Assada Social media B/kebbi

Assada Social media B/kebbi Masu buqatar ayi musu tallah ko sanar damu labarai da s**a shafi al'ummah kofarmu a bude take. 08130992813

16/02/2022

Labaran Safiyar Laraba 16/02/2022CE - 14/07/1443AH. Cikakkun labarai

Shugaba Buhari ya amince da nadin Muhammad Bello-Koko a matsayin Shugaban Hukumar tasoshin ruwa, NPA.

Kamfanin NNPC ya umurci wuraren tara Mai su rika aiki awa 24.

Kotu ta bai wa Hukumar EFCC damar karbe wasu ƙaddarori da kudinsu ya kai Naira bilyan 3.7

Gwamnatin Tarayya ta dukufa wajen ƙara yawan man fetur da gas da take sayar wa Turai.

Wani matashi ya kashe kansa saboda budurwarsa ta juya masa baya a Kano.

Kwamitin Amaechi ya wanke Hadiza Bala Usman Tsohuwar shugabar Hukumar NPA.

Wahalar man fetur ta sanya 'yan buburuntu suna sayar da lita kan Naira 600.

Wasu bayanai na nuna cewa ƙananan hukumomin Jibiya da Batsari da Safana da suke jihar Katsina na hannun 'yan bindiga.

EPL: Manchester United ta sami nasara a kan Brighton da ci 2:0 a wasan jiya.

UCL: PSG ta sami nasara a kan Real Madrid da ci 1:0 a wasan jiya.

UCL: Manchester City ta sami nasara a kan Sporting CP da ci 5:0 a wasan jiya.

15/02/2022

Labaran Yammacin Talata 15/02/2022CE - 13/07/1443AH. Cikakkun labarai

Shugaba Buhari zai ƙara naira tiriliyan biyu da rabi a kasafin kuɗi don biyan tallafin man fetur.

Alƙaliyar Alƙalai ta Zamfara ta fara bincikar Mataimakin Gwamna Mahdi.

Shugaban ’Yan Sandan Najeriya ya rushe rundunar da Abba Kyari ya jagoranta.

Shugaba Buhari ya tafi Belgium don halartar taron hadin gwiwa kasashen Turai da na afrika a birnin Brussels.

Matafiya sun yi cirko-cirko yayin da karancin man fetur ke ci gaba da ta’azzara a Birnin Tarayya, Abuja.

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 10 tare da halaka mutum daya yayin da s**a kai farmaki tashar jirgin kasa da ke Ajaokuta, Jihar Kogi.

Minista Ali Pantami ya kaddamar da cibiyar fasahar sadarwa ta Muhammadu Buhari a jihar Katsina.

Za a fara toshe asusun bankuna na masu zanga-zangar dokokin korona a Kanada.

Jami'an tsaron Sudan sun harbe 'yan zanga-zanga biyu.

Gwamnatin kasar Ethiophia ta janye dokar ta-bacin da ta sanya a lokacin da 'yan tawayen Tigray s**a yi barazanar shiga birnin Addis Ababa da yaki.

Kotu ta yanke wa wani malami da ya yi wa kananan dalibai 13 fyade, 8 s**a dauki ciki a wata makarantar addini hukuncin daurin rai-da-rai a kasar Indonesiya.

15/02/2022

Labaran Safiyar Talata 15/02/2022CE - 13/07/1443AH. Cikakkun labarai

Hukumar Kwastom ta yi hasashen tara Naira trilyan 3.01 a wannan shekarar.

Gwamnatin jihar Katsina ta haramta ƙungiyoyin 'yan sa-kai a jihar.

Wani makwabci ya hallaka makwabcinsa da tabarya saboda bokitin ruwa a Kaduna.

'Yan bindiga sun yi garkuwa da jami'in kwastam a Zamfara sun buƙaci a ba su Naira milyan 10.

Hukumar tattara haraji a jihar Gombe ta rufe Bankin Access saboda rashin biyan haraji.

'Yan gudun hijira daga ƙasashen Afrika sun koka kan yadda Tunisia ke musguna masu.

