Jawaban Sheikh Zakzaky

Jawaban Sheikh Zakzaky Insha Allah zamu na kawo muku jawaban Jagora Sayyid Zakzaky (H) na Dakuma yazu

Update Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) met with brothers and sisters of the islamic movement who are studying at vari...
20/01/2024

Update

Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) met with brothers and sisters of the islamic movement who are studying at various universities in Iran.



19/01/2024

Hausa

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya gana da yan uwa na harka Islamiyya dake Karatu a Jami’o'i daban daban a Iran.



19/01/2024

BANGAREN JAWABIN JAGORA SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) DANGANE DA ‘PASSPORT’ DINSU DA AKA BASUDa yake ganawa da ba’adin ‘ya...
03/10/2023

BANGAREN JAWABIN JAGORA SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) DANGANE DA ‘PASSPORT’ DINSU DA AKA BASU

Da yake ganawa da ba’adin ‘yan uwa Musulmi a ranar Mauludin Manzon Allah (S) -17 ga Rabi’ul Auwal 1445 (2/10/2023)- a gidansa da ke Abuja, Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya ambata cewa:

“Kuma na so in muku wani albishir da cewa, ainihin ‘Passport’ din nan da aka yi ta fafutukar a samu, to dai yanzu yana hannu. A karshe, su da kansu s**a zo nan har gida s**a dauki hotuna da duk abubuwan da ake bukata wanda akan yi a ofis din, sun zo har gida s**a yi mana, kuma s**a aiko da Fasfo din, insha Allah.

“Saboda haka yanzu muna ‘yan shirye-shirye ne na k**a hanya, mun shirya da asibitocin da za mu je, da kuma likitocin da za su yi aikace-aikace, saboda haka ba da jimawa ba, insha Allahu za a dan ji mun dan fita. Insha Allah.

“To, muna godiya Allah Ta’ala, da kuma sadaukarwar ‘yan uwa da yawan gaske. Na ji wadansu har suna surutai, wani yana cewa, wai ‘yan Shi’a a kan Passport takardar banza wai su sun yi shahada. Nace, ba kan passport s**a yi Shahada ba, ‘Fisabilillahi’ s**a yi. Su wadanda s**a ga taron, haushin da suke ji shi ne, duk wani abu da yake bayyana izzar addinin nan tsoro yake basu. Koma wane iri ne. Shi yasa kaga suke adawa da duk wani abu. Suna son kowa ya yi shiru ne.

“Mauludin nan suna son kowa ya yi zamansa a gida ne, yace yana son Annabi (S) a zuciyarsa. Da zaran an fito, to ya nuna izzar addini, kuma haushi suke ji. To duk wani lokaci da s**a ga kuma abin da ya shafi Harkar nan, in dai s**a ganshi a bayyane, haushi suke ji. Shi yasa su kuma ‘yan uwa ko da wane lokaci akan samu wani dalili da zai sa ko da wane lokaci a rika nuna izza din, don fitowar namu izzar ce.

“Idi ainihin an yi shi ne don nuna izza shi ma, don haka aka koyar da mu cewa, a taru ne a tsakiyar gari, a fita ta hanya guda ana Azkar, in an gama Idin a dawo ta wata hanya tadaban, ba wadda aka fita zuwa Idin ba, sannan a sake haduwa a tsakiyar garin inda aka fara, sannan kowa ya k**a hanyar gida. To, da za a yi haka nan a gari guda, ace a hadu duk guri daya, kuma a dawo ta wata hanya daban. Haba! Ai ka ga zai nuna izzar wannan al’ummar.

“To, haka nan duk abin da s**a ga muke yi, wanda yake nuna martaban iyalan gidan Annabi (S) haushi yake basu ai. Mauludi yana nuna son Annabi (S) ne, sauran ‘Marasim’ na A’imma (AS) yana nuna ana raya abin da ya shafi iyalan gidan Annabi (S) din ne, don haka kowanne yana basu haushi. Suna jin haushin Ashura, suna jin haushi Mawalid da muke yi na A’imma (AS), duk wani taro namu, kai ko mene ne namu ma.

