Glee Radio Online

Glee Radio Online gaskiya

Take it seriousBai k**ata ace wai sai ana tinama OGC ba, duba da manyan shirye-shirye da sukeyi, ga partners manya. Regi...
27/01/2024

Take it serious

Bai k**ata ace wai sai ana tinama OGC ba, duba da manyan shirye-shirye da sukeyi, ga partners manya.

Register and start claiming ✨
Hi! Join the most influential community in gaming. Grab OGC tokens every day for free and win draw for simple actions: https://app.ogcom.xyz/invite/yl-1J2IqZBQ6VYnH

https://youtu.be/QXoGMxDOz7k
23/11/2023

https://youtu.be/QXoGMxDOz7k

wannan wasa anyishine agarin bichi yayin gudanar da daurin auren yar gidan sarkin dawar masarautar bachi sarki rabe bichi ...

05/10/2022
Ministan ilimi Mista Adamu ya yi alkawarin ganin kungiyar malamai ta Jami'o'I sun janye yajin aiki da suke yi.Mista Adam...
09/09/2022

Ministan ilimi Mista Adamu ya yi alkawarin ganin kungiyar malamai ta Jami'o'I sun janye yajin aiki da suke yi.

Mista Adamu ya yi wannan alkawarin ne a yau Laraba, a cikin shirin "politics today" da tashar talabijin channels ta yi.
Me zakuce Kan hakan?

Sarauniya Elizabeth ta rasu!Masarautar Birtaniya ta sanar da rasuwar Sarauniya Elizabeth. Ta Rasu tana da shekara 96; ta...
09/09/2022

Sarauniya Elizabeth ta rasu!

Masarautar Birtaniya ta sanar da rasuwar Sarauniya Elizabeth. Ta Rasu tana da shekara 96; ta kuma kwashe shekaru 70 a kan gadon sarauta.
Me zaku iya tunawa dashi dangane da ita.
Glee

Da fatan kun tashi cikin koshin lafiya, marasa lafiya gida da asibiti Allah ya Basu lafiya.
09/09/2022

Da fatan kun tashi cikin koshin lafiya, marasa lafiya gida da asibiti Allah ya Basu lafiya.

30/08/2022

Ana cigaba da kokarin ceto mutanen da gini Mai Hawa uku ya danne a kasuwar waya ta beruit dake jahar Kano.

Akalla mutum 41 NE s**a mutu sak**akon gobara a wata chochi a Giza a kasar misra.Gobarar ta faru ne a dalilin wutar lant...
14/08/2022

Akalla mutum 41 NE s**a mutu sak**akon gobara a wata chochi a Giza a kasar misra.
Gobarar ta faru ne a dalilin wutar lantarki a daidai lokacin da sama da mutum 5000 s**a taru Dan gabatar da ibada a chochin da ake Kira Abu sifin.

Source: https://bbc.in/3w5QpgZ

An tsinci gawarwakin mutane ashirin a tsakanin mahadar qasar sudan da libya, hukumomi da suke kula da iyakokin kasashen ...
12/08/2022

An tsinci gawarwakin mutane ashirin a tsakanin mahadar qasar sudan da libya,

hukumomi da suke kula da iyakokin kasashen guda biyu (sudan da libya) sun rawaito cewa sun riski gawarwakin mutane ashirin yashe acikin sahara,

mujallar sudan state news agency (SUNA) ta rawaito tseratar da mutum takwas daga cikin matafiyan inda ashirin daga ciki kafin akawo musu dauki rai yai halinsa ba wannan ne na farko ba da aka taba tsintar gawarwakin mutane acikin ita wannan sahara ta libya, domin hanyace da mafi yawan al,umar kasashen afirika s**a dauka da matukar muhimmanci domin saduwa da kasashen turai,

Allah yajikan musulmi

GLEE ONLINE RADIO

DAGA KASAR LIBYA 🇱🇾✍️

Wata Kotun Shari'ar Addinin Musulunci Ta Aike Da Wani Sojan Gona Gidan Maza    Kotun Shari'ar Addinin Musulunci dake zam...
10/08/2022

Wata Kotun Shari'ar Addinin Musulunci Ta Aike Da Wani Sojan Gona Gidan Maza


Kotun Shari'ar Addinin Musulunci dake zamanta a Gama PRP ƙarƙashin jagorancin mai Shari'a Nura Yusuf Ahamed an gurfanar da wasu matsa guda biyu Umar Muhammad mazaunin Bachirawa mai shekaru 26 wanda ake zargi da laifin yin sojan gona a matsayin jami'in Kwastom wanda hakan ya saɓawa sashi 222 na spcl

Tunda fari wasu mutane ne suke yi ƙararsa kan cewar ank**a shi da kayan jami'an kwastom kan cewar shi jami'in kwatom ne a inda yake tsaka da gudanar da aikinsa sanye da kayan jami'an na kwastom din da shidar aikin wato Id card na jami'an yansanda

mai gabatar da kara Aliyul Abideen yakaranta masa kunshin tuhumar inda nan take ya musanta zargin.

Barrister Saifulhak Yaro Balare shi ne lauyan wanda ake kara yayi roko karkashin sashi na 35,36,karamin kashi na daya da sashi na 168 ACGl da sashi na 192 da a sanya wanda ake kara a hannun beli kuma a shirye suke dasu cika dukkanin sharudan da kotun ta gindaya mu su.

mai gabatar da kara ya nemi kotun data basu ranar 17 ga watan da muke ciki domin yin martani akan rokon lauyan wanda aka yi ƙara

kotun ta sanya ranar 16/9/2022 domin cigaba da sauraran karar ta kuma aike dashi zuwa gidan ajiya da gyaran hali .