Morocco ta bai wa Isra'ila kwangilar samar da mak**ai na Dala milyan 500.

Wata kungiya a Algeria za ta kai Faransa kotun duniya kan diyyar gwajin mak**an nukiliya.

Saudiyya ta lalata kayan aikin Houthi a Ma'aikatar Sadarwa ta Yemen.

Kungiyar kasashen G7 ta ja kunnen Rasha cewa za ta ƙaƙaba mata takunkumai kan Ukraine.

Dan wasan Denmark, Christian Eriksen ya dawo ƙwallo, watanni bayan da ya samu bugun zuciya ana wasa.

REGISTRATION FOR JAMB 2022Ina Dalibbai masu son Rubuta jarabawar JAM! To muna sanar daku insha Allah za'a fara Register ...
15/02/2022

REGISTRATION FOR JAMB 2022

Ina Dalibbai masu son Rubuta jarabawar JAM! To muna sanar daku insha Allah za'a fara Register on 14/2/2022 domin samun code na Profile sai ka shiga wajen messages dinka ka rubuta numbers din NIN number dinka a kula sosai da Capital letter za'a rubuta kuma ana bada space tsakanin NIN da numbers k**ar haka👇

NIN .......... To 55019

Ko kuma👇

NIN .......... To 66019

Daga nan sai a jira na dan lokaci zasu turo profile code din insha Allah muna bada shawara a zabi step two zasufi turo code din wadanda suke cikin Birnin Kebbi zamu sanar daku branch na Registration zuwa ranar juma'a insha Allah domin Neman karin bayani sai a tuntubemu ta wannan number 👇

07040775611 ko pagenmu na facebook👇

14/02/2022

TSAKANIN SU DATTI ASSALAFIY DA ARTIFICIAL KAARUWAI

Abinda Artificial karuwa ta tsana a rayuwarta shine a ambaci karuwanci a tozarta karuwanci a tonawa karuwanci asiri koda ba tare da an ambaci suna ba hankalinsu yana tashi

Ku lura da kyau, su Datti Assalafiy basa k**a sunan wata s**e karuwa ce, wannan ba karantarwan Musulunci bane, duk wanda ya boye zunubinsa to ya zama wajibi a rufa masa asiri

Saboda rufin asiri na Musulunci, an karantar cewa ko wucewa kazoyi sai kaga wasu suna zina to ka nemo wani abu ka musu sutura saboda kar wani yazo wucewa ya gani, don a rufa musu asiri, wannan itace akidarmu

To amma Musulunci ya yadda ayi magana akan miyagun zunnubai wanda ya hada da karuwanci, Luwadi da Madigo domin a tsoratar da al'umma su guji zunubin

Bamu da karfi ko ikon da zamu hana wata karuwanci, k**ar yadda babu wani da yake da iko ya hanamu muzanta karuwanci ba tare da mun ambaci sunan kowa ba, wanda ya tsargu to halinsa ne

Karuwai sun dana mini tarko sosai, ta kowace kofa da hanya farautata suke k**ar yadda 'yan ta'adda da sauran zindikai suke farautata, amma da yake lamarin na Ubangiji ne zasu cigaba da fadi kasa warwas Insha Allah

Mun sani kun fimu karfi, kuna da tasirin da zaku sa manyan 'yan siyasa da manyan sarakuna da manyan jami'an tsaro wadanda suke kwanciya daku kuka ha'incesu kuka dauki hotunansu tsirara kuna tatsar kudadensu, kuna sasu su k**a abokan gabanku su kulle su tozatar dasu, yes, mun sani kunayin haka

To ku sani muma muna da Allah, muna da karfin media, muna da tasirin da zamu dafaku a media da ruwan sanyi

Yaa Allah Ka taimakemu akan gaskiya, Ka tsare mana imaninmu, Ka karemu daga makircin karuwai

JINJINA ZUW GA SARKIN WAKAYanzun nan na kalli bidiyon Naziru Sarkin waka yana bawa masoyansa hakuri cewa a kai zuciya ne...
14/02/2022

