Appeal Court a Sakkwato ta yanke hukuncin kan ƙarar da almajiran Sheikh Ibrahim Yaqoub Alzakzaky (H) na Sakkwato s**a shigar da Hukumar ƴan sanda kan zargin buɗe wuta ga masu muzaharar Ashura a Sakkwato, wanda ya yi sanadiyar rasa rayukan mutane huɗu daga cikin masu muzaharar tare da raunata dadama.

Idan ba a manta ba a ranar Alhamis 19 ga watan Agustan shekara ta 2021 ne dai rundunar ta jami'an ƴan Sanda s**a aukawa masu muzaharar da harbi da harsasai masu rai a daidai lokacin da suke gudanar da jawabin rufe muzaharar da ta shafe sama da awa ɗaya da rabi ana gudarwa lami lafiya, wanda a take s**a kashe mutane Uku Shahid Hassan Abubakar Sakkwato, Shahid Imrana Yabo, Shahid Muhammad Bello Illela, sai kuma Shahid Ali Haidar Boɗinga wanda shima ya yi shahada bayan jinya.

Tun bayan wannan ta'addanci ne dai almajiran Sheikh Zakzaky s**a shigar da hukumar ta ƴan sanda ƙara kan wannan ta'addanci, inda kuma kotun ta sanya ranar sauraren ƙarar tare da bin duk matakai na Shari'a wanda a ƙarshe ta yanke hukuncin a Yau Litinin 18/3/2024.

Kotun ta umurci hukumar ta ƴan sanda da ta biya diyyar mutanen da s**a kashe akan Naira Miliyan 10 kowane mutum ɗaya tare da biyan diyyar masu rauni Naira Miliyan 2 kowane mutum ɗaya, sai kuma ta biya harkar musulunci Naira Miliyan 30 na ɓata mata lokaci da kuma suna da tayi.

18/03/2024

Tafseer: Day 13

Suratul Baqara (Aya ta 57—62)

Daga Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)



7/9/1445 (17/3/2024)

GOBARAR KASUWANNI.Mallam Zakzaky yake cewa ba ku ga kasuwanni ko ina ana ta gobara ba?, Haka kawai gobara sai ta riƙa ci...
18/03/2024

GOBARAR KASUWANNI.
Mallam Zakzaky yake cewa ba ku ga kasuwanni ko ina ana ta gobara ba?, Haka kawai gobara sai ta riƙa cin kasuwanni a Arewa ba? TO ai da gangan ne ake cinna wutar. Wato ala dole sai an gurguntar da tattalin arzikin Mutane kawai!

Mallam ya ƙara da cewa sannan kuma ga “Kidnapping” da ake yi ace a kawo kuɗin fansa, Mutum danginsu su tattaro duk abin da su ke da shi su miƙa!. Wato ala dole sai an gurguntar da tattalin arziƙin Mutane! —Mallam Zakzaky Ranar Juma'a 06/10/1443, 06/05/2023.

Note: Kwanaki biyar baya Gobara a Wuse Market Abuja, Yau kuma Sokoto, Allah ka fahimtar da wannan al’ummar haƙiƙanin masoyinsu Mallam Zakzaky [H].

Ga Wasu Zaɓaɓɓun Zantukan Mallam Zakzaky [H] Guda 14.“Waqar mawaƙi na minti goma tana iya tasiri fiye da tunatarwar Mala...
18/03/2024

Ga Wasu Zaɓaɓɓun Zantukan Mallam Zakzaky [H] Guda 14.

“Waqar mawaƙi na minti goma tana iya tasiri fiye da tunatarwar Malami na shekaru goma”—Shaikh Zakzaky [H].

“Wannan Addini na Musulunci shine mafita gare mu a rayuwar Duniya da Lahira” —Shaikh Zakzaky [H].

“Ka k**a hanyar Allah ƙyam koda zaka yi asarar duk duniyar nan ne”—Shaikh Zakzaky [H].

“Ka sadaukar da kanka da dukiyarka ga wannan Harkar ta tajdidin Musulumci” —Shaikh Zakzaky [H].

“Ka yiwa kanka tarbiyya ta yadda zaka siffantu da sifofin addinin nan a zantukanka da ayyukanka”—Shaikh Zakzaky [H].

“Ka himmatu wajen neman ilimin addini da aiki dashi”—Shaikh Zakzaky [H].

“Kaji tsoron yawo da tsegumi, ka kuma ƙwaɓi mai yin hakan”—Shaikh Zakzaky [H].

“Karka sanya kanka cikin rigingimun Mazhabobi, domin abin daya haɗa mu yafi karfin Mazhaba”—Shaikh Zakzaky [H].

“Karmu ba da’awar mu wata sura ta cewa mu siyasa ce ta dame mu”—Shaikh Zakzaky [H].

“Lalle ne da’awarmu ta zama tana ɗauki ɗai-ɗai ne, ba ta jawo mutane ɗu ba”—Shaikh Zakzaky [H].

“Ya k**ata da’irori su rika tsirowane, amma ba a riƙa kafa su ba, k**ar na ƴan wa’azin ƙasa”—Shaikh Zakzaky [H].

“Ya zama ka shiga wannan harka ne domin tsamar da kanka daga fushin Allah [T] ranar gobe ƙiyama” —Shaikh Zakzaky [H].

“Kar kayi gardama ko ɓata lokaci akan abin da ba zai kai ka ga Aljanna ba, da wannan gwara kai ta Zikiri da Salatin Annabi (S).”— Shaikh Ibraheem Zakzaky (H).

“Duk gidan da aka samu akwai Shahidi, to lalle an girmama gidan ne”—Shaikh Zakzaky [H].

Address

Danmaigauta
Danja

Telephone

+9647840313248

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da'irar Danmaigauta posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Da'irar Danmaigauta:

Videos

Share


Other Danja media companies

Show All