“Saboda haka, babu wani wanda ya yi shahada kan wani abu ‘in particular’. Alal misali, wanda aka kashe ranar Quds, ba za ka ce musu sun yi Shahadar Quds ba, Fisabilillahi s**a yi. Wanda aka kashe ranar Ashura, ba sunansa Shahadar Ashura ba, sunansa Shahada Fisabilillahi. Wanda aka kashe ko ma a kan mene ne, in dai an kashe shi a kan ‘manifestation’ na addini ne, to saboda addini ne. Shi ma cewa, lallai a sakar mana fasfuna dinmu, ya nuna cewa an samu wadansu mutane da su ba su yarda a zalunce su ba. Suna neman hakkinsu ta kowane hali. Kuma abin da basu so kenan, suna son a yi musu shiru ne kar a ce komai. Yauwa.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa: “wannan alama ce da ke nuna mutane (da s**a rika Muzaharori) sun yi ne saboda nuna izzar addini, kuma haqa ta cimma ruwa insha Allahul Azeem.”

Sannan ya kuma mika godiyarsa ga Allah (T) da cewa: “Kuma mun godewa Allah Ta’ala, duk da mun zauna da rashin lafiyar da ga yadda aka saba bisa dabi’a Dan Adam ba zai yiwu ya rayu da irin wannan rashin lafiyar ba, amma kuma da yake Allah ne mai rayawa, sai ya raya mu haka nan din.”

Yace: “Amma duk da haka dai da lalurori, musamman kuna iya ganin Malama yadda take takarkarowa babu kafa, tun 2016, yau shekara bakwai cur tana sallah a kujera ne, to amma kuma haka nan, yana dada tabarbarewa ne al’amarin guiwan nata, ba don kiyayewar Allah ba.”

Yace: “Mun yi sa’a, lokacin da aka kai mu ‘prison’ na yi ta jin tsoron kar abin ya taso mata, don takan yi k**ar ba za ta yi rai ba (idan ya tashin), to sai kuma dai bai taso ba sam har izuwa ma fitowar mu din nan, bai sake tasowa ba, amma ya rika tasowa (lokacin) muna tsare a hannun DSS. Har ma a Kaduna (lokacin ana wajen DSS) ya taso ya yi tsanani sosai. To dai kiyayen Allah ne kawai, mun godewa Allah bisa kiyayewar da ya mana da abin da yake bisa ka’idar dabi’a ba za a rayu da shi ba, kuma dai da yake Allah ne mai rayawa, shi ya raya mu din.”

Rubutawa: Saifullahi M. Kabir
03/10/2023

03/10/2023

Video

Ku kalli Jawabin Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) dangane da ba da Passport, a ranar Litinin 17 ga Rabiul Auwal 1445 (2/10/2023) a gidansa da ke Abuja.


❤️

Eid Maulud Mobarak 🌹 "Manzon Allah (S) da kyawawan ɗabi'unsa ne ya yi Nasara akan maƙiya, ba da yaƙi ba! Manzon Allah (S...
27/09/2023

Eid Maulud Mobarak 🌹

"Manzon Allah (S) da kyawawan ɗabi'unsa ne ya yi Nasara akan maƙiya, ba da yaƙi ba! Manzon Allah (S) ramzi ne na kyakkyawan ɗabi'a. Shi ne kamilin mutum, idan da akwai wanda za ka ce masa 'Perfect' a mutum, to shi ne! Shi ne 'perfect' ! Sai dai a kwaikwaye shi, shi ne samfur wanda Allah Ta'ala ya ajiye don mu koya "Walakum fi Rasulullah Uswatun Hasana" shine 'Uswa' (Abin da za a gani a kwafa). Baza a taɓa wuce shi ba, ba kuma za a taɓa dai-dai da shi ba. Shi ne abin kwafan mutum, da ɗabi'unsa kyawawa da shi ne ya yi galaba".

–Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H)



12/RabiuAuwal/1445
27/09/2023

14/08/2023

Jawabin Jagora (H) na Makircin Makiya akan Harka Islamiyya da yayi jiya Lahadi 13/08/2023, yayin Ziyarar Daliban Hauza Ilmiyya.


14/08/2023

14/08/2023

IDAN AKA KAWO WA NIJERIYA HARI FARANSA CE BA NIJER BA! IN AKA KAI WA NIJAR HARI AMURKA CE BA NIJERIYA BA!

— Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) Ya Jaddada Kasheji a yayin ganawarsa da Daliban Hauza a ranar Lahadi 13/8/2023 a gidansa da ke Abuja.

IDAN AKA KAWO WA NIJERIYA HARI FARANSA CE BA NIJER BA! IN AKA KAI WA NIJAR HARI AMURKA CE BA NIJERIYA BA!— Shaikh Ibrahe...
14/08/2023

IDAN AKA KAWO WA NIJERIYA HARI FARANSA CE BA NIJER BA! IN AKA KAI WA NIJAR HARI AMURKA CE BA NIJERIYA BA!

— Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) Ya Jaddada Kasheji a yayin ganawarsa da Daliban Hauza a ranar Lahadi 13/8/2023 a gidansa da ke Abuja.

Ga bangaren jawabinsa:

“Wannan yana da muhimmanci mutane su san cewa, ba yadda za a yi ace muna fada tsakaninmu da junanmu, da wai wata kasa sunanta Nijar, da wata kasa wai Nijeriya. Dama wa ya yi Nijar da Nijeriyan in ba su ba? Ba su s**a tsaga ba? S**a raba kan iyaka s**a ce nan Faransa nan Ingilishi? Mu ba mu muka yi ba, dama muna tare, sun gammu kuma a tare ne.

To, abin da nake jin tsoro shi ne, tana iya yiwuwa, tunda yanzu duk sun saka sojoji a kan iyaka, sun yi wata kalma da muka saba jin Amurka tana fada, “all options on the table”. Dama maganarsu ne in suna ma kasashe barazana. Tun Bush uba, da Bush da, da su Clinton da Obama da Trump duk kowannensu ya yi amfani da wannan Kalmar ta “all options on the table”. Sai gashi wannan kalmarsu ce. Wato yanzu ba su cire yiwuwan su kai yaki ba.

To wa zai yaki wani? Don Allah ina ruwan Nijeriya da wani abu wai shi ‘Democracy’ a Nijar? Ina ruwansu? Sau nawa ana juyin mulki a Nijar su koma kan farar hula? Ina ruwan Nijeriya? Nijeriya ta je ta yi musu? Sau nawa kuma ana juyin mulki a nan? Wa ya zo yace mana dole sai an koma farar hula? Na taba jin dirkaniya irin wannan? Haka kawai kace dole kai za ka je ka (yi yaki da sunan kai Damukuradiyya?).

To kuma a sarari yake wannan ba yakinmu ba ne, yakin Amurka da Faransa ne. To kuma Faransa duk da Nijar sun rufe sararin samaniyarsu, sun hana abi, amma Faransa tana bi da jiragenta. Kuma suna da sansanoni na ‘yan ta’adda, wanda har an k**a wasu sun je sun kwace su. Daga nan ake kawo hare-hare Nijeriya. Wadanda ake ce ma ‘yan boko Haram din nan, ai sansanoninsu na can ne. Za su zo su kawo hare-hare, su debi gwalagwalai a raba.

To yanzu abin da nake jin tsoro shi ne, suna iya su yi amfani da wadannan ‘yan ta’addan. Ko kuma su da kansu ma su kawo hari ta sama, su ce Nijar ta kawo harin. Sai a fake da wannan ace, ai gashi nan Nijar ta kawo mana hari, saboda haka yanzu Nijeriya ma ta mai da martini. Saboda haka randa duk aka ji ko an yi harbi a Nijeriya, ko an ‘crossing boarder’, to ka tabbatar su ne s**a yi; Faransa ce da Amurka s**a yi, ba Nijeriya ba, ba Nijar ba!

Ba yadda za a yi ma a yi fada babu ma gaba. Haka kawai? Na wani da nake ba da labarin wani abu da naji wani ya fada, k**ar karin magana ne. Yace, wai ko kauye ka je kaga wa da kani suna fada, to ka bincika, Baturen Ingila ya zo wurin. Ingilishi ya zo nan. Yace, saboda duk inda s**a je suna hada fada ne. Duk inda s**a je, dama salonsu ne, tuntuni haka s**a saba, duk inda s**a je su hada fada, shikenan, shi wannan ke basu dama su mallaka.

To yanzu, an taba hada fada, baa bin da ya hada mu, muna zaune kawai muna zumunci, mun zama abu daya ne, mu fa ba daban-daban ba ne, mu abu daya ne, kawai rana daya ace wai muna fada? Wannan hauka har ina? To amma suna iya yi, tunda su suke da bukatar yin fada din, su za su iya zuwa su hahharbi wurare, sai su ce kuma ana mai da martani. Sai mu wayi gari kawai ana rugurguza kauyukanmu da biranenmu, ba a san adadin mutanen da za a kashe ba, a kan abin da babu gaira babu dalili illa kawai za su debi arziki. Shikenan abin da ya kawo su, basu kuma damu ba, duk cikanmu gaba daya suna iya kashe kowa, basu kuma damu ba, ba mu ne ke da muhimmanci ba.