JINJINA ZUW GA SARKIN WAKA

Yanzun nan na kalli bidiyon Naziru Sarkin waka yana bawa masoyansa hakuri cewa a kai zuciya nesa ga wadanda suke ta zaginsa don ya fito ya fadi gaskiya

Sannan ya bawa Ladin Cima kyautar kudi Naira Miliyan 2 domin ta kula da kanta tunda yanzu 'yan Kannywood ba zasu sake sakata a shirin fim ba, kuma yace zai cigaba da taimakonta

Sannan akwai wata jarumar Kannywood mai suna Fati Slow wanda tayi bidiyo tace Naziru Sarkin Waka ya rantse da Allah shima bai taba danne wata 'yar Kannywood ba, to Naziru yace ya barta da Allah, kuma itama yayi alkawarin zai bata kudi Naira Miliyan daya ta k**a sana'a

Gaskiya na jinjinawa Naziru Sarkin Waka, kuma ba shakka yafi 'yan Kannywood gaskiya

Allah Ka saka masa da alheri

NEMAN KUJERAN SIYASA BAI HANASHI ZUWA HIDIMAN QUR'ANI BAKamar yadda na kawo bayani dazu da safe akan Alaramma Gwani Muha...
14/02/2022

NEMAN KUJERAN SIYASA BAI HANASHI ZUWA HIDIMAN QUR'ANI BA

Kamar yadda na kawo bayani dazu da safe akan Alaramma Gwani Muhammad Adam Alkali OON wanda ya fito takaran kujeran dan majalisar tarayya a mazabar Jos North da Bassa jihar Pilato karkashin jam'iyyar PRP

Yau saura kwanaki 17 ayi zaben cike gurbi bayan rasuwar dan majalisar tarayya na yankin, yanzu zaben zai gudana ne tsakanin Musulmi da wanda ba Musulmi ba a mazabar da Musulmai ke da yawan al'umma da kaso 90 cikin 100, sai dai dan takaran na jam'iyyar APC wanda ba Musulmi ba yana tare da goyon bayan Gwamnati dari bisa dari

Don haka muke sanar da al'umma halin da ake ciki, ku taimaka mana da addu'ah ma'aocin Qur'ani ya samu nasara, Wallahi nasaran wannan bawan Allah nasaran Musulunci ne da Musulmai

Hoto na farko, Gwani Muhammad ne tare da daliban Qur'ani dazun nan bayan an kammala gasar karatun Al-Qur'ani Maigirma a matakin jihar Pilato, hidiman siyasa bai hanashi zuwa hidiman Qur'ani ba

Muna rokon addu'ah daga bakunan 'yan uwa Musulmai a duk inda kuke, ku yiwa Gwani Muhammad fatan nasara

Muna rokon Allah Ya tabbatar masa da nasara Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum

NIGERIA KENANBatun Sarkin Yakin Nigeria DCP Abba Kyari da hukumar NDLEA ba tun yau na samu labarin abinda ya faru ba, ma...
14/02/2022

NIGERIA KENAN

Batun Sarkin Yakin Nigeria DCP Abba Kyari da hukumar NDLEA ba tun yau na samu labarin abinda ya faru ba, mataimakinsa ACP Sunny Obua hukumar NDLEA ta fara kaiwa kara gurin IGP wanda yanzu haka yana tsare, me yasa basu saka sunan ACP Sunny Obua cikin wanted ba da press release dinsu akan wannan batu ba sai Abba Kyari kadai?

Mai yasa NDLEA sai a wannan lokaci s**a fitar da wannan zargi akan DCP Abba Kyari a daidai lokacin da ake shirin dawo dashi bakin aiki bayan hukumar kula da aikin 'yan sanda ta tabbar da cewa ba'a samu Abba Kyari da laifin karban cin hanci a gurin Hushpuppi ba?