Kazalika bayan kammala sauraran wannan ƙara ne aka ƙara Karanto masa wata ƙunshin tuhumar shi da wani abokinsa waɗanda ake zargin sun haɗa da Umar Muhammad Bachirawa da Abubakar sha'aibu Rijiyar lemo, waɗanda ake zargi da laifin hada kai, yin sata , yin sojan gona da karban kayan sata wanda ya sabawa sashi na 120,133,292,198 na kundin spcl

tunda fari wani mutum ne mai suna Anas M. Ahamed ma zaunin unguwar Ungoggo yake kararsu da cewar shi umar muhammad sanye da kakin custom ya tare shi akan hanyar Miltara bayan ya siyi shinkafa buhu 24 kimanin kudi naira dubu dari biyar ya kwace masa inda ya ce masa shi jami'in kwastom ne ya fito aiki fatirol inda shi kuma Abubakar sha'aibu ya sayi shinkafar a hannun Umar din alhalin yasan bashi ne mai shinkafar ba amma ya siya.

Sai dai bayan da yansanda s**a fara gudanar da binciki ne akan Umar kian k**ashi da ID card din yansanda da kuma uniform din custom.

Mai gabatar da kara Aliyu Abideen ya karanto musu kunshin tuhumar inda dukkanin su s**a musanta

lauyansu Barrister Saifulhak Yaro Balare ya roki kotun data sanyasu a hannun beli

Sai dai kotun ta sanya ranar 16/9/ domin cigaba da suraran karar ta kuma aike dasu gidan ajiya da gyaran hali da tarbiyya.

L.A. Abdullahi shi ne mai magana da yawun hukumar custom reshin jihar kano da jigawa ya nemi al'umma da su ringa basu bayanana sirri akan duk wani mutum dabasu yarda shi ba

Alƙali Ya Aike Da Ɗa Da Mahaifinsa Gidan Yari Sak**akon Zarginsu Da Aikata Laifin Cin Mutumci Da Razanar WaHausa Live Au...
09/08/2022

Alƙali Ya Aike Da Ɗa Da Mahaifinsa Gidan Yari Sak**akon Zarginsu Da Aikata Laifin Cin Mutumci Da Razanar Wa
Hausa Live August 09, 2022 0

ad728
download-2
Babbar kotun shari'ar Addinin Musulunci dake zamanta a rijiyar lemo karkashin jagorancin mai Shari'a Abdu Abdullahi Wayya an gurfanar da wani Ɗa da mahaifinsa sak**akon samun su da laifin d lakaɗawa makwafcin su dukan tsiya.

Ana dai tuhumarsu da aikata laifin haɗa kai , kwada ƙarfi, cin mutunci da kuma razanar wa wanda laifin yasaɓa wa sashi na 121,167,164, da kuma sashi na 228 na kundin spcl.

Tunda fari dai antuhumarsune da laifin lakadawa makwafcinsu dukan tsiya batare da yayi musu wani laifi ba.

bayan karanto musu ƙunshin tuhumar da ake yi musu nan take s**a musanta zargin.

kotun ta dage zaman zuwa ranar 22- 8 -2022 domin cigaba da sauraran karar ankuma aike dasu zuwa gidan ajiya da gyaran hali da tarbiyya.

JIN RA,AYI WANE KALLO KAKEWA WANNAN RANA TA GOMA GA MUHARRAM
08/08/2022

JIN RA,AYI
WANE KALLO KAKEWA WANNAN RANA TA GOMA GA MUHARRAM

DATTIJO MAI SHEKARU 74 YA KARƁI ADDININ MUSULUNCI A KATSINAWani Dattijo mai shekaru 74 a duniya ya musulunta, biyo bayan...
06/08/2022

DATTIJO MAI SHEKARU 74 YA KARƁI ADDININ MUSULUNCI A KATSINA

Wani Dattijo mai shekaru 74 a duniya ya musulunta, biyo bayan mafarkin da yayi yana riƙe da carbi a hannunsa, da kuma mala'iku suna kabbara da zikiri a gabansa, bayan ya farka ne sai yaga babu jazbin da ya wuce ya haɗu da Imam Abdullahi Abbah Galadanci Katsina, wanda shi ne ya musuluntar da shi.
Majiyar Katsina Post ta ruwaito cewa dattijon mai suna Gebreal wanda yanzu aka maida masa sabon suna da Abdullahi, ya musulunta yana da shekaru 74 a duniya, wanda haifaffen jihar Ogun ne da yake zaune a garin Kano da iyalansa.

Babban limamin masallacin Juma'a na Sheikh Abubakar Gumi da ke kusa da Firamare ta Sabuwar Unguwa Katsina, shi ne wanda ya musuluntar da shi.

Daga ƙarshe dai tsohon zai k**a hanyar tafiya ƙaramar hukumar Jibia inda ɗansa ke aiki, don ya faɗa masa ya musulunta, domin ya shaida mana ɗansa ma'aikacin kwastam ne da yake aiki a babbar boda ta Jibia da ke Katsina.