Dama da s**a fara yakin Ukrain, sun nuna a sarari basu damu da mutanen Ukrain ba, ko da duk za su halaka, suna son a yi ta yakin ne har Rasha ta durkushe. Abin da ya dame su kenan, in ya so duk mutanen Ukrain su halaka. Amma kuma suna takaicin cewa mutanen Ukrain fa Turawa ne, har suna fada, wannan fa ba mutanen wai Afganistan ne ko Iraq ba, mutane ne fa masu shudin ido. Kai ka ji irin wannan. Wato abin takaici, shine mutum mai shudin ido yake mutuwa, inda mutumin Afganistan ne ko mutumin Iraq ai ba damuwa, sai ya mutun kawai. To yanzu kuma ina ga mutumin Afirka, wanda shi basu dauke shi ma a bil’adama ba. Shi kaga shi za a iya kashe shi ba damuwa, in ya so duk gaba daya shi ya kare, tunda shi basu dauke shi ma a matsayin bil’adama ba ma, ballantana har su yi tunanin don me ba zai mutu ba.

To, banda dirkaniya, su wadanda s**a yi juyin mulkin nan a Nijar, basu kashe kowa ba, ko an kashe wani? Ko mutum daya. To amma yanzu ana barazanar za a yi amfani da karfin soja a je a yi fada a kashe mutane don a dawo da Bazoum. In mutum yana da hankali, Bazoum din nan yana hannun wane ne? Yana hannun soja. Bazoum din nan fa mutum ne ba tsauni ba ne, kasan in kana rigima kan tsauni idan ka kori mutum sai ka kwace tsaunin ko? Ba kogi ba ne, in kogi ne, idan ka kori mutum sai ka kwace kogin. To shi mutumin nan kuna tsammanin yana hannunsu, sai ku je ku yi musu luguden wuta, sai su ce muku ga Bazoum dinku?

To kuma mu kaddara, in banda wauta ma, idan misali kuka ce Bazoum za ku dawo da, a karagar mulki. To in abin ku je ne, tunda Bazoum din yana nan k**ar kila ba za a yi masa komai ba, yana hannunsu. Sai su sako Bazoum din, sai ku dora shi, to za ku dawo Nijeriya ne? Ko kuwa za ku zauna ne ku tabbatar mulkin ya cigaba? Ko kuma yanzu babu wani soja a Nijar kenan sai ku? Na tabbata ba Bazoum ya dame su ba. Abin da ya dame su kawai, su haddasa fitina, a rugurguza kasashen nan guda biyu a debi arzikin wurin. Illa iyaka.

To dama abin da nake jin mana tsoron, kar wata rana a wayi gari an kawo mana hari a ce Nijar ne. In aka kawo mana hari mun san wa ya kawo mana hari, Amerika da Faransa ne, ba Nijar ba! Haka kuma in an kai hari Nijar, to ba Nijeriya ce ta kai mata hari ba, Amurka da Faransa ne! Saboda mene? Ba mu suke bukata ba, basu bukatarmu, suna bukatan arzikin da ke karkashin kafafunmu ne, kuma abin da ya kawo su kenan. Amma muna fatan Allah Ya kiyaye.

Nace, har wala yau, ba kawai muna gargadin cewa suna iya zuwa su haddasa fada tsakanin abin da suke kira Nijar da abin da suke kira Nijeriya ba ne, suna iya haddasa fada kuma a cikin kowadanne. Yanzu ma suna iya haddasa fada na kabilanci a cikin ita Nijar din, su ce mutanen Bazoum yan kabila kaza ne, mutanen kuma kaza suma kaza, sai a yi fada, k**ar yadda s**a haddasa a Sudan ana yi tsakanin Dinka da Nuer. To suna iya haddasa wannan.

Kuma Nijeriya din ma, shima suna iya ba da dama ana cikin yin wannan, wani bangare yace shi ma ya b***e. An fahimta ai? Sai ya zama shima an koma ana fadan cikin gida a cikin Nijeriya din. Duk zai taimake su. Kowanne zai taimake su. Fadan cikin gida yana iya yiwuwa a cikin Nijeriya kanta, tsakanin Kudu da Arewa, ko Kudu maso Gabas yace ya b***e. An fahimta ai? Dama akwai masu kiran b***e-b***e. Kaga sai a ce a raba kasar gida uku ko hudu. Sannan kuma ko cikin Arewan ma suna iya haddasa rigima, s**e ai akwai Musulmi akwai Kirista, an fahimta? Duk suna iya haddawa wadannan, saboda haka a kiyaye.