Baya cikin doka da ka'ida hukumar NDLEA ta ayyana wani jimi'in tsaro matsayin wanted, sun san ofishin Maigirma Shugaban 'yan sanda IGP, idan sun nemi Abba Kyari ya kawo kansa yaki to gurin IGP zasu je su sanar dashi tunda sun san hanyar ofishin IGP, amma sai s**ayi declaring nashi wanted a media saboda akwai wata manufa ta karkashin kasa

Batun bidiyo da yake yawo akwai editing da yawa a cikinsa, sai an samu forensic pixel analysis akan bidiyon kafin a gaskata sahihancinsa a kotu

Matsayar Datti Assalafiy akan wannan batu; da DCP Abba Kyari da jami'in NDLEA da ya tsara wannan abin kowa abin zargi ne, sai wanda bincike na gaskiya ya tsarkake shi, bama bayan kowa anan, muna bayan gaskiya ne

Muna rokon Allah Ya tabbatar da gaskiya da adalci akan wannan batu

MAKIYA DA MAHASSADA SUN DIRA KAN MALAMKungiyar Malaman jami'o'in Nigeria ASUU sun nemi da a cire mukamin Professor da wa...
14/02/2022

MAKIYA DA MAHASSADA SUN DIRA KAN MALAM

Kungiyar Malaman jami'o'in Nigeria ASUU sun nemi da a cire mukamin Professor da wata jami'ar Tarayya ta bawa Maigirma Ministan Sadarwa Sheikh Professor Isa Ali Pantami

A sanina tun da aka kafa tarihin Nigeria babu wani mutum da aka nuna masa bakar hassada da kiyayya don ya samu mukamin Professor k**ar Malam Isa Ali Pantami

A zahiri idan akwai wani matakin ilmi da ya wuce mukamin Professor Wallahi Malam Isa Ali Pantami ya cancanta a bashi

Imbanda Nigeria hadin gambiza ce, wai ace mutumin da ya haddace mafi girman Littafi (Al-Qur'ani) wanda ya tattara dukkan ilmi na sammai bakwai da kassai bakwai, ya haddace haddisai, kuma yayi karatun boko har matakin digiri na uku ace wai bai cancani mukamin Professor ba?

Kaf cikin Professors da ake da su a Nigeria waye idan ya zauna a gaban Malam Isa Ali Pantami ba zai karantar da shi ilmi ba?

Ba komai, suna yakarsa ne kawai saboda yana kusantuwa zuwa ga Malamin addinin Musulunci, ya samu ni'ima ta rayuwa irin wanda basu samu ba

Zamu cigaba da kiran Malam Isa Ali Pantami da sunan Professor har abada, idan an isa a mayar damu cikin iyayen mu

Allah Ka daukaka darajar Malam Isa Ali Pantami

RASHIN IMANI NE KO RASHIN SANIN CIWON KAI???✍️✍️✍️✍️✍️Daga-Zubairu Ibrahim AssadaA kwanan nan duk wanda ke bibiyar media...
18/05/2021

RASHIN IMANI NE KO RASHIN SANIN CIWON KAI???

✍️✍️✍️✍️✍️
Daga-Zubairu Ibrahim Assada

A kwanan nan duk wanda ke bibiyar media yana gani yadda Yahudawan kasar Isra'ila ke kaddamar da harin ta'addanci na ruwan wuta ga 'yan uwanmu musulmai na falasdin kuma harin ma na rashin imani mai kan uwa da wabi babba da yaro mata da tsofaffi kowa basa dagawa kafa kuma majalisar dinkin Duniya na kallon abinda ke faruwa amma saboda shafaffu ne da mai anrasa mai taka musu birki sai karensu suke ci ba babbaka saboda samun daurin gindi, amma duk da haka na mutanen kirki basa karewa domin naga wasu daga cikin kasashen musulmai sun fito sun kalubalanci wannan zalunci baya ga haka da idona naga babban malamin musulunci a Nigeria Sheikh Musa Yusuf Asadus-Sunnah ya fito yayi fata fata dasu ba tare da tsoron komai ba wanda haka ake so idan matsala na tunkarar musulmai da musulunci 'yan uwansu su fito su bada kariya muna kara kira ga shugabanninmu na musulmai na Duniya su fito su nuna bara'arsu tare da bada kariya ga jinin musulmai da ake zubarwa har wayau malaman addini ku fito kuyi magana sautinku ya rakade duniya kuna bara'a da Allah wadai ga wannan zalunci Talakawa manyanmu da kanananmu mu dukufa ka'in da na'in da addu'o'I ubangiji ya tarwatsa shirin wadannan Azzalumai na neman Ruguza musulunci a karshe muna kira ga limaman juma'a dana khamsus-Swalawat ku sanya kasar falastin cikin Alqunut ubangiji Allah ya yaye mana wannan bala'I ya basu kariya da kansa daga sharrin masu sharri ya Rabbal Alameeeen👏👏👏