TAMBAYOYI 35 DA AKAIWA MALAN ABDULJABBAR KABARA AKOTU WANDA KUMA DASU AKA RUFE YIMASA TAMBAYAR (T1) Azam da,akayi abaya ...
06/08/2022

TAMBAYOYI 35 DA AKAIWA MALAN ABDULJABBAR KABARA AKOTU WANDA KUMA DASU AKA RUFE YIMASA TAMBAYAR

(T1) Azam da,akayi abaya ka fassara Kalmar fyade, kwace, auren dole, mu,amala tsakanin da namiji da mace, aharshen larabci inda kace fyade yana nufin (Al mubaja,ati ijbaran) auren dole kace (Azzawaju ijbaran) mu,amala tsakanin da namiji da mace kace (Atta,amuru bainarrujulu wal mir,ati) wadannan kalmomi kayi amfani dasu wajan fassara hadisai musamman hadisi Na 1365 amuslim Dana 5120 abikari hakane
(A) Eh hakane amma Na fassara da ma,ana ne bada lafaziba
(T2) Inaso anuna masa littafin danyaga hadisi 1365
(A) To ai wannan hadisin ba Wanda ake magana akansa bane lambardai dayace amma lafazin ba daya bane shi wannan yana maganane akan fitar annabi SWA kaibar
(T3) wato Ina nufin hdsn Nana safiya Wanda anass yarawato Wanda ka nasabtawa annabi SWA aikata wayancan kalmomi
(A) Ni bance hakaba cewa nai akwai ma,anar hakan inda anyi
(T4) To kawai inda aka rubuta Kalmar al mubaja,atu ijbaran nake so kanuna a hdsn
(A) Babu lafazin amma akwai ma,anar hakan
(T5) Acikin hdsn akwai inda aka ambaci azzawaju ijbaran
(A) A,a saidai ma,anar hakan
(T6) Duba wannan littafin sahihu bukari hds Na 5120 ka ganshi
(A) Eh Na ganshi
(T7) Shine hdsn dakace annabi SWA yabi wata mata kwararo ya biyamata bukata ta da namiji da mace
(A) Ni bance hakaba cewa nai mu,amalar da namiji da mace kuma ba abukari yakeba amuslim yake kuma iya binta kwararone aciki maganar mu,amala ta da namiji da mace bayanina ne danai bayan nagama karatu
(T8) Kamar yadda kasha fada cewa kai ma,ana kake fada nayi dai dai innace lafazin nakane
(A) A,a bakai dai dai ba
(T9) To lafazin nawaye
(A) Shi lafazin danai amfani dashi ba nawabane wani Na malaman Lugga ne wanikuma Na malaman sharhine
(T10) wadannan lafazan Na almubaja,atu ijbaran Dana azzawaju ijbaran ka tabbatar dacewa babusu acikin ruwayar hakane
(A) Eh amma akwai ma,anar su
(T11) To a ina kasamo lafazan
(A) To shidai almubaja,atu ijbaran ban nasabtawa waniba nace bayani nane
(T12) To sauranfa
(A) Duk suma ba lafazin saidai ma,anar
(T13) wadannan kalmomi dakai amfani dasu da Hausa fyade, kwace, auren dole, da mu,amala tsakanin da namiji da Mace hakane
(A) Bahaka bane kuma ni bance kwace ba cewa nai kwacewa dan da banbanci tsakanin kwace da kwacewa a Hausa duk dace alarabci sunansu daya
(T14) Ginshikim ilimin duk wani malami aduniya shine ilimin dayasamu agaban malaman dayai karatu agabansu Hakane
(A) Eh amma akwai kari Dan akwai ilimin da,ake samu ba takan malamaiba Dan Allah yanacewa و يعلمكم الله
(T15) to kana nufin wata baiwace akaima ko wahayi akema
(A) Wane wahayin kake nufi Dan shi wahayi nau,i biyune
(T16) Ni ilimina bai kai nanba ni bansan banbance banbance wahayiba
(A) To nidai ba aimim wahayi kuma banda yakinin Allah yana sanar dani ta wata hanya saidai abinda nasani shine Allah yaimin baiwar bahasi acikin littattafai kuma Allah ya horemim lafiyar yin batare da gajiyawaba saidai bacci ko yinwa
(T17) Malan nasiru kabara Babban malamine kowa ya shaida hakan masanine aharshen larabci ko akaratunsa Na Muslim antaba jin yace annabi SWA yayi fyade ko kwace ko auren dole ko mu,amala tsakanin da namiji da Mace da wata mata
(A) Bai taba cewa ba saboda azamaninsa babu wadannan matsalolin na farmaki ga annabi SWA da,akeyinsu a social media
(T18) Acikin karatunka Na audio daka gabatarwa wannan kotun innak tisabu li safiyatu kanat ala darajatul ula kafadi haka ko Baka fadaba
(A) Eh na fada amma bance da lafaziba
(T19) Inna fahimceka shi wannan larabcin babu shi Acikin hdsn Muslim kenan
(A) Eh babu shi da lafazi amma akwai ma,ana
(T20) Ko zaka iya fassara wa kotu
(A) Eh
(T21) Kenan innace iktisabu safiya nayi daidai innace anyiwa safiya fyade
(A) Eh kayi dai dai
(T22) Asanda kake karatunka kafadawa dalibanka da ma,ana kake ruwaya
(A) Eh na fadamusu
(T23) To yanzu in akakunna karatunka akaji sabanin haka kayarda kotu ta daukeka Mara gaskiya
(A) To itadai maganar ruwaya da ma,ana k**ar yadda yazo a alfiya duk inda kace haisu sarraha ya wadatarmaka agane da ma,ana kake ruwaya
(T24) Da za,a samu mutun daya ya sabawa mutun 10 yazo da wata ma,ana sabanin tasu ta sun za,a dauka hakane
(A) A,a hujjarsa za,a kalla inyafisu to tasan za,adauka
(T25) Littafin algaya yana daya saga cikin littattafan da kagabatarwa kotu to acikin wannan littafin ashafi na 52 ance Duk abinda aka rubutashi yakasance acikin littafin bukari da Muslim dangane da abinda ya kunsa aciki ba,a rawaitarsa da ma,ana hakane
(A) akwai amma yayi raddinsa a littafin kuma ya koma kan nawa ra,ayin