Musamman ‘yan Nijar. Kar su yarda a jefa su a fadan kabilanci. Domin su al’umma guda ce, kuma kabila Allah ne dai ya yi kabila ba wani ya yi kabila ba. Ko akwai bambancin kabila tsakanin wasu da wasu, Allah ne ya yi kabilolin. Kamar yadda Allah Ta’ala yake cewa, “Waja’alnaakum shu’uban wa qaba’ila lita’arafu.” Allah ne ya yi kabiloli daban-daban don su san juna, ba don su yi fada ba. Saboda haka yanzu ana iya haddasa wannan, a kiyaye, kar a yarda a fada rigimar cikin gida tsakanin mutumin Nijar da mutumin Nijar da sunan wannan dan kabila kaza ne, wancan dan kabila kaza ne.

Har wala yau, mu kuma nan, kar a haddasa mana rigimar cikin gida tsakanin Kudu da Arewa, ko tsakanin Musulmi da Kirista, ko tsakanin wasu kabila da wasu kabila. Allah dai ya kiyaye.

Abin da muka ce, muna da babban makami, wanda ya fi kowane irin makami, shi ne komawa ga Allah. A koma ga Allah da magiya da addu’a, don duk wata aniya ta makiya Allah Ta’ala ya fi karfinsu. Su karfin nasu na makami ne, amma karfin Allah Ya fi su. Aadawa sun ce “Man ashaddu minna quwwa?” Allah Ta’ala yace, to basu ga wanda ya halicce su ya fi su karfi ba? Yauwa. To Allah Ta’ala ya fi karfinsu. Muna fata Allah Ta’ala Ya kiyaye mu da kiyayewarsa. Insha Allahul Azeem.”

— Cibiyar Wallafa
Www.cibiyarwallafa.org

06/08/2023

Gargadi ga Masu Zumudin Kaiwa Jamhuriyar Nijar Hari.


06/08/2023

08/07/2023
Update:Yan uwa mata da s**a shirya tadrib sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) a gidansa dake Abuja.  17/06/20...
18/06/2023

Update:

Yan uwa mata da s**a shirya tadrib sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) a gidansa dake Abuja.


17/06/2022

Update: Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) met with the brothers and sisters who were discharged and acquitted by the co...
04/06/2023

Update:

Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) met with the brothers and sisters who were discharged and acquitted by the court after 4 years of illegal detention in Kaduna prison.


04/06/2023

Hausa:

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya gana da yan uwa maza da mata da kotu ta wankesu bayan shekaru 4, bisa zalunci a gidan yarin Kaduna.


04/06/2023

Update During 7-day programme to mark 2023 Imam Khomeini's Week, the representatives of the Academic Forum of the Islami...
04/06/2023

Update

During 7-day programme to mark 2023 Imam Khomeini's Week, the representatives of the Academic Forum of the Islamic movement in Nigeria, pay a visit to leader, Sheikh Ibraheem Zakzaky today at his Abuja residence.



03/06/2023

Hausa:

Yayin da ake gudanar da tarukan makon Imam Khomeini (QS) na shekarar 2023, wakilai daga dandalin daliban harka islamiyya (Academic Forum), sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), a gidansa dake Abuja.



03/06/2023

20/05/2023

JAWABIN JAGORA SAYYID ZAKZAKY [H] NA RUFE MAKON MUJADDADI SHEIKH USMAN BN FODIYE [RA] A SAKKWATO

Cikakken Jawabin jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky [H] wanad ya gabatar na rufe makon Sheikh Usman Bn Fodiye [RA] da bangaren ACADAMIC FORUM s**a gabatar a Sakkwato.

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya amshi bakuncin dalibaidaga makarantun fudiyya daban daban dake shirin bikin saukar...
17/05/2023

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya amshi bakuncin dalibai
daga makarantun fudiyya daban daban dake shirin bikin saukar Alkur’ani, yau Laraba a gidansa dake Abuja.


17/05/2022

SANARWA: Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H). بسم الله الرحمن الرحيم وَبَشِّرِ الصَّابِرِينَ الَّذِينَ إِذَا أَصَاب...
07/05/2023

SANARWA:

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H).

بسم الله الرحمن الرحيم

وَبَشِّرِ الصَّابِرِينَ الَّذِينَ إِذَا أَصَابَتْهُم مُّصِيبَةٌ قَالُواْ *إِنَّا لِلّهِ وَإِنَّا إِلَيْهِ رَاجِعونَ* ، أُولَئِكَ عَلَيْهِمْ صَلَوَاتٌ مِّن رَّبِّهِمْ وَرَحْمَةٌ وَأُولَئِكَ هُمُ الْمُهْتَدُونَ!!

