Islamic Online TV

  • Home
  • Islamic Online TV

Islamic Online TV Wannan shafi an kirkiro shine saboda yada addinin Allah musulunci, bamu da wani aiki daya wuce wannan Media/News/Publishing

An shirya birnin masallacin Annabi da ke Madina tsaf bayan kammala aikin Hajjin bana domin karɓar Alhazai masu ziyara wa...
10/06/2025

An shirya birnin masallacin Annabi da ke Madina tsaf bayan kammala aikin Hajjin bana domin karɓar Alhazai masu ziyara waɗanda ba su samu yi ba kafin fara aikin Hajji.

Kafin in yi aure, ina kashe kamar awa 10 wajen da'awa a kowacce rana.Sai mutane suke ce mun idan ka yi aure ba za ka din...
10/06/2025

Kafin in yi aure, ina kashe kamar awa 10 wajen da'awa a kowacce rana.

Sai mutane suke ce mun idan ka yi aure ba za ka dinga samun damar yin da'awa na awa 10 a rana ba.

Sai na auri 'yar da'awa

Sai na zama ina da'awa na awa 12 a rana.

Dr Zakir Naik (Hafizahullah).

Tarihin Bajimin Shehin Malami Na Duniya Baki Daya.Zakir Naik ɗan asalin Indiya ne, an haife shi ranar 18 ga Oktoba, 1965...
10/06/2025

Tarihin Bajimin Shehin Malami Na Duniya Baki Daya.

Zakir Naik ɗan asalin Indiya ne, an haife shi ranar 18 ga Oktoba, 1965 a birnin Mumbai. Ya kammala karatun likita (MBBS) daga jami'ar Mumbai, amma bai yi aiki a fannin likitanci ba, sai ya mai da hankali wajen koyar da addinin Musulunci da fadakarwa ta hanyar jawabi da hulɗa da addinai daban-daban.

A farkon shekarun 1980, Zakir Naik ya haɗu da Ahmed Deedat, wani shahararren malamin addinin Musulunci daga Afirka ta Kudu, wanda hakan ya ba shi ƙwarin gwiwa ya fara wa’azi da koyarwa. Tun daga lokacin ne ya fara yin jawabai na ilimantarwa game da bambance-bambancen addinai, da kuma nuna alakar ilmin kimiyya da addinin Musulunci.

Zakir Naik ya kafa wata ƙungiya mai suna Islamic Research Foundation (IRF), wadda take shirya tarurruka, kuma shi ne shugaban tashar talabijin ta Peace TV, inda yake watsa shirye-shiryensa na wa’azi da muhawara ta addini.

Amma duk da wannan aiki nasa, Zakir Naik ya shiga cikin wasu rikice-rikice. A wasu ƙasashe, an zarge shi da fadin maganganu da ake ganin suna kawo rabuwar kai ko kuma tashin hankali, wanda ya sa aka haramta tashar Peace TV a wurare da dama kamar Indiya, Kanada, da Birtaniya. Haka kuma, an tuhume shi da wasu laifuka a Indiya, ciki har da laifin zamba da bada gudummawar kuɗaɗe ba bisa ka’ida ba.

A yanzu haka, Zakir Naik yana zaune a Malaysia inda yake ci gaba da wa’azantar da al’umma ta hanyar yanar gizo da talabijin. Ya shahara musamman a tsakanin Musulmai saboda iliminsa, kwarjinin jawaban sa, da kuma irin muhawararsa da malaman addinai daban-daban.
Allah ka taimaki Addinin ka da masu taimakon sa.
Gass Ne Wlh ✍️

Hotuna daga Taron Bayan Arfa da ake gudanarwa a yau, 10 ga Yuni, 2025, a birnin Makkah, Saudiyya, tsakanin shugabannin N...
10/06/2025

Hotuna daga Taron Bayan Arfa da ake gudanarwa a yau, 10 ga Yuni, 2025, a birnin Makkah, Saudiyya, tsakanin shugabannin NAHCON, jami'an hukumomin jin dadin Alhazai na jihohi, da sauran masu ruwa da tsaki a sha’anin aikin Hajji.

Taron ya samu halartar manyan shugabanni daga NAHCON, wakilan hukumomin jin dadin Alhazai daga sassa daban-daban na kasar, tare da sauran masu ruwa da tsaki.

Ana gudanar da irin wannan taro a kowace shekara domin duba abubuwan da aka cimma da kalubalen da aka fuskanta a aikin Hajjin da ya gabata, tare da tsara matakan ingantawa da kyautata tsare-tsare a gaba.

10/06/2025

Lalle Dr Tauhid ba wasa bane, a wajen mukabala da yan bid'a da mush-rikai. Allah yaji kan Dr Idris 😭.