(T26) Kayarada alkali iyad yace yin ruwaya da lafazi shiyafi akan yi da ma,ana
(A) Bahaka yaceba kuma wannan maganar ta Sakawice bata alkali iyad ba shi alkali iyad cewa yai yak**ata arufe kofar yin ruwaya da ma,ana Dan kar Wanda bazai iya yin hakanba yazace zai iya k**ar yadda yafaru dawasu malaman ada da yanzu
(T27) Akwai littafin al kifaya Wanda shima yana cikim Wanda ka gabatarwa wannan kotun shafi na 577 aciki an nuna cewa ruwaya bil ma,ana an takaitatane akan canza wata kalma da wadda zatai dai dai da ita sai s**a bada misali k**ar haka
Jalasa da ka,ada duk suna nufin ya zauna alima da arafa duk suna nufin yasani to idan muka bi wannan ka,idar wacce Kalmar kamusanya acikin hds na 1365 tabaka Kalmar fyade kalama day tak mukeso
(A) Amsata ta daya su wayanda s**a shimfida wannan ka,idar ta jalasa da ka,ada suna maganane akan hdsn annabi bata wani sahabiba shikuma wannan hadisin na 1365 nakawo littattafai daya das**ace ba hadisin annabi bane maganar anass ce amsa da 1 kenan amsa ta 2 ita Kalmar ja,ala itqaha saqiha banine na fassara ta ahaka ba malaman das**a girmi bukari da Muslim su s**a fassarata s**ace wannan aure bai halattaba annabi bazai yishiba maliku Dan anas shine yai mata wannan fassarar Dan haka inaga shi yak**ata aiwa wannan tambayar da sauran tsarekunsa irin su Abu hanifa da sauransu baniba Dan shi yadorani akan wannan fahimtar
(T28) Adai cikin wannan littafin na alkifaya ankawo cewa mafi yawan malamai damasu bin diddigin hadisi sunce ba,a ruwayar hadisi da ma,ana sai dai akawo asalin hadisin babu dadi babu kari akwai wannan maganar
(A)Eh akwai ta amma tana maganane akan hdsn annabi shikuwa wannan hadisin 1365 nafada ba hds bane maganar anasce sannan kuma ya datse karashen maganar bai fadetaba Dan shi malamin aciketa dacewa kunzumin malamai sun tafi akan halaccin yin ruwaya da ma,ana
(T29) Malaman hds sunce abinda ake nufi da hadisi shine abinda aka jinganashi ga annabi nadaga zance ko aiki ko tabbatar da wani Abu da,akai agabansa ko suffa ta halitta ko ta dabi,a to abinda anas ya rawaita baya dagacikin haka
(A) Eh haka s**ace amma ai shi wannan hadisin na 1365 banine nace ba hadisin annabi bane malamai nakawo da s**a tabbatar ba hds bane maganar anass ce dagacikinsu akwai alkali iyad haka aini yafada haka ibn hajar yafada
(T30) Acikin shaidarka daka bayar agaban wannan kotu kace imamu malik yace wannan aure bai ingantaba kuma annabi bazaiyishiba sai kajinginawa imamu malik kace an rawaito acikin littafin Al mu,ulim ko hakane kafada
(A) Eh hakane nafada amma da kari ba,iya littafin Al mu,ulim nfadaba nakawo wasu littattafan amma idai maganar bai halattabane to tanacikin umdatul kari na Aini mujalladi na 20, har za,a wuce atafi tambaya ta gaba sai alkali yace yana bukatar adauko umdatul kari Dan akaranta duk dacewa shi lauya mai gabatar da tambaya have baya bukata amma kasancewar alkali ne yakeso yasa aka dauko littafin kuma kabawa Wanda ake kara yakaranto abinda akeso, aciki yake ashafi na 114 maliku yace wannan aure bai halatta ba
(T31) Adai cikin wannan littafin ashafin na 114 daga kasa cigaban maganar da kafara sai dashi malan dahawi yanancewa wannan Abu baya halatta gani inba annabi ba zai iya yin aure batare da sadaki ba sai dai yantawa sabosa Allah madaukakim sarki ya halatta masa aure batare da sadaki ba wannan itace cikon maganar daka fara Baka karasaba akwaita aciki ko babu
(A) inada amsa 2 tafarko ni cewa nai malik yace shikuma yatafi maganar dahawi kuma ni duk awayanda nace sunkore maganar nan ban ambaci sunan dahawi ba sannan shi aini bayan yakawo duk sabane sabanen akarshe ya rushe wanna auren na khaibar yakuma tabbatar da na banu kuraiza Wanda nakawo anan Wanda shine aure mai kyau da annabi SWA yaiwa Nana safiya kuma nima akansa nake
(T32) Akwai littafin Attaubih shafi na 228 Wanda shima wannan littafin ka dogara dashi agaban wannan kotun hakane
(A) Hakane
(T33) Ashi wannan littafin annuna karara ra,ayin imamu malik ne shi wannan aure kususiyace ta annabi akwai wannan maganar
(A) Wannan maganar akwaita saidai nafada wahami alkali iyad yasamu maganar dahawi ce dagacikin ikmalil mu,ulim ibn mulaqqib yadaukota kuma akarshe shima ya rushe auren khaibardin da aure razina yarufe Wanda nima akansa nake
(T34) Wannan ijaza da kake son kagabatar ta mahaifinkace sheikh nasiru kabara hakane
(A) A,a tawace
(T35) Ko zaka iya nuna mana inda aka ambaci sunanka aciki
(A) Amsa ita ijaza nau,i takwasce rawi ko sheyinka zai iya dauka yabaka batare da an fadi sunaka acikiba ita ake kira MUNAWALA Dan haka ba sharadine ba sai anga sunanka acikinta danhaka tinda ya dankamin ta tabbata tawa kuma dukkan yayansa ba Wanda yabawa maisuna acikinta yanda yabani haka yabasu