Ana sanar da ƴan'uwa rasuwa Ɗan"uwa Malam Jamilu Ya'qub, hadimin gidan Jagora (H), a sak**akon hadarin mota a hanyarsa ta dawowa Abuja daga Kaduna.
Jana'iza: Gobe Litini 8/5/2023
Waje: Gidan Marafa, Matazu Road , Sabo Gari, Tudun Wada, Kaduna.
Lokaci = Karfe 2:00 na Rana

Allah Ya amshi uzirinsa, Ya yafe masa, Ya saka shi cikin ceton Annabi da iyalan gidansa tsarkaka. Mu kuma Allah Ya tabbatar da mu bisa tafarkin addinin Musulunci har karshen rayuwarmu.


-Fatiha🙏
7/5/2023

05/05/2023

Ya na da kyau Musulmi su hada kai wajen nuna rashin goyon bayan zaluncin da ake yi wa al'ummar Palastinu Wani yakin na jawabin da Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya yi a ranar Quds ta duniya.

04/05/2023

Idan kana son ka zama waliyi zaka iya zama amma dai *Ka kauracewa sabon Allah, kar ka yadda kaci haram, ka aikata wajibi sannan ka kara da nafiloli* to zaka zama waliyi..

JAWABIN JAGORA SHAIKH ZAKZAKY (H) YAYIN ZIYARAR GORON SALLAH Da yammacin ranar Asabar 9 ga watan Shawwal 1444H (29/4/202...
04/05/2023

JAWABIN JAGORA SHAIKH ZAKZAKY (H) YAYIN ZIYARAR GORON SALLAH

Da yammacin ranar Asabar 9 ga watan Shawwal 1444H (29/4/2023) ne Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gana da wasu daga wakilan ‘yan uwa a gidansa da ke Abuja. Abin da ke tafe rubutaccen jawabin da ya gabatar ne, wanda CIBIYAR WALLAFA Da Yada Ayyukan Jagoran ta rubuto muku.

GABATARWA:

A’uzu billahis Sami’il Alim, Minas shaidanir rajim, Bismillahir Rahamanir Raheem. Wasallallahu Ala Sayyidina Wa Nabiyina wa Habibi Qulubina Abil Qasimi Mustapha Muhammad wa ala alihid Dayyibinad Dahirinal Ma’asumiyn, Siyma Baqiyatullahi fiyl ard, Sahibul Asr waz Zaman arwahuna lahu fidah.

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi Ta’ala wa barakatuh.

Asalin wannan zaman namu saboda barka da sallah ne (Idil Fidr) na shekarar 1444. To, idan yadda ya k**ata ne, ya dace ace k**ar bayan sallah da kwana daya ne ko da kwana biyu (aka yi zaman), amma saboda sha’anin yadda abubuwa suke tafiye-tafiye da sauransu, sai ya zama da dan jidali a ce nan da nan daga yin sallah a zo.

Dama dai irin yadda muke yi da ne, kun san ranar Sallah ma mu kan zauna, haka kashegari ma, duk dai ranakun bayan sallah mu kan dan zazzauna. Sannan kuma mu kan dan yi wasu bayanai haka bayan sallah da kuma lokacin ma sallar.

To na san dai zuruf ba su iya bamu damar yin hakan ba. Saboda haka dai, na san na yi sakon Quds, amma sakon sallah sai dai idan yanzu ne za a ji. Saboda haka sai na fara da taya mu murna kenan da kammala Azumin watan Ramadan na wannan shekara da kuma ganin wannan Idi na karamar Sallah.

AL’UMMA BATA FAHIMCI MENE NE MAFITARTA BA

Na’am, na san ko bara mun ce muna cikin mawuyacin hali. Wani irin yanayi muka samu kanmu a ciki, kuma dai yanayin ba sakewa ya yi ba, yana nan yadda yake, idan ma ba dada tabarbarewa ya yi ba. Ko ba haka nan bane? Kun san abubuwa gyaruwa suke yi ko dada lalacewa? Abubuwa sai dada lalacewa suke ta yi. To kuma abin bai sake ba, sai dai muni ma yake ta ta yi, yanayin kenan.

Kuma al’umma tana cikin baganniya, bata gane wai mene ne ya sa ta fada cikin halin da ta fada ba, kuma meye mafita? Na kuma san tun shekarun baya mun sha batun cewa idan kana batun matsala, kowa ka yi magana da shi za ka ga ya san matsala, amma meye musabbabin matsala, mene ne kuma magani? To nan ne za ka ji maganganu mabambanta, wannan yace kaza, wannan yace kaza.