❤❤❤
10/06/2025

❤❤❤

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya halarci bikin rufe aikin Hajji na shekarar 2025/1446H da aka gudanar ...
09/06/2025

Shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya halarci bikin rufe aikin Hajji na shekarar 2025/1446H da aka gudanar a birnin Makkah, inda Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya, Dr. Tawfiq Al-Rabiah, ya sanar da fara shirye shiryen aikin Hajji na shekarar 2026/1447H.

A yayin bikin raba kyaututtuka na Labbaitum da aka karrama manyan masu ruwa da tsaki, Ministan ya jaddada aniyar kasar Saudiyya na ci gaba da inganta aikin Hajji da samar da kwarewa mai inganci ga ‘Baƙin Allah’. Ya kuma yaba da nasarorin da aka samu a Hajjin 2025, yana mai cewa shiri da tsari tun da wuri shi ne mabuɗin nasara.

NAHCON ta bayyana kudurinta na ci gaba da aiki da hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki a Najeriya domin ganin an shirya Hajjin 2026 cikin lokaci. Tuni hukumomin Saudiyya s**a fitar da takardar izinin fara shirye-shirye ga kowace kasa, ciki har da amincewa da fara tattaunawa da masu ba da sabis na masauki, abinci, sufuri da jiragen sama.

09/06/2025

Kur'ani hasken Rayuwa. ❤❤❤

09/06/2025

Idan akace maka yan shi'ah ba musulmai bane baka yarda, ka duba yanda suke sallah a addinin su. 🤔

Wallahi Hawaye Naji Ya Zubomin 😭Lokacin da Shugaban Hukumar NAHCON yake zagayawa Kaimomin Alhazai a Minna domin tabbatar...
09/06/2025

Wallahi Hawaye Naji Ya Zubomin 😭

Lokacin da Shugaban Hukumar NAHCON yake zagayawa Kaimomin Alhazai a Minna domin tabbatar da komai yana Tafiya Dai-dai,

Duk inda ya shiga duk layin daya biyo sai kaga Jama'a sun taso sun tare shi suna Godiya suna cewa mun gode Wallahi bakaci Amana bamu da korafin komai Alhamdulillah

Wallahi ko ina sai tonfin Alkairi ake masa akece mun gode bamu da Korafi wajan komai, wannan sautin ne yake tashi Wallahi Malam bakaci Amana.

Duk inda mukaje yabo da Godiya ake yiwa Malam saboda farin ciki sai kawai naji Kwalla tana Zubomin daga idona 😭

Tabbas wannan nasarar daga Allah take.

Abdullahi Suraj Nagegime

Nan da 2050 ba za a sake yin aikin Hajji cikin tsananin zafi ba - NCMHussein Al Qahtani, mai magana da yawun Cibiyar Kul...
09/06/2025

Nan da 2050 ba za a sake yin aikin Hajji cikin tsananin zafi ba - NCM

Hussein Al Qahtani, mai magana da yawun Cibiyar Kula da Yanayi ta Ƙasar Saudiya (NCM), ya bayyana cewa Hajjin bana zai kasance na ƙarshe da za a yi shi a cikin zafi na lokacin bazara.

Ya ce daga 2026, aikin Hajji zai fara komawa cikin lokutan da yanayin su ya fi sauƙi — kamar lokacin iska lokacin sanyi , da lokacin damina — waɗanda za su bayar da yanayi mai daɗi ga miliyoyin masu ibada a kowace shekara.

Mai magana da yawun ya bayyana cewa nan guda takwas masu zuwa hajji Masu zuwa za su faru a lokacin bazara, sannan hajjoji guda takwas masu biyo baya a lokacin sanyi, kafin su shiga lokacin damina inda zafin rana zai fara ƙaruwa a hankali, kafin a koma lokacin bazara (zafi) bayan kusan shekaru 25.

Al Qahtani ya ce wannan canji yana faruwa ne saboda juyin da kalandar Musulunci ta wata (Hijri) ke yi, wanda ke baiwa masu niyyar Hajji damar gudanar da ibada a yanayi mafi sauƙi a shekaru masu zuwa.

NCM ta fitar da kalandar Hajji na tsawon shekaru 25 da ke bayyana yadda ranakun Hajji — bisa ga kalandar Hijri — za su yi daidaito da lokutan shekara na kalandar Gregorian har zuwa shekara ta 2050.

Saboda yanayin kalandar Hijri wanda ke da kusan kwanaki 11 kasa da na kalandar Gregorian, ana samun canji na lokacin Hajji zuwa gaba da kusan sati daya a kowace shekara.

Ya ce masu gudanar da Hajji ba za su sake fuskantar zafin rana mai tsanani ba har sai bayan shekaru 25 masu zuwa.

Al Qahtani ya ƙara da cewa za a samu yanayi mai daɗi sosai ga mahajjata har sai Hajji ya dawo cikin lokacin zafi a shekara ta 2050.

Address


Telephone

+2348038723868

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Islamic Online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Islamic Online TV:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share