Da wannan tambayace lauyoyi masu gabatar da kara s**ace sun rufe yin wayannan tambayoyi nasu
# Dashi glee radio online

Ya Nemi Naira Miliyan Ɗari Ko Yayi Garkuwa Da Abokin Mahaifinsa Rundunar yan sandan jahar Kano ta cafke wani matashi da ...
05/08/2022

Ya Nemi Naira Miliyan Ɗari Ko Yayi Garkuwa Da Abokin Mahaifinsa


Rundunar yan sandan jahar Kano ta cafke wani matashi da ake zargin sa da aikata laifin yin garkuwa da wani mutum. Tun bayan samun ƙoƙarin ne a ranar 31 ga watan Yulin da ya gabata ne daga wani mazaunin Garin Makaɗi dake ƙaramar hukumar Garko ta jahar Kano,da cewar an kira shi a waya tare da neman Naira miliyan ɗari ( ₦ 100,000,000:00) da ya yi gaggawar biyan kuɗin ko ayi garkuwa da shi ko wani daga cikin ƴaƴan sa ,wanda aka cimma matsaya akan Naira miliyan biyu (₦2,000,000:00).
Bayan hakanne muƙaddashin kwamishinan yan sandan jahar Kano DCP Abubakar Zubairu ya tashi ƴan sandan kan kace kwabo karkashin jagorancin O/C na masu yaƙi da garkuwa da mutane SP Aliyu Muhammad domin kamo waɗanda ake zargin. Bayan jami'an yan sandan sun shiga gudanar da bincike ne s**a samu nasarar k**a wani matashi mai suna Isah Musa mai shekaru 30 wanda kuma maƙocin wanda yake yi wa barazanar sacewar ne. Mai magana da yawun rundunar yan sandan jahar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce binciken farko wanda ake zargin ya tabbatar masu da cewa mutumin abokin mahaifinsa ne wanda s**a haɗa kai da wani abokinsa dake wajan jahar Kano wanda s**a nemi Naira miliyan ɗari daga bisani aka ƙarƙare akan Naira miliyan biyu.

Sp Kiyawa ya ce da zarar sun kammala gudanar da bincike akan matashin za su gurfanar da shi a gaban kotu dan ya fuskanci hukunci daidai da laifin da ake zargin sa da aikata wa.

Shima a nasa ɓangaren mutumin da aka so yin garkuwar dashi bayyana jin daɗin sa tare da yabawa jami'an yan sandan da wannan namijin ƙoƙari da s**a yi na fitar da su daga tsoro.

aƙarshe SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce mukaddashin kwamishinan yan sandan jahar Kano DCP Abubakar Zubairu ya yi godiya da mutanen jahar Kano bisa haɗin kan da suke bawa rundunar da kuma addu'o'in su tare da shawarar al'ummar da zarar sun ga wani abu da basu amince masa ba suyi gaggawar sanar da ofishin ƴan sanda mafi kusa.

LAUYOYIN GWABNATI SUNRUFE CROSS EXAMINATIONBayan gabatar da akalla tambayiyi guda 40 s**ai ayau sun tabbaarwa da kotu ce...
04/08/2022

LAUYOYIN GWABNATI SUNRUFE CROSS EXAMINATION
Bayan gabatar da akalla tambayiyi guda 40 s**ai ayau sun tabbaarwa da kotu cewa sunrufe yin cross examination lauya mai gabatar da yin cross examination din brrst Abdurrahman yayi kokarin kawar da s**an da malamin yakemusu Na cewa sunkasa tauna mas,alar ilimi inda ayau shi wannan lauya yashiga cikin gundarin abinda ake tuhumar malamin shine hadisi Na 1365 a muslim Dana 2120 abukari al amarin daya farantawa malamin rai kenan inda yake ganin sai yanzu akazo fagensa kuma yayi kokarin amsa duk tambayoyin da,akaimasa wasuma said a yai sharhi akansu Dan yafutowa da kotu hakikar abinda yake nufi duk dacewa su lauyoyi masu kara hakan baimusu dadiba tayanda s**anyi s**a akan hakan s**e su iya amsar tambayarsu das**ayi sukeso
Daga karshe alkali Ibrahim sarki yola yajuya ga lauyan kariya inda yace dashi kokanada magana ananne lauyan yamiki yayi roko guda biyu k**ar haka
1 inaso wannan kotu tabani dama dannayiwa shaidana tambayoyi
2 inaso kotu tasake gayyatomin shaidun da bangaren masu kara s**a gabatar guda 3 amma banda professor Dan nima nagabatar was kotusu amatsayin shaiduna tinda doka tabani damar yin hakan
Lauyan masu kara yayi s**a akan wannan roko amma daga karshe mai Shara,a yace ya amince da rokon lauyan nafarko shikuma nabiyun yabashi dama azama nagaba yagabatarwa kotu dokar data bashi wannan dama
Alkali yadage wannan zama har zuwa ranar 11/8/2022 inda a wannan ranane shi lauyan kariya zai gabatar da tambayarsa ga shaidansa sannan kuma yakawo hujjojinsa daya dogara dasu Dan dawo da shaidun masu kara

To anan munacewa damu daku duk sai mujira wannan rana
Kucigaba da kasancewa damu damu Dan samun sahihan labari akan lamuran duniya

# Dashi glee radio online

KOTU TA BADA UMARNIN ACIGABA DAYIWA MALAN ABDULJABBAR KABARA CROSS EXAMINATIONBayan kin amincewa da alkali Ibrahim sarki...
04/08/2022