BA ZA A DAINA CEWA “WAYYO BA” HAR SAI AN GANO ASALIN MATSALA DA HAKIKANIN MAFITA

To, mun godewa Allah, akalla kaga dai cikin ni’imar da Allah Ta’ala ya yi mana, ya nuna mana hanya. Mun gode masa. Ba za mu iya cewa bisa hadari bane, bisa tagomashi ne daga wajensa.

Na’am, mun wayi gari ne muka gammu (a matsayin) ‘ya’yan iyayenmu Musulmi. To amma idan mutum ya lura, kusan dan abin da ya rage shine dan abin da ya rage na abin da bamu gama lalatawa ba, na wadanda kakanninmu s**a yi mai kyau. Su s**a yi aikin kirki ya wanzu, kuma tun lokacin sai muka yi ta lalatawa, muka yi ta lalatawa, to bamu gama lalatawan bane, shine a ka samu dan abin da aka samu a yanzu.

To kuma k**ar su mutane suna tunanin shikenan haka za a yi ta tafiya. Idan kace musu to wai ba mafita ne? Ko su ce maka babu mafita, ko kuma su kawo maka mafitan da ba ita ce (hakikar) mafita ba.

Na san bara ina cewa, kullum idan ka tambayi mutane mafita? Sai su ce maka to a jira sai an yi zabe. Sai an zabi shugaba mai adalci, sai ya gyara, sai a huta. Har nace to ba irin wannan ne kuka yi ba shekarun baya? Sai da kuka darje waliyi zanqalele? Kuma yanzu ya kwashe shekara takwas yana ta muku gyara, sannan kuma sai kuna wayyo-wayyo?

To har bara nake cewa to wa ya sani, idan aka sake irin wannan? A bara nake cewa, su suna cewa sai a jira 2023. Yanzu gashi 2023 din ta iso, har ma an yi zaben ko? Nake cewa to yanzu wa ya sanar da ku ko ma sai kun sake cewa wayyo? Wa ya sanar da ku ko ma sai kun ce ina ma tsohon waliyin nan ya dawo? Saboda yadda abubuwa s**a zama.

Ba haka nake fata ba, amma tana iya yiyiwu ya zama hakan ai. Wa ya tsammaci abin da ya faru yanzu zai faru? Ai da mutane sun dauka mafita s**a samu ko? To sai s**a ga abin da s**a samu. To wa ya sanar da su ko nan gaba abin da za su gani sai sun sake cewa wayyo? To, wayyo kam gaskiyar magana, yana da wahalar gaske a bar wayyo din nan har sai ranar da aka gane cewa wai mene ne asalin lalacewar nan kuma mene ne mafita?

Za mu cigaba.
Cibiyar Wallafa
www.cibiyarwallafa.org

Update:Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) receives a group of students of seminary schools (Hawza Ilmiyah) from Iran, Ir...
03/05/2023

Update:

Leader Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) receives a group of students of seminary schools (Hawza Ilmiyah) from Iran, Iraq and Lebanon at his Abuja residence.


03/05/2023

Hausa:

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gana da daliban Hauza Ilmiyya daga Iran, Iraq da Lebanon a gidansa dake Abuja.


03/05/2023

NASIHAR JAGORA (H) GA 'YAN UWA"To kuma don Allah ‘yan uwa, a kauce wa irin abin da ake jefa mu a kai na maganganu, la’al...
30/04/2023

NASIHAR JAGORA (H) GA 'YAN UWA

"To kuma don Allah ‘yan uwa, a kauce wa irin abin da ake jefa mu a kai na maganganu, la’alla yamu-yamu ne tsakaninmu ne, ko kuma tsakaninmu da wasu. Don Allah a kauce wa wannan.

“Yamu-yamu dama kullum na kan wa ‘yan uwa magana nace in dai za ku yi aiki tare akwai matsala fa, haka abin ya gada. Za ka ji wani kai kana abinka tsakani da Allah, wani kuma bashi da wani aiki sai s**a, wai kai dan bani na iya ne, kana wani nuna ka fi kowa ne, kai kaza-kaza.

"Oho dai, kana yi don wane ne? To ka yi abinka idan don Allah kake yi, amma idan domin shi (mai s**an) kake yi, sai ka bari tunda ya kwazzabeka ya dame ka, amma idan don Allah kake yi sai ka cigaba da abinka, ladanka na wajen Allah."

— Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a yayin ganawa da wakilan yan uwa a jiya Asabar 9/10/1444 (29/4/2023) a gidansa da ke Abuja.

30/04/2023

JAWABIN JAGORA SAYYID ZAKZAKY [H] A LOKACIN DA WASU WAKILAN 'YAN'UWA S**A KAWO MASA ZIYARA

UpdateJagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya amshi bakuncin wakilan yan'uwa a gidansa dake Abuja. Wakilan sun ziyarci Ja...
30/04/2023

Update

Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ya amshi bakuncin wakilan yan'uwa a gidansa dake Abuja.

Wakilan sun ziyarci Jagora (H) domin gaisuwar Sallah Karama.


29/04/2023

28/04/2023

Video

Sakon Jagora Shaikh Zakzaky (H) Zuwa ga 'yan uwa 'yan Gwagwarmaya

28/04/2023

Ko Gudummawar da 'yan uwa mata s**a ba da a wajen juyin-juya halin Musulunci a Iran kusan ya fi na maza.

Wani yanki daga cikin Jawabin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

25/04/2023

Babban dama ita ce ta kuriciya

12/04/2023

Kiran Jagora Sayyid Zakzaky (H) gane da ranar Qudus da nuna goyon baya ga al'ummar Palestine

10/04/2023

Addu'a

09/04/2023

Ramadan 1436 - 2015 Husainiyar Baqiyyatullah

Halin Kunci A Kasar Nan; A LURA DA ABUBUWA BIYU:“Zan so na tunatar da mu cewa, wannan al'amari (na halin da muke ciki), ...
08/04/2023

Halin Kunci A Kasar Nan; A LURA DA ABUBUWA BIYU:

“Zan so na tunatar da mu cewa, wannan al'amari (na halin da muke ciki), tushensa biyu ne;

Na farko tsarin da ya fandarewa na Allah, kuma (mu Musulmi) muka yarda da shi.

Na biyu kuma tsarin nan (da ya sabawa na Allah) abin da zai haifar shi ne fajirai, fasiqai, azzalumai su zama sune shugabanni.

Wannan tsarin ba yadda za a yi ko Mala'ika ne ya tafi da shi (bisa adalci)! Ko Mala'ika ya sauko daga sama wanda bai taba zunubi ba, ka ce shi ne Shugaban qasar nan, dole sai ya zama Azzalumin Mala'ika. Saboda haka duk wanda ke shugabantar tsarin Azzalumi ne, ba kuma yadda zai yi ya tashi a zalunci, saboda tsari ne da ma bisa zalunci aka shirya shi. Fima-labudda azzalumi zai zama shugabanta. Kuma dole da ma mutane in s**a zama haka nan su zama fasiqai da fajirai.

Muna iya ganin yadda wannan al'amari yake, muna zaune a qasar nan, ba a yi fari ba, bara da bara wancan an sami abinci baje-baje, amma duk da haka ana fama da rashin abinci. Qasar nan na cikin qasashen da suke da arzikin man fetur, amma qasar nan yanzu ba man fetur. Ga Nijar, busasshen wurin da ba ko man fetur guda, amma har suna kukan cewa yanzu har fetur din ma ya yi masu yawa. Me ya janyo wannan? Masarar da muke shukawa da Dawa da Gero da sauransu, haqa rami muke muna zubawa, ko kuwa cinyewa muke yi? Kuma Mai din ina yake?

Idan ya zamana kenan azzaluman da yake ba rahama a zukatansu su suke tafiyar da al'amari, wanda yake da ma tabbas in aka fitsare wa Allah da ma azzalumai ne za su yi shugabanci, ba su da tausayin kowa, har ma su sanya a yi Giya da Dawa ya fi masu a ci a kasuwa. Kuma su kadar wa qasar waje da dukiyar qasa, har da Mai din da ake taqama da shi ya fi masu, a yi masu gida a Paris ko London ko New York, a zuba masu kudi a Banki suna yi suna komawa can suna fasiqanci, Aljannarsu kenan, ya wadace su hakan. Za su iya kadar da qasar da duk wadanda suke ciki, ko su mutu, ko su yi rai!

- Cikin wani jawabin Shaikh Ibraheem Zakzaky a yayin Pre-Khudba a masallacin ABU, Zaria a 1992.

Address

Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jawaban Sheikh Zakzaky posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jawaban Sheikh Zakzaky:

Videos

Share

Category


Other Publishers in Abuja

Show All

You may also like