02/04/2021
15/10/2020

Assalamu Alaikum yaku ma'abota wannan PAGE namu mai albarka muna sanar daku cewa akwai wani tsarin Debate da zamu fara gabatarwa ga members dinmu da s**ayi LIKE na wannan PAGE namu domin wasa kwakwalwa da kuma Kara fadada ilimin juna juna, wannan DEBATE zai kunshi tambayoyi goma sha biyu a fannoni guda uku na ilimi 👇

1. Alqur'ani (mai girma) Tambaya hudu.

2. Tauheed Tambaya hudu

3. Sirah Tambaya hudu

Debate din zai riqa zuwa muku a ko wace ranar Juma'a da misalin karfe uku na yammah 3:00pm Kuma duk wanda yayi nasara Insha Allah zamu dauki sunansa da hotonsa muyi posting a wannan PAGE a matsayin gwarzon juma'a zamuyi masa addu'a tare da neman addu'ar jama'a zuwa gareshi domin Allah ya haskaka Rayuwarshi da ahalinshi baki daya zuwa gaba zamu riqa bada kyauta insha Allah ga duk wanda yayi nasara, muna fata Allah yasa wannan hanya ta zamo sanadin Shiryuwar mutane da yawa har su koma makaranta domin kasancewa ahalin ilimi Ameeen.

Saboda haka wanna Debate zai riqa zuwa muku iya wannan Page na MADARASATU SHEIKH DR MH'D KABIR GOMBE BK idan bakayi Like na Page dinmu ba muna sanar dakai kayi gaggawar yin Like domin hakan ne zai baka damar ganin postng dinmu har ka zamo daya daga cikin wadanda za'a fafata dasu kuma Insha Allah gobe Juma'a zamu fara wannan Debate Allah ya tashemu lfya Ameeee.

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya yi kira ga sarkin Kano, Aminu Ado-Bayero, da ya yi amfani da kujerarsa wurin ...
10/08/2020

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya yi kira ga sarkin Kano, Aminu Ado-Bayero, da ya yi amfani da kujerarsa wurin assasa hadin kai na yankin arewacin kasar nan.
Ka yi amfani da kujerarka wurin kawo hadin kan arewa - Matawalle ga Sarkin Kano

WATA BUDURWA TA KASHE ALMAJIRAI, SABO DA YA RABASU FADAWani babban lamari mai cike da Tausayi yafa faru a Garin Yawuri d...
10/08/2020

WATA BUDURWA TA KASHE ALMAJIRAI, SABO DA YA RABASU FADA

Wani babban lamari mai cike da Tausayi yafa faru a Garin Yawuri dake Jihar Kebbi, Inda wata Yarinya Budurwa Suke fada a tsakanin ta da wata Budurwar, Sai Wani Dattijo dake Zaune a Gefe ya hangi Almajirin zai wuce ya kira shi, yace "Yaro(almajiri),je ka raba wayancen Yara Matan fada"
Nan take shi kuma almajirin ya nufi wurin da 'Yan matannan ke baiwa hammata Iska, koda zuwansa ashe qarar kwana ke kiransa Inda daya daga cikin wayanan 'Yan Matan da suke fada ta Burma masa (wannan aljirin) Wuka Aciki Sabo da ya zo raba su fadan da sukeyi

Labaran Yammacin Alhamis 30/07/2020CE - 09/12/1441AH. Cikakkun labaran DuniyaGwamna Zulum na jihar Borno ya nuna fushins...
30/07/2020

Labaran Yammacin Alhamis 30/07/2020CE - 09/12/1441AH. Cikakkun labaran Duniya

Gwamna Zulum na jihar Borno ya nuna fushinsa ga sojoji game da harin da aka kai wa tawagarsa bayan sun nuna kwace garin.