KOTU TA BADA UMARNIN ACIGABA DAYIWA MALAN ABDULJABBAR KABARA CROSS EXAMINATION
Bayan kin amincewa da alkali Ibrahim sarki yolayai da rokon lauyan kari Na Neman acanzawa Shara,ar dayake jagoranta kotu mai Shara,ar yabada dalilansa days dogara dash wajan kin amincewa da wannan roko idayace
Kasancewar doka ta bashi zabine akan yin hakan inyaga ya dace to shi a fahimtarsa yaga bai daceba sbd wannan kotun tasa itace kotu ta daya a wannan gari to idan andauke wannan Shara,a daga nan to ina za,a kaita India yafinan sannan Cuba da inda Wanda ake kara yake gabatar da wannan karatuttuka nasa da kuma inda wannan kotu take bazai kai klm 5 ba hakan yana nuna wannan kotun itace take da haqqi sauraron wannan shara,a sannan Cuba da irin tuhumar da,akewa Wanda ake kara tuhumace babbab wabba ta zawo hankalin mutanan gari hakannema yasa aduk sanda za,a kawo Wanda ake kara wannan kotu sai anbada Jami,an tsaro kuma antare hanya to idan aka kalli inda ake daukoshi wato kurmawa da kuma inda ake kawoshi wannan kotun babu wata tazara hakan yana nuna koda wata kotun ake wannan Shara,ar wajinbin wancan alkalin yadauko wannan Shara,a yadawomin da ita dan kiyaye lapiyar Wanda ake kara, sannan kuma ita wannan Shara a yaukimanin shikara guda anayinta hard a wata daya kuma doka tace indai aka dauke wannan Shara,a daga wannan kotun sai andawo farko nikuma bazanyi abinda zai cutar da Wanda ake kara ba haka alkali ya zaiyano wannan za,ayi nasa akarshe yace Allah shine mafi sani daga sanin kowa
To muma munacewa Allah shine masani
Kucigaba da kasancewa damu dankawo muku cigaban wannan Shara,a

# Dashi glee radio online

MINISTAN SUFURI NA NIJERIYA YA CE ZA A SAKA NA'URORI KAFIN JIRAGEN ƘASA NA ABUJA-KADUNA SU KOMA AIKIMinistan sufuri na N...
03/08/2022

MINISTAN SUFURI NA NIJERIYA YA CE ZA A SAKA NA'URORI KAFIN JIRAGEN ƘASA NA ABUJA-KADUNA SU KOMA AIKI

Ministan sufuri na Nijeriya Mu'azu Sambo ya ce za a sanya fasahar da ta dace kafin su jiragen ƙasa su koma kan hanyar Abuja zuwa Kaduna .
Sambo ya kuma bayyana fatan cewa za su kuɓutar da sauran fasinjojin jirgin ƙasan da aka sace .

Ya bayyana hakan ne a wata ziyarar aiki da yai tashoshin jiragen ƙasa na Idu da Kubwa a ranar Talata a Abuja. Ministan ya ce akwai buƙatar ganin ganin an ɗauki matakan da s**a da ce domin kaucewa sake afkuwar harin na Jirgin ƙasa na ranar 28 ga watan Maris 2022.

" Gwamnatin tarayya na yin duk mai yiwuwa dan ganin an kuɓutar da waɗanda wannam lamarin mara daɗi ya shafa ". Sambo ya ƙara da cewa za a samar da isasshen tsaro dan kare fasinjojin daga dukkanin wata barazana . Kamfanin dillacin labarai na Najeriya (NAN)ya ruwaito cewa hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta dakatar da zirga-zirgar Jiragen ƙasa akan hanyar Abuja - Kaduna bayan harin ta'adancin da aka kai a ranar 28 ga watan Maris 2022.

DUBUN WASU ƁARAYIN DABBOBIN JAMA'A YA CIKA A HANNUN RUNDUNAR ƳAN SANDAN JAHAR JIGAWA Rundunar ƴan sandan jahar Jigawa ta...
02/08/2022

DUBUN WASU ƁARAYIN DABBOBIN JAMA'A YA CIKA A HANNUN RUNDUNAR ƳAN SANDAN JAHAR JIGAWA


Rundunar ƴan sandan jahar Jigawa ta cafke wasu matasa 4 da ake zargin su da satar dabbobin jama'a a jahar .
Kakakin rundunar ƴan sandan jahar Jigawa DSP Shiisu Lawan Adamu ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.

Shiisu ya ce a ranar 29 ga watan Yulin da ya gabata jami'an yan sandan su da suke gudanar da sintiri a Yankin Jahun , waɗanda s**a samu nasarar k**a mutane 4 da wasu tumaki 2 a cikin mota ƙirar Golf Ja, mai Namba TGD 410 AA da suke ƙoƙarin Siyar da Tumakin a kasuwar Aujara dake ƙaramar hukumar Jahun.

DSP Shiisu ya ƙara da cewa da s**a tsananta bincike akan waɗanda ake zargin sun tabbatar da cewa sun haɗa kai domin aikata laifin satar kuma sun sato dabbobin ne daga unguwar Sabuwar Kasuwa da yankin Tukur duka a ƙaramar hukumar Dutse .

Waɗanda Ake Zargin Sun haɗa Kabiru Abdu mai shekaru 22, Hadau Shehu mai shekaru 20 , Usman Ya'u mai shekaru 19 ,Tasi'u Yusha'u mai shekaru 20 dukkansu ƴan Garin Tsada dake Dutse.

A ƙarshe ya tabbatar da cewa kwamishinan yan sandan jahar CP Aliyu Saleh Tafida ya bada umarnin gudanar binciken kwaƙwaf kuma da zarar sun kammala za su gurfanar da su a gaban kotu dan su fuskanci hukunci daidai da laifin da ake zargin su da aikata wa

YAN SANDA A KANO SUN TABBATAR DA CAFKE JAMI'AN BIJILANTI 6 BAYAN SUN YI WA WANI MUTUM JINA-JINA Rundunar yan sandan jaha...
01/08/2022

YAN SANDA A KANO SUN TABBATAR DA CAFKE JAMI'AN BIJILANTI 6 BAYAN SUN YI WA WANI MUTUM JINA-JINA


Rundunar yan sandan jahar Kano ta tabbatar da cafke wasu jami'an Bijilanti 6 bisa Zarginsu da lakaɗawa wani mutum duka wanda hakan yai sanadiyar mutuwar sa. Tun a ranar 31 ga watan da ya gabata na 2022 lamarin ya faru a yankin Unguwar Kankare dake Rijiyar Zaki ,wanda aka ga mutumin mai suna Musa Lawan ɗauke da wani jariri a hannunsa wanda mutane s**a rufe shi da duka.
Mai magana da yawun rundunar yan sandan jahar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce bayan samun rahotanne muƙaddashin kwamishinan yan sandan jahar Kano DCP Abubakar Zubairu ya tashi tura tawagar yan sanda waɗanda s**a garzaya da mutumin da kuma jaririn zuwa babban Asibitin Murtala dake Kano wanda likita ya tabbatar da mutuwarsa.

Kiyawa ya ƙara da cewa yanzu haka jami'an Bijilanti 6 suna hannun a sashin binciken manyan laifukan kisan kai dake Bompai kuma da zarar an kammala gudanar da bincike za su sanar da halin da ake ciki

RUNDUNAR YAN SANDA TA HARAMTAWA YAN FIM AMFANI DA KAKINSU A FINA-FINASifeta Janar na Yan sandan Najeriya ya gargadi masu...
01/08/2022

RUNDUNAR YAN SANDA TA HARAMTAWA YAN FIM AMFANI DA KAKINSU A FINA-FINA

Sifeta Janar na Yan sandan Najeriya ya gargadi masu shirya fina-finai a kasar da su guji aibanta aikin dan sanda a shirye-shiyensu na talabijin, ba tare da izinin rundunar ba.

IG Usman Baba ya kara da cewa daga yanzu ka da a ƙara ganin wani mutum sanye da kayan ɗan sanda a fina-finai, ba tare da izini ba k**ar yadda doka ta tanadar.

Ya ce idan ba haka ba to kuwa duk wanda ya karya doka zai ɗanɗana kudarsa.

Masu shirya fina-finai a Najeriya kan kwaikwayi jami’an yan sandan kasar, kuma a mafi yawan lokuta ba a nuna su a mutanen kirki.

INEC ta rufe yiwa yan Nigeria rijistar katin zabe

Sanarwar da rundunar yan sandan ta fitar ta ce “ka da wani mai shirya fina-finai da ya sake nuna ƴan sanda a matsayin marasa kirki ba tare da izini ba a rubuce daga rundunar yan sanda.”

Sanarwar ta ƙara da cewa ba za ta amince da bayyana aikin ɗan sanda ba a fina-finai, matsawar abin da aka kwaikwaya a aikin ba shi da kyakkyawan tasiri ga al’umma

INJINIYA SAGEER ƘOƘI YA TAYA AL’UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR BIRNIN DA JIHAR KANO MURNAR SHIGOWAR SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCIInj...
01/08/2022

INJINIYA SAGEER ƘOƘI YA TAYA AL’UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR BIRNIN DA JIHAR KANO MURNAR SHIGOWAR SABUWAR SHEKARAR MUSULUNCI

Injiniya Sageer Ƙoƙi Ya Taya Al’ummar Ƙaramar Hukumar Birnin Da Jihar Kano Murnar Shigowar Sabuwar Shekarar MusulunciInjiniya Sageer Ƙoƙi Ya Taya Al’ummar Ƙaramar Hukumar Birnin Da Jihar Kano Murnar Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci.
Injiniya sageer koki ya mika sakon barka da shigowa sabuwar shekarar musulunci ga al’ummar musulmin Nigeria.

Injiniya koki ya nuna farin cikinsa da shigowa shekara ta 1444 bayan hijjrah, wanda ya yi kira ga dukkan al’ummar musulumi da su yi amfani da wanann lokaci wajen yiwa Kasa addu’o’in samun Zaman lafiya.

Cikin wata Sanarwar da injiniya sageer koki ya fitar ya kuma yi kira ga iyaye da su rika sanya idanu sosai ga ‘ya’yansu wajen daukan al’amuransu na yau da Kullum tare da kira gare su da su kasance mutane na gari.

Sageer koki ya taya injiniya Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso murna bisa managartan ayyuka da ya samarwa al’ummar jihar kano,
kuma Yana da yakinin shi ne ya dace da zama shugaban Kasar Nigeria .

Dan Takarar Majalisar ya kuma taya al’ummar karamar hukumar birni murnar shigowa sabuwar shekarar musulunci, harma ya yabawa malaman addinin musulunci bisa addu’oi da sukeyi na Samun zaman lafiya a kano kasa baki daya.

AN K**A MUTANEN HUDU DA AKE ZARGIN SUN TAIMAKA WAJEN KAI HARI GIDAN YARIN KUJEAN K**A MUTANEN HUDU DA AKE ZARGIN SUN TAI...
31/07/2022

AN K**A MUTANEN HUDU DA AKE ZARGIN SUN TAIMAKA WAJEN KAI HARI GIDAN YARIN KUJEAN K**A MUTANEN HUDU DA AKE ZARGIN SUN TAIMAKA WAJEN KAI HARI GIDAN YARIN KUJE

An k**a mutanen hudu da ake zargin sun taimaka wajen kai hari gidan yarin Kuje
Jami'an tsaron Najeriya sun cafke wasu mutane hudu da ake zargin na kwarmata bayanan sirri ga 'yan bindiga a babban birnin ƙasar, Abuja.