'Yan majalisar wakilai sun ce akwai yiwuwar za a kai sababbin hare-hare a kudancin Kaduna lokacin bukukuwan Sallah.

Sarkin Katsina, Abdulmumin Kabir ya ce kwanan shi biyar bai Yi bacci ba saboda halin da Katsina ke ciki na rashin tsaro.

Gwamantin jihar Kano za ta gina layin dogo mai amfani da wutar lantarki.

Wani Kamfanin wutar lantark na Siemens da ke Jamus zai fara aikin samar da 25, 000MW a Najeriya.

Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi kira a jinkirta zaben shugaban kasar.

Majalisar dinkin duniya ta ce kashi biyu cikin uku na 'yan Zimbabwe za su nemi tallafin abinci zuwa karshen 2020.

Shugaban kasar Egypt, Abdel Fattah al-Sisi ya sanya a sabuwar dokar da ta hana sojoji a kasar shiga harkokin siyasa.

Jami'an gwamnatin Amurka sun ziyarci Masallacin Juma'a na Hagia Sophia.

Dakarun sojin Azabaijan sun harbo jirgin sama mara matuki mallakar Armeniya.
Kungiyar Manchester City ta sayi Nathan Ake kan £40m daga Bournemouth.

Mai son labaran Duniya na safiya da yammah ya biyomu a shafinmu na Facebook yayi Like👇
https://www.facebook.com/100368468346032/posts/149439960105549/?flite=scwspnss&extid=KSI6OWYtyucnHUUx

30/07/2020

Labaran Yammacin Alhamis 30/07/2020CE - 09/12/1441AH. Cikakkun labaran Duniya
Gwamna Zulum na jihar Borno ya nuna fushinsa ga sojoji game da harin da aka kai wa tawagarsa bayan sun nuna kwace garin.
'Yan majalisar wakilai sun ce akwai yiwuwar za a kai sababbin hare-hare a kudancin Kaduna lokacin bukukuwan Sallah.
Sarkin Katsina, Abdulmumin Kabir ya ce kwanan shi biyar bai Yi bacci ba saboda halin da Katsina ke ciki na rashin tsaro.
Gwamantin jihar Kano za ta gina layin dogo mai amfani da wutar lantarki.
Wani Kamfanin wutar lantark na Siemens da ke Jamus zai fara aikin samar da 25, 000MW a Najeriya.
Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi kira a jinkirta zaben shugaban kasar.
Majalisar dinkin duniya ta ce kashi biyu cikin uku na 'yan Zimbabwe za su nemi tallafin abinci zuwa karshen 2020.
Shugaban kasar Egypt, Abdel Fattah al-Sisi ya sanya a sabuwar dokar da ta hana sojoji a kasar shiga harkokin siyasa.
Jami'an gwamnatin Amurka sun ziyarci Masallacin Juma'a na Hagia Sophia.
Dakarun sojin Azabaijan sun harbo jirgin sama mara matuki mallakar Armeniya.
Kungiyar Manchester City ta sayi Nathan Ake kan £40m daga Bournemouth.

Innalillahi Wa Inna Ilaihi RajiunWasu tagwayen Bama-bamai sun tashi a Maiduguri, inda ake kyautata zaton mutuwar mutane ...
30/07/2020

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun
Wasu tagwayen Bama-bamai sun tashi a Maiduguri, inda ake kyautata zaton mutuwar mutane da dama.
Lamarin dai ya auku da yammacin yau Alhamis a Gunge da tsakayiyar gidajen al'umma da Mairi da kuma yankin Custom dukkansu a cikin garin Maidugurin.
Allah ya kawo mana karshen wannan bala'in.

Address

Badariya Birnin Kebbi
Birnin-Kebbi

Telephone

+2348130992813

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Assada Social media B/kebbi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Assada Social media B/kebbi:

Videos

Share