Jaridar PRNigeria ta rawaito wata majiya mai karfi ta hukumar leken asiri ta kasa da ke tabbatar da kamen.

Jaridar ta ce an cafke mutanen tare da wasu na'urori da mak**ai da tsoffin wayoyin hannu da basa amfani da intanet.

Majiyar da ke cikin ayarin mutanen da s**a yi kamen na cewa, ana ci gaba da bincike cikin sirri domin gano shugabanninsu da masu daukar nauyinsu.

Waɗannan mahara ake kuma zargi da kai hari a wasu sassan yankunan Abuja, a cewar majiyar.

Yanzu haka ana tsare da mutanen da aka cafke da tuhumarsu domin amsa tambayoyi.

Jaridar ta kuma rawaito cewa hukumar tsaro ta Najeriya na tattara bayanan sirri domin gano masu hannu a matsalolin tsaro da hare-haren da ake kitsawa.

RAYUWA TA TANA CIKIN HATSARI IDAN NA BAYYANA MASU ƊAUKAR NAUYIN MU : DESTINY AGBAIJOH Hukumar yaƙi da hana sha da  fatau...
31/07/2022

RAYUWA TA TANA CIKIN HATSARI IDAN NA BAYYANA MASU ƊAUKAR NAUYIN MU : DESTINY AGBAIJOH


Hukumar yaƙi da hana sha da fataucin miyagun ta ƙasa NDLEA ta cafke wani matashi mai suna Destiny Agbaijoh, ɗauke da bindiga ƙirar AK-47 a jahar Ondo.
Destiny ana Zarginsa da aikata laifin kisan kai ,wanda ya tabbatar da cewa matuƙar ya bayyana sirrin masu ɗaukar nauyin su rayuwarsa tana cikin hatsari.

Da yake jawabi kwamandan hukumar NDLEA a jahar Mista Kayode Raji, ya ce an k**a matashin da ake zargin ne a lokacin da suke gudanar da bincike akan hanyar Ore-Okitipupa. Raji ya ƙara da cewa wanda ake zargin ya yi yunƙurin bai jami'ansa cin hanci amma s**a ƙi karɓa .

" An k**a Destiny a ranar 20 ga watan Yuli 2022 a kan hanyar Ore-Okitipupa da jami'an suke tsaka da gudanar da bincike".

Binciken Farko da s**a gabatar akansa an samu Harsasai iri daban-daban da kuma wasu jakunkuna. Kwamandan ya ce sun gudanar da binciken su na farko kuma za su miƙa shi ga jami'an ƴan sandan Nijeriya dan ɗaukar matakin da ya dace akansa.

TSADAR MAN FETUR YA SA MA'AIKATAN GWAMNATI NA NEMAN ƘARIN ALBASHIBiyo bayan ƙarin farashin man Fetur wasu ma'aikatan gwa...
31/07/2022

TSADAR MAN FETUR YA SA MA'AIKATAN GWAMNATI NA NEMAN ƘARIN ALBASHI

Biyo bayan ƙarin farashin man Fetur wasu ma'aikatan gwamnatin tarayya da na jahohi sun yi kira ga gwamnatocin biyu su ƙara wa ma'aikata albashi domin rage mu su wahalhalu. Ma'aikatan sun shaidawa kamfanin dillacin labarai na Najeriya NAN a ranar juma'a a jahar Katsina, sunce roƙon ya zama dole saboda farashin kaya da sufuri sun yi tashin Gwauron zabi.
Malam Abdullahi Balarabe ,wani Ma'aikacin gwamnatin tarayya ne a Katsina ya ce sak**akon ƙarin farashin man Fetur, farashin kayayyaki ya ruɓanya.

Kamfanonin jiragen Saman Nijeriya sun ƙara farashin man fetur sak**akon tashin man jiragen Jet A1. Balarabe ya ce abinda ya saba siya akan Naira 200 a yanzu ana siyarwa tsakanin Naira 300 zuwa 400 , wanda ya ƙara da cewa hakan ya zama babban ƙalubale ga ma'aikata masu ƙaramin karfi.

" Kamar yadda kuka sani , duk da ƙarin farashin man fetur da kuma ƙarin farashin kayan Abinci da sauran kayayyaki , albashin mu ya tsaya cak. " Kafin ƙarin farashin da aka samu a halin yanzu, ba za iya kaimu har zuwa ƙarshen wata ba".

" Ya ƙara da cewa wasu daga cikin mu suna kashe albashin su ne a biyan bashi ". Wani mai suna Edwin Michael ,kuma Ma'aikacin gwamnatin tarayya ya ce sai da ya ajiye motarsa domin tafiya ofis saboda wasu gidajen mai suna siyarwa akan fiye da Naira 185 .

" Muna kira ga gwamnatin tarayya da ta yi duk mai yiwuwa don ƙara mana albashi domin mu cike giɓin da muke samu a gida duk wata. Wani ɗan kasuwa a jahar Katsina Malam Isma'il Garba ya ce an samu ƙarin farashin kayayyaki ne saboda ƙarin kuɗin da aka yi na sufuri , yanzu haka ana siyar da Koyar man Fetur tsakanin Naira 184 zuwa 220 a gidajen mai .

Address

Benghazi
BANGAZI

Telephone

+218944467745

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Glee Radio Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Glee Radio Online:

Videos

Share

Category



